Sashe 46
Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kashe wutar dakin yayi ya nufi kan bed d'in ya janyo amarya sa,.
Tabdijan wannan irin cafta haka ba dani ba alkur'an, bazan tsaya ayi kisa a gabana,Amira Allah yajiƙan ki, nidai na tafi da safe nazo dubiya.
~ZAHRA~
Yan kai amarya sun isa lafiya, kuma alhamdulillahi sun samu tarba na musamman daga yan uwan Barr, zahra na rungume jikin ummi sai kuka takeyi gwanin tausayi har zazzabin dole ya kamata, dayake da dare suka iso yasa ba daman komawa ranan dole su kwana, gidan ta daya da uwar gidan Barr saidai part din kowa dabam haka shima mai gidan part dinshi daban wacce keda girki taje part d'in miji,.
Uwargida maryama itama yau tayi taronta, kawayenta ta tara manyan mata suka zauna sai yada habaici sukeyi suna zagin dangin amarya dana ango,.
Bayan an natsa ummi tace ma wata kanwar mummy data zo biki , ya kamata su kai zahra gurin uwar gidan shi, tunda gobe da sassafe zasu dauki hanyar minna.
Haka ko akayi ummi da anty Jamila suka saka zahra a tsakiya suka nufi part din maryama, falon damkam yake da kawayenta ana zaune sai ciye ciye da shaye shaye suke suna yada habaici, sun kunna speaker sun kure volume wakar anty uwar gida na tashi.
Su ummi na sawo kai wakar,
Kusa kidan antynmu uwargida ♪
Anty muna gaishe ki uwargida♪
An buga an barki uwargida♪
Allah gatanki. uwargida♪
Kin darasu da maki. uwargida♪
Mijin na kaunarki. uwargida♪
Kuma yay miki maki uwargida♪
Anty dole su barki uwargida♪
Labule asirin daki. uwargida♪
Yama su sallama anty Jamila ta rike baki tare da cewa tohfa, haka dai suka daure suka karasa bakin kofar suka yi sallama, wata kanwar maryama ne Mara kunya tazo ta bude , tana ganin su taja wani dogon tsaki kamar dogon bakinta zai tsinke, sannan ta buga musu harara daga sama har kasa, ta juya ta koma ciki, sun kusa kwashe 10 minutes a tsaye anty Jamila sai buga tsaki takeyi tana ƙari, ummi kam sai hakuri take bata, candai ta gaza jurewa ta kama hannu zahra dana ummi tace, "wlh bazai yuwu ba kuzo mu wuce sai kace wasu yan iska zasu barmu a tsaye, shiru shiru fa ba tsoro bane" cikin haka yarinyar ta kara bude kofar ta jefe su da wani wulakantaccen kallo kafin tace "ku shigo" ta juya abinta,.
Anty Jamila tace "umminsu baza mu shiga ba mu wuce kawai " ummi tace "ba'a yi haka ba anty jamy bari mu shigan dai tunda muke nema".
Badan ran anty Jamila taso ba ta bi ummi suka shiga, hamshakiya maryama tana hakimce tana zuba mulki taci kwalliya da wata uwar lessi kamar itace amaryar, fuskar nan ta dau makeup bajau, duk kawayenta sun ciccika kujerun falon ba wani sauran guri da su ummi zasu zauna, kuma ba wacce tayi niyar basu guri dan su zauna d'in,kuma ba wacce tace musu ƙala, wannan lamari ya matukar kona ran anty jamy , ji take kamar ta tanka, amma tasan in ta tanka rigima ne zai barke , karshe azo ace dangin amarya sunbi uwar gida har daki sun zageta,.
Daga tsayen da suke ummi tace "bayin Allah sannun ku", shiru ba wacce ta tanka saima bisu da kallon banza da suke yi, ummi ta sake cewa "uwar gidan Barr muke nema mun kawo mata amarya ne" daga bayan su sukaji wata hamshakiyar murya tace "gani nan turmin tsakar gida nake sha luguden mahassada, uwar gida saurautar gida nice ta fari nicen uwar yayan gida, duk wata karamar yar iskar data auran min miji, wlh nayi mata alkawarin cin burauba ta, da kafarta zata fita tabar min gidana da takalma a hannu dan uban ubanta, gidana daga ni sai mijin sai yayana babu wata karamar yar iskan data isa ramin kura sai yayanta," yan koranta ne suka dauki sowa tare da rangada bude suka shiga jero mata kirari
Ummi tuni ranta ya gama baci da wannan irin cin mutumcin da maryama ta musu, amma matsayin ta na babba kuma mai hankali da ilimi yasa ta danne zuciyar ta, anty Jamila kam kasa hakura tayi ta zabga shewa tare da cewa"ai wallahi maryam kike kowa,baki cika babban ƙwaruwa ba tunda har kikayi saken da mijiki, ya kalli wata mace a waje har ya sota ya kuma bada sadaki dan ya mallaketa ba, inda kin cika Babbar yar iska kamata yayi ki hana ayi auren bawai bayan anyi kizo kina cikawa mutane kunne da kurarin banza ba, kuma fatima zahra kainuwace dashen Allah ta shigo gidan nan kenan ita da barrister mutu ka raba,saidai ke ki fita ki bata fili tunda ke jakace wawiya mara hankali jahila kawai".
Wai wai wai jar ubancen, nan yan koran maryama sukayo caaa akan anty jamy harda masu shan gabanta kamar zasu daketa, ita kuma mandiyan na zaune kafa daya kan daya, duk da zagin da anty Jamila ta mata ba karamin dukan zuciyar ta yayi ba.
Ganin haka yasa ummi sauri damkar hannayensu ita da zahra suka bar part d'in cikin sauri,.
Suna shiga daki zahra ta fada kan gadonta ta fashe da wani irin marayan kuka, aiko anty jamy da ranta ke bace ta hau kanta da masifa tana cewa "ki zauna dai da wannan raguwar zuciyar taki ,wlh inbaki tashi tsaye , bakar wuya zakisha a hannun wannan yar iskan kishiyar taki, shiyasa batula ke burgeni kuma nake ɗasawa da ita , wlh ita ta biyo gida sak, kin zauna kina zubar ma kishiya hawaye sai kace ba jinin mu ba, tir da wannan raguwar zuciya taki," ganin abin na Neman yin yawa yasa ummi ta shiga kakkare Zahra tana ba anty jamy hakuri.
Ummi saida ta raba dare tana ma zahra nasiha , da koya mata dabarun zama da kishiya, take taji zuciyar ta yadan karfafa, ga kuma hargagin anty jamy shima ya taimaka.
A haka suka kwana ran kowa a dagule washe gari kuwa ko haske gari bai gama yi ba aka kawo musu motocin da zai maida su minna, dan su suka bukaci hakan.
Haka zahra ta wuni ita kadai taci kuka ta gode Allah, an kawota an barta, ita kadai , hmmmm aure kenan babu inda baya kai mace.
Sai dangin Barr dake dan zuwa baki da suka zo biki daga nisa suna son su koma, shine suke ta zuwa ganin dakin amarya.
Hankalin zahra ya kwanta ganin yadda dangi miji ke sonta suna haba haba da ita, sai yada maganganu sukeyi akan maryama , da alama kam ita da dangin miji basa ga maciji, ita ba ruwanta murmushi kawai take binsu dashi.
Abincinta daga can family hause dinsu Barr aketa kawo mata safe rana dare, abinci mai rai da motsi, ta dan caccakura ta barshi kasancewar bata cikin yanayi mai dadi.
Sai wurin karfe tara Barr ya shigo gidan zuwa lokacin ba kowa dan yan ganin daki tun magriba kafarsu ta dauke.
Cike da jin kunyar shi ta tsuguna har kasa tana gaishe shi, yaji daɗin hakan kuwa tunda Dama su nufawa tambarin su kenan ladabi, shiyasa take son ta fara koya tun da zafi zafi donta saba tun wuri, kar nan gaba tazo ta samu matsalar zama da dangin shi.
Hannunta ya kama ya mikar da ita tsaye ya zaunar da ita kan cinyar shi, kunya kamar tace kasa ya tsage ta shige haka take ji, murmushi yayi yace "Babyn Adam bana son irin wannan gaisuwar tsakanina dake indai ba cikin mutane muke ba", girgiza kai tayi alamar to, yasake cewa "kinci abinci" nan ma dakai ta amsa mai, murmushi yayi ganin alamar duk a tsorace take dashi,.
Hannunta ya rike suka nufi bedroom, dinta alwala yace taje tayi a toilet ba musu kuwa tayi bayan ta fito shima ya shiga yayi, sallah yajasu raka'a biyu bayan sun idar ya kama goshinta yayi addu'o'i, mikewa yayi ya dauko mata kayan bacci a wardrobe ya bata yace ta sanya yana zuwa fita yayi daga dakin zuwa nashi dakin dan yayi shirin kwanciya shima,.
Saida ta gama saƙe saƙen tasa ne ko kar tasa itafa gaba daya a tsorace tace, ƙudunbale tayi ta saka rigar dan kar yace daga zuwanta har ta fara mai rashin biyayya tana sakawa ta haye gado ta kudundune cikin bargo,.
Saida ya gama abinda zaiyi ya kulle ko ina dama ya riga ya sallami maryama tsiya tsiya ma suka rabu , badan yakai zuciya nesa ba daya shashara mata mari da daddaren nan ma,.
Ganinta gudundune a bargo yasa shi sakin miskilin murmushi, ya fahimci gaba daya a tsorace take dashi, shikam ba sauri yakeyi ba zai bita a hankali har sai ta saki jiki dashi tukunna zai kusanceta, yuwar ta dai ta zama mallakin shi , hankalin shi ya kwanta, shi ba yaro bane yasan yadda zai lallaba abarshi har ita da kanta ta mika wuya,.
Hawa gadon yayi bayan ya kashe wutar dakin, jawota yayi jikin shi ya rungumeta, gabanta ne ya shiga faduwa da karfi har yana jin sautin shi kasancewar manner suke da juna, peck ya kai mata a goshi tare da cewa "ki kwantar min da hankalinki babyn Adam babu abinda zan miki bayan hakan, bacci kawai zamuyi mu huce gajiyan biki", gyada mai kai tayi kafin ta shiga sauke ajiyar zuciya, hankalinta ya kwanta, take bacci mai daɗin gaske ya kwashe ta,
Ba dole ba hajiya zahra anji ɗumin jikin miji..........
~ASLAM ~
Oum ummeetarh
07041130088
Share
And
Comment
Fisabillilah🙏..💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wanna book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu}
Page 85 & 86
~ASLAM~
Zuwa yanzu jikin Aslam yayi sauki sosai har idan ba mutum ya Sani ba bazai taba yarda yayi wani ciwo makamancin wannan ba, ramace dai kawai yayi sai kuma hasken daya kara, hakan ko ba karamin kyau ya karamai ba,.
Washe garin ranar da aka miƙa amare dakin su ranar lahadi kenan, a ranar aka bashi sallama daga asibiti, babu kowa a tare dashi a lokacin sai Abba, bayan Abba ya gama biyan duk abinda ya kamata a biya, wani cleaner ya hahhaɗa musu kayan su zuwa motar Abba.
Tabdijan wannan irin cafta haka ba dani ba alkur'an, bazan tsaya ayi kisa a gabana,Amira Allah yajiƙan ki, nidai na tafi da safe nazo dubiya.
~ZAHRA~
Yan kai amarya sun isa lafiya, kuma alhamdulillahi sun samu tarba na musamman daga yan uwan Barr, zahra na rungume jikin ummi sai kuka takeyi gwanin tausayi har zazzabin dole ya kamata, dayake da dare suka iso yasa ba daman komawa ranan dole su kwana, gidan ta daya da uwar gidan Barr saidai part din kowa dabam haka shima mai gidan part dinshi daban wacce keda girki taje part d'in miji,.
Uwargida maryama itama yau tayi taronta, kawayenta ta tara manyan mata suka zauna sai yada habaici sukeyi suna zagin dangin amarya dana ango,.
Bayan an natsa ummi tace ma wata kanwar mummy data zo biki , ya kamata su kai zahra gurin uwar gidan shi, tunda gobe da sassafe zasu dauki hanyar minna.
Haka ko akayi ummi da anty Jamila suka saka zahra a tsakiya suka nufi part din maryama, falon damkam yake da kawayenta ana zaune sai ciye ciye da shaye shaye suke suna yada habaici, sun kunna speaker sun kure volume wakar anty uwar gida na tashi.
Su ummi na sawo kai wakar,
Kusa kidan antynmu uwargida ♪
Anty muna gaishe ki uwargida♪
An buga an barki uwargida♪
Allah gatanki. uwargida♪
Kin darasu da maki. uwargida♪
Mijin na kaunarki. uwargida♪
Kuma yay miki maki uwargida♪
Anty dole su barki uwargida♪
Labule asirin daki. uwargida♪
Yama su sallama anty Jamila ta rike baki tare da cewa tohfa, haka dai suka daure suka karasa bakin kofar suka yi sallama, wata kanwar maryama ne Mara kunya tazo ta bude , tana ganin su taja wani dogon tsaki kamar dogon bakinta zai tsinke, sannan ta buga musu harara daga sama har kasa, ta juya ta koma ciki, sun kusa kwashe 10 minutes a tsaye anty Jamila sai buga tsaki takeyi tana ƙari, ummi kam sai hakuri take bata, candai ta gaza jurewa ta kama hannu zahra dana ummi tace, "wlh bazai yuwu ba kuzo mu wuce sai kace wasu yan iska zasu barmu a tsaye, shiru shiru fa ba tsoro bane" cikin haka yarinyar ta kara bude kofar ta jefe su da wani wulakantaccen kallo kafin tace "ku shigo" ta juya abinta,.
Anty Jamila tace "umminsu baza mu shiga ba mu wuce kawai " ummi tace "ba'a yi haka ba anty jamy bari mu shigan dai tunda muke nema".
Badan ran anty Jamila taso ba ta bi ummi suka shiga, hamshakiya maryama tana hakimce tana zuba mulki taci kwalliya da wata uwar lessi kamar itace amaryar, fuskar nan ta dau makeup bajau, duk kawayenta sun ciccika kujerun falon ba wani sauran guri da su ummi zasu zauna, kuma ba wacce tayi niyar basu guri dan su zauna d'in,kuma ba wacce tace musu ƙala, wannan lamari ya matukar kona ran anty jamy , ji take kamar ta tanka, amma tasan in ta tanka rigima ne zai barke , karshe azo ace dangin amarya sunbi uwar gida har daki sun zageta,.
Daga tsayen da suke ummi tace "bayin Allah sannun ku", shiru ba wacce ta tanka saima bisu da kallon banza da suke yi, ummi ta sake cewa "uwar gidan Barr muke nema mun kawo mata amarya ne" daga bayan su sukaji wata hamshakiyar murya tace "gani nan turmin tsakar gida nake sha luguden mahassada, uwar gida saurautar gida nice ta fari nicen uwar yayan gida, duk wata karamar yar iskar data auran min miji, wlh nayi mata alkawarin cin burauba ta, da kafarta zata fita tabar min gidana da takalma a hannu dan uban ubanta, gidana daga ni sai mijin sai yayana babu wata karamar yar iskan data isa ramin kura sai yayanta," yan koranta ne suka dauki sowa tare da rangada bude suka shiga jero mata kirari
Ummi tuni ranta ya gama baci da wannan irin cin mutumcin da maryama ta musu, amma matsayin ta na babba kuma mai hankali da ilimi yasa ta danne zuciyar ta, anty Jamila kam kasa hakura tayi ta zabga shewa tare da cewa"ai wallahi maryam kike kowa,baki cika babban ƙwaruwa ba tunda har kikayi saken da mijiki, ya kalli wata mace a waje har ya sota ya kuma bada sadaki dan ya mallaketa ba, inda kin cika Babbar yar iska kamata yayi ki hana ayi auren bawai bayan anyi kizo kina cikawa mutane kunne da kurarin banza ba, kuma fatima zahra kainuwace dashen Allah ta shigo gidan nan kenan ita da barrister mutu ka raba,saidai ke ki fita ki bata fili tunda ke jakace wawiya mara hankali jahila kawai".
Wai wai wai jar ubancen, nan yan koran maryama sukayo caaa akan anty jamy harda masu shan gabanta kamar zasu daketa, ita kuma mandiyan na zaune kafa daya kan daya, duk da zagin da anty Jamila ta mata ba karamin dukan zuciyar ta yayi ba.
Ganin haka yasa ummi sauri damkar hannayensu ita da zahra suka bar part d'in cikin sauri,.
Suna shiga daki zahra ta fada kan gadonta ta fashe da wani irin marayan kuka, aiko anty jamy da ranta ke bace ta hau kanta da masifa tana cewa "ki zauna dai da wannan raguwar zuciyar taki ,wlh inbaki tashi tsaye , bakar wuya zakisha a hannun wannan yar iskan kishiyar taki, shiyasa batula ke burgeni kuma nake ɗasawa da ita , wlh ita ta biyo gida sak, kin zauna kina zubar ma kishiya hawaye sai kace ba jinin mu ba, tir da wannan raguwar zuciya taki," ganin abin na Neman yin yawa yasa ummi ta shiga kakkare Zahra tana ba anty jamy hakuri.
Ummi saida ta raba dare tana ma zahra nasiha , da koya mata dabarun zama da kishiya, take taji zuciyar ta yadan karfafa, ga kuma hargagin anty jamy shima ya taimaka.
A haka suka kwana ran kowa a dagule washe gari kuwa ko haske gari bai gama yi ba aka kawo musu motocin da zai maida su minna, dan su suka bukaci hakan.
Haka zahra ta wuni ita kadai taci kuka ta gode Allah, an kawota an barta, ita kadai , hmmmm aure kenan babu inda baya kai mace.
Sai dangin Barr dake dan zuwa baki da suka zo biki daga nisa suna son su koma, shine suke ta zuwa ganin dakin amarya.
Hankalin zahra ya kwanta ganin yadda dangi miji ke sonta suna haba haba da ita, sai yada maganganu sukeyi akan maryama , da alama kam ita da dangin miji basa ga maciji, ita ba ruwanta murmushi kawai take binsu dashi.
Abincinta daga can family hause dinsu Barr aketa kawo mata safe rana dare, abinci mai rai da motsi, ta dan caccakura ta barshi kasancewar bata cikin yanayi mai dadi.
Sai wurin karfe tara Barr ya shigo gidan zuwa lokacin ba kowa dan yan ganin daki tun magriba kafarsu ta dauke.
Cike da jin kunyar shi ta tsuguna har kasa tana gaishe shi, yaji daɗin hakan kuwa tunda Dama su nufawa tambarin su kenan ladabi, shiyasa take son ta fara koya tun da zafi zafi donta saba tun wuri, kar nan gaba tazo ta samu matsalar zama da dangin shi.
Hannunta ya kama ya mikar da ita tsaye ya zaunar da ita kan cinyar shi, kunya kamar tace kasa ya tsage ta shige haka take ji, murmushi yayi yace "Babyn Adam bana son irin wannan gaisuwar tsakanina dake indai ba cikin mutane muke ba", girgiza kai tayi alamar to, yasake cewa "kinci abinci" nan ma dakai ta amsa mai, murmushi yayi ganin alamar duk a tsorace take dashi,.
Hannunta ya rike suka nufi bedroom, dinta alwala yace taje tayi a toilet ba musu kuwa tayi bayan ta fito shima ya shiga yayi, sallah yajasu raka'a biyu bayan sun idar ya kama goshinta yayi addu'o'i, mikewa yayi ya dauko mata kayan bacci a wardrobe ya bata yace ta sanya yana zuwa fita yayi daga dakin zuwa nashi dakin dan yayi shirin kwanciya shima,.
Saida ta gama saƙe saƙen tasa ne ko kar tasa itafa gaba daya a tsorace tace, ƙudunbale tayi ta saka rigar dan kar yace daga zuwanta har ta fara mai rashin biyayya tana sakawa ta haye gado ta kudundune cikin bargo,.
Saida ya gama abinda zaiyi ya kulle ko ina dama ya riga ya sallami maryama tsiya tsiya ma suka rabu , badan yakai zuciya nesa ba daya shashara mata mari da daddaren nan ma,.
Ganinta gudundune a bargo yasa shi sakin miskilin murmushi, ya fahimci gaba daya a tsorace take dashi, shikam ba sauri yakeyi ba zai bita a hankali har sai ta saki jiki dashi tukunna zai kusanceta, yuwar ta dai ta zama mallakin shi , hankalin shi ya kwanta, shi ba yaro bane yasan yadda zai lallaba abarshi har ita da kanta ta mika wuya,.
Hawa gadon yayi bayan ya kashe wutar dakin, jawota yayi jikin shi ya rungumeta, gabanta ne ya shiga faduwa da karfi har yana jin sautin shi kasancewar manner suke da juna, peck ya kai mata a goshi tare da cewa "ki kwantar min da hankalinki babyn Adam babu abinda zan miki bayan hakan, bacci kawai zamuyi mu huce gajiyan biki", gyada mai kai tayi kafin ta shiga sauke ajiyar zuciya, hankalinta ya kwanta, take bacci mai daɗin gaske ya kwashe ta,
Ba dole ba hajiya zahra anji ɗumin jikin miji..........
~ASLAM ~
Oum ummeetarh
07041130088
Share
And
Comment
Fisabillilah🙏..💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wanna book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu}
Page 85 & 86
~ASLAM~
Zuwa yanzu jikin Aslam yayi sauki sosai har idan ba mutum ya Sani ba bazai taba yarda yayi wani ciwo makamancin wannan ba, ramace dai kawai yayi sai kuma hasken daya kara, hakan ko ba karamin kyau ya karamai ba,.
Washe garin ranar da aka miƙa amare dakin su ranar lahadi kenan, a ranar aka bashi sallama daga asibiti, babu kowa a tare dashi a lokacin sai Abba, bayan Abba ya gama biyan duk abinda ya kamata a biya, wani cleaner ya hahhaɗa musu kayan su zuwa motar Abba.