Sashe 110
Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunda ta ji dirar mota hankalin ta ya bata shine ya dawo, cike da dauki na san ganin kyakkyawar fuskar shi ta dago kai tana kallon kofar sai dai abin da ta gani ya matukar dukar zuciyar ta, har sai da taji kamar zuciyar ta zai zillo kasa ya faɗo, da sauri ta dukar da kanta ta shiga kokarin komawa da zuciyar ta, tana maimai ta innalillahi wainnailaihi rajiun, kallon ta Asmah tayi, gaskiya taji babu dadi don ko ita ne baza taji dadi ba duk da dai baisan suna falon ba, kuma ji yadda ya wuce kamar bai ganta ba, kawai sai taji zee ta bata tausayi, nufar ta tayi tana kirkiran murmushi tana magana ta shiga ta mata amma bata san tana yi ba da alama tayi nisa sosai cikin tunani sai da ta ce "Anty zee!" Da karfi sannan tayi firgigit ta dago ganin ta yasa ta saki murmushin yaƙe wanda yafi kuka ciwo amma fa na ciki na ciki. Tace " kin gani ba kin tsai dani gashi oga ya zo ya tarad dani gaskiya naji kunya kuma duk laifin kine." Ta fada tana mike wa da nufin daukar little su tafi sai dai ga mamakin su wayam ba yaro ba dalilin shi, zaro idon da tayi ne yasa Asmah saurin juyawa, itama abin ya daure mata kai to ina little din yake, abu kamar almara babu shi a falon babu alamar shi, Asmah tace ina zuwa ko yabi "honey sama ne." Da sauri ta haura tabar zee nan gaban ta na faduwa.
Samun shi tayi zaune a bakin bed ya rage kayan jikin shi ya bar dogon wandon suit da singlet little na kamkame a kirgin shi ya rungume yaron kamar zai mai da shi jikin shi, sauke ajiyar zuciya tayi ganin yaron a nan, fitowa tayi da sauri dan ta gaya wa zee ga ya cen gurin Aslam sai dai ga mamakin ta wayam taga falon, ko shakka babu ta wuce, wannan abu bai mata dadi ba gaskiya, zama tayi na kusan mintin goma tana tunane tanane lamarin Aslam ya mugun daure mata kai, yana son danta amma yace ita baya son ta to ko shakka babu wagga batu karya ce , jiki a sanyaye ta mike ta nufi upstairs tun kafin ta tura kofar dakin ta ringa jiyo dariyar shi shida yaron kamar zasu tada dakin, da sauri ta karasa ciki a kan gado ta hango su Aslam na kwance ya daura little akan kafarshi ya daga shi sama yana mishi lilo shi kuma yana ta kwasan dariya, ikon Allah tace a ranta, wannan lamarin da daure kai yake. Karasa wa ciki tayi ya dago yana kallon ta, rasa abin cewa yasa tace "sannu da dawowa." Sauke little yayi ya mike zaune yace mata "me ya kawo ta part din nan." Tace "kamar yaya." Hararan wasa ya watsa mata tare da cewa "kamar yayo." Dariya ta kwashe da shi tace "hira tazo muyi ko haramun ne kishiyoyi suyi hira a tare." Yace "bazan hana ki ba amma wlh kibi a hankali dan da kike ganin ta haka shalau shalau ba kanwar lasa bace." Dariya ya bata wai shalau shalau ta kuwa dara sosai tare da cewa " kai dai ka sani, koma ya take ai dai zabin ka ce, kuma sai na gaya mata." "Kin daɗe." Ya fada yana mikewa "muje ni da Allah ki bani abinci naci na kwaso yunwa da gajiyar aiki."
Ranar dai a part dinsu little ya wuni, a tsakanin su sai ji dashi suke yi suna wasa dashi, cikin kankanin lokaci yaron ya saba dasu, ko tunanin su maida mata ɗanta basu yi ba har gurin karfe taran dare, Asmah ce tayi hankalin cewa "Baza mu mayar mata da shi ba, kaga dare yayi kuma ita kaidai ce a part din ta nasan tana cen tana jira." Share ta yayi, sai da ta sake maimai tawa sannan ya kalle ta yace "A nan zai kwana." Bata rai yayi ya mike tare da daukar little suka wuce sama dan ma kar ta samu daman yi mai wani magana, baya jin zai iya rabuwa da yaron koda na minti daya ne ba tare da wani kwakwarar dalili ba, zama tayi tayi shiru tana tunani, gaskiya basu kyauta wa zee ba idan suka yi haka, to amma ya ta iya, yanzu yanda ya haɗe ran nan tana magana cibi zai zama kari, a tsakiyar su yaron ya kwana ranan dan tsabar gata.
A bangaren zee kuwa hakan bai dame ta ba, sai ma dadi da ya mata, domin duk wanda ke kaunar danka ai masoyin ka ne, ko iya haka suka tsaya wlh sun nuna mata soyayya, a bangare daya kuma abin da ya faru dazu yana tsungulin ta a rai, sai dai tana danne wa , duk yadda sheɗan yaso yasa ta taga bakin Asmah taƙi yarda duk yadda zuciya ta hasaso mata sai ta kauce, ta daukar ma kanta alkawari tun da Asmah bata nuna mata wani mugun hali ba to kuwa ita baza ta nuna mata komai ba zata jata a jikin ta su zama kamar yan uwa hakan ma wani mata ki ne da zata samu kusanci da burin ranta.
Washe gari daker ya tafi aiki karshe ma cewa yayi zai tafi da yaron, daka tsallen albarka tayi ta hana, dan tasan idan har ta kuskura ta bashi wannan daman so daya ya dinga yi kenan kuma bazai maida hankali kan aikin shi ba. Yana tafiya ta dauke shi suka tafi part din zee dama sun riga sunyi wankan su sun karya. Da fara'a ta tare su babu alamun damuwa a fuskar ta, bayan sun gaisa Asmah tace "sai kika jimu shiru jiya ko." Murmushi tayi tace "ba komai ai yaro ya koma wajen Asalin mummy shi." Hakan data fada yama Asmah dadi take ita ma ta fara bata labarin yadda Aslam ya karbi yaron da yadda ya dinga mai harda cewa da yayi zai tafi dashi office, dariya zee ta ringa yi zuciyar ta wasai, Asmah ta bata wannan labarin ne dan ta faran ta mata rai kuma ta kwantar mata da hankali , aiko dai kwalliya ta biyu kudin sabulu, ranar a part din zee ta wuni tuni wani irin sabo da shaƙuwa ya shiga tsakanin su kamar ba kishiyoyi ba tare sukayi girki anan Asmah taga basu da kayan abinci sai wanda ta siya ta kuma kudiri aniyar yiwa Aslam magana, sai gurin karfe ukun rana ta koma shiyar ta ta daura ma Aslam girki, tuwon shinkafa tayi lafiyayye kuma gaba daya ta girka harda zee, tako ji dadi ta amsa tana ta mata godiya.
Cikin abinda baifi sati daya ba sun gama fahimtar juna, duk da kowacce zuciyar ta cunkushe yake da kishi musammam ma zee dan ita Asmah har yanzu bata San dawan garin ba tunda kullum tana tare da miji, zee na matuaƙar kokarin danne wa amma fa kullum Daren duniya sai tasha kuka ta gode Allah, Aslam gaba daya bata gaban shi kasancewar yanzu tana yawan zuwa part din Asmah dan tare ma suke hada dinner kullum duk idan ranar tayi rashin sa'a suka hadu takan gaishe shi, a dake yake amsa mata kuma kallo daya yake mata babu kari wannan abin shi yafi komai kona mata rai, bata da matsala ko kaɗan da Asmah sai wanda ba'aka rasa ba, little kam zuwa yanzu ya zama mai uwaye biyu yau ya kwana a nan gobe ya kwana a nan duk dai inda yaga dama.
Yau ma kamar kullum tare suka gama haɗa dinner, sunayi suna hira, Asmah ce ta fara kawo zancen Aslam cikin firan nasu, da sauri zee ta kauda maganar ta canza wata hiran Asmah ta lura sau da yawa haka take mata da ta dauko zancen Aslam zata doje, tausayi take bata sosai na yadda Aslam ya wofintar da ita, sau da yawa takan auna kanta a matsayin zee taga idan ita ake wa haka zata iya jura kuwa, duk sanda tayi wannan tunanin takan jinjina wa zee da hannu bibbiyu. Bayan sun kammala hada mata nata a basket Asmah tayi kamar yadda take yi kullum, dauka tayi ta tashi dan lokacin dawowar Aslam yayi daf, cikin tsokana tace ma little "muje." noƙe kafada yayi alamar bazai bita ba dariya suka zaka mai tace "dama tsokanar nake yi zaman ka wurin mummyn ka." Har takai kofa yace "Mummah." Ta juyo yace "kar kiyi kuka yau kinji." Kallon juna sukayi da Asmah, Asmah tace "kuka kuma?" Murmushin yaƙe tayi tace "shirmen little ne kawai rabu dashi." Tana gama fadin haka ta sa kai tabar part. Kuka kuka haka tayi ta maimaita kalman, tabbas yaro baya karya, to meke saka ta kuka ne, da sauri ta kalli little dake ta wasan shi tace "my boy Mummah ka na kuka kace." Yace "eh mana mummy kullum sai tayi kuka da daddare, ta ringa cewa Allah ya dawo mata da hankalin mijin ta,Allah yasa ya yafe mata, zuciyar ta zata fashe." Zama tayi dabass tana maimaita innalillahi wainnailaihi rajiun, lallai suna shiaga hakkin zee, baiwar Allah a she tana cikin damuwa har haka amma ko a fuska bata taba nunawa ba, kila ma tana jin haushin ta , kila ma ta ringa ganin kamar ita ta hana Aslam dawowa gare ta, tasan ba abinda baza ta ayya na ba tun da dai ita zuciya ai bata da ƙashi lallai Aslam yau ya dawo zata same shi suyi magana ta fahimtar juna.
Samun shi tayi zaune a bakin bed ya rage kayan jikin shi ya bar dogon wandon suit da singlet little na kamkame a kirgin shi ya rungume yaron kamar zai mai da shi jikin shi, sauke ajiyar zuciya tayi ganin yaron a nan, fitowa tayi da sauri dan ta gaya wa zee ga ya cen gurin Aslam sai dai ga mamakin ta wayam taga falon, ko shakka babu ta wuce, wannan abu bai mata dadi ba gaskiya, zama tayi na kusan mintin goma tana tunane tanane lamarin Aslam ya mugun daure mata kai, yana son danta amma yace ita baya son ta to ko shakka babu wagga batu karya ce , jiki a sanyaye ta mike ta nufi upstairs tun kafin ta tura kofar dakin ta ringa jiyo dariyar shi shida yaron kamar zasu tada dakin, da sauri ta karasa ciki a kan gado ta hango su Aslam na kwance ya daura little akan kafarshi ya daga shi sama yana mishi lilo shi kuma yana ta kwasan dariya, ikon Allah tace a ranta, wannan lamarin da daure kai yake. Karasa wa ciki tayi ya dago yana kallon ta, rasa abin cewa yasa tace "sannu da dawowa." Sauke little yayi ya mike zaune yace mata "me ya kawo ta part din nan." Tace "kamar yaya." Hararan wasa ya watsa mata tare da cewa "kamar yayo." Dariya ta kwashe da shi tace "hira tazo muyi ko haramun ne kishiyoyi suyi hira a tare." Yace "bazan hana ki ba amma wlh kibi a hankali dan da kike ganin ta haka shalau shalau ba kanwar lasa bace." Dariya ya bata wai shalau shalau ta kuwa dara sosai tare da cewa " kai dai ka sani, koma ya take ai dai zabin ka ce, kuma sai na gaya mata." "Kin daɗe." Ya fada yana mikewa "muje ni da Allah ki bani abinci naci na kwaso yunwa da gajiyar aiki."
Ranar dai a part dinsu little ya wuni, a tsakanin su sai ji dashi suke yi suna wasa dashi, cikin kankanin lokaci yaron ya saba dasu, ko tunanin su maida mata ɗanta basu yi ba har gurin karfe taran dare, Asmah ce tayi hankalin cewa "Baza mu mayar mata da shi ba, kaga dare yayi kuma ita kaidai ce a part din ta nasan tana cen tana jira." Share ta yayi, sai da ta sake maimai tawa sannan ya kalle ta yace "A nan zai kwana." Bata rai yayi ya mike tare da daukar little suka wuce sama dan ma kar ta samu daman yi mai wani magana, baya jin zai iya rabuwa da yaron koda na minti daya ne ba tare da wani kwakwarar dalili ba, zama tayi tayi shiru tana tunani, gaskiya basu kyauta wa zee ba idan suka yi haka, to amma ya ta iya, yanzu yanda ya haɗe ran nan tana magana cibi zai zama kari, a tsakiyar su yaron ya kwana ranan dan tsabar gata.
A bangaren zee kuwa hakan bai dame ta ba, sai ma dadi da ya mata, domin duk wanda ke kaunar danka ai masoyin ka ne, ko iya haka suka tsaya wlh sun nuna mata soyayya, a bangare daya kuma abin da ya faru dazu yana tsungulin ta a rai, sai dai tana danne wa , duk yadda sheɗan yaso yasa ta taga bakin Asmah taƙi yarda duk yadda zuciya ta hasaso mata sai ta kauce, ta daukar ma kanta alkawari tun da Asmah bata nuna mata wani mugun hali ba to kuwa ita baza ta nuna mata komai ba zata jata a jikin ta su zama kamar yan uwa hakan ma wani mata ki ne da zata samu kusanci da burin ranta.
Washe gari daker ya tafi aiki karshe ma cewa yayi zai tafi da yaron, daka tsallen albarka tayi ta hana, dan tasan idan har ta kuskura ta bashi wannan daman so daya ya dinga yi kenan kuma bazai maida hankali kan aikin shi ba. Yana tafiya ta dauke shi suka tafi part din zee dama sun riga sunyi wankan su sun karya. Da fara'a ta tare su babu alamun damuwa a fuskar ta, bayan sun gaisa Asmah tace "sai kika jimu shiru jiya ko." Murmushi tayi tace "ba komai ai yaro ya koma wajen Asalin mummy shi." Hakan data fada yama Asmah dadi take ita ma ta fara bata labarin yadda Aslam ya karbi yaron da yadda ya dinga mai harda cewa da yayi zai tafi dashi office, dariya zee ta ringa yi zuciyar ta wasai, Asmah ta bata wannan labarin ne dan ta faran ta mata rai kuma ta kwantar mata da hankali , aiko dai kwalliya ta biyu kudin sabulu, ranar a part din zee ta wuni tuni wani irin sabo da shaƙuwa ya shiga tsakanin su kamar ba kishiyoyi ba tare sukayi girki anan Asmah taga basu da kayan abinci sai wanda ta siya ta kuma kudiri aniyar yiwa Aslam magana, sai gurin karfe ukun rana ta koma shiyar ta ta daura ma Aslam girki, tuwon shinkafa tayi lafiyayye kuma gaba daya ta girka harda zee, tako ji dadi ta amsa tana ta mata godiya.
Cikin abinda baifi sati daya ba sun gama fahimtar juna, duk da kowacce zuciyar ta cunkushe yake da kishi musammam ma zee dan ita Asmah har yanzu bata San dawan garin ba tunda kullum tana tare da miji, zee na matuaƙar kokarin danne wa amma fa kullum Daren duniya sai tasha kuka ta gode Allah, Aslam gaba daya bata gaban shi kasancewar yanzu tana yawan zuwa part din Asmah dan tare ma suke hada dinner kullum duk idan ranar tayi rashin sa'a suka hadu takan gaishe shi, a dake yake amsa mata kuma kallo daya yake mata babu kari wannan abin shi yafi komai kona mata rai, bata da matsala ko kaɗan da Asmah sai wanda ba'aka rasa ba, little kam zuwa yanzu ya zama mai uwaye biyu yau ya kwana a nan gobe ya kwana a nan duk dai inda yaga dama.
Yau ma kamar kullum tare suka gama haɗa dinner, sunayi suna hira, Asmah ce ta fara kawo zancen Aslam cikin firan nasu, da sauri zee ta kauda maganar ta canza wata hiran Asmah ta lura sau da yawa haka take mata da ta dauko zancen Aslam zata doje, tausayi take bata sosai na yadda Aslam ya wofintar da ita, sau da yawa takan auna kanta a matsayin zee taga idan ita ake wa haka zata iya jura kuwa, duk sanda tayi wannan tunanin takan jinjina wa zee da hannu bibbiyu. Bayan sun kammala hada mata nata a basket Asmah tayi kamar yadda take yi kullum, dauka tayi ta tashi dan lokacin dawowar Aslam yayi daf, cikin tsokana tace ma little "muje." noƙe kafada yayi alamar bazai bita ba dariya suka zaka mai tace "dama tsokanar nake yi zaman ka wurin mummyn ka." Har takai kofa yace "Mummah." Ta juyo yace "kar kiyi kuka yau kinji." Kallon juna sukayi da Asmah, Asmah tace "kuka kuma?" Murmushin yaƙe tayi tace "shirmen little ne kawai rabu dashi." Tana gama fadin haka ta sa kai tabar part. Kuka kuka haka tayi ta maimaita kalman, tabbas yaro baya karya, to meke saka ta kuka ne, da sauri ta kalli little dake ta wasan shi tace "my boy Mummah ka na kuka kace." Yace "eh mana mummy kullum sai tayi kuka da daddare, ta ringa cewa Allah ya dawo mata da hankalin mijin ta,Allah yasa ya yafe mata, zuciyar ta zata fashe." Zama tayi dabass tana maimaita innalillahi wainnailaihi rajiun, lallai suna shiaga hakkin zee, baiwar Allah a she tana cikin damuwa har haka amma ko a fuska bata taba nunawa ba, kila ma tana jin haushin ta , kila ma ta ringa ganin kamar ita ta hana Aslam dawowa gare ta, tasan ba abinda baza ta ayya na ba tun da dai ita zuciya ai bata da ƙashi lallai Aslam yau ya dawo zata same shi suyi magana ta fahimtar juna.