Sashe 78
Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bacci yake yi idanunshi a kulle fari sol ƙato da shi mai kama da Aslam sak, babu abinda ya banbantasu,kwata kwata bai dakko komai na zee ba, duk da mum da Dad basa kaunar Aslam hakan bai hana ɗanshi samun kyakkyawan matsuguni a zuciyoyin su ba, farat daya yaron ya shiga ransu, a kallo na farko.
Gaba ɗaya sun shagala da kallon yaron saida sukaji, muryar nurse tana musu magana sannan suka dawo hayyacinsu,saƙon Dr ta sanar musu na cewa da yayi su same shi a office, Dad ne yabi bayan nurse din zuwa office ɗuin Dr yayinda mum ta rungume yaron tsam a kirginta tanajin wani irin son shi da kaunar shi na huda kofofin zuciyarta.
Saida zee ta kwashe awa shidda kwarara tana barci kafin ta farka, wuraren la'asar, zuwa lokacin kam asibiti ya cika makil da yan'uwa da abokan arziki yan gayu masu abin hannu,yawancin su ma turawa ne wadan da su mum ke hulɗa dasu, kowa ya dauki yaron nan kallon daya zakaji ya shiga ranka, da alama dai baiwarsa ce hakan.
Zee ta farka da sauƙi sosai don bayan Dr ya duba ta, ya tabbatar musu nan da gobe ma za'a iya sallamarta taje gida abinta, bayan mum ta bata shayi mai zafi tasha ta kuma sha magunguna, sannan aka bada daman mutane su shiga su dubata, kowa barka yake mata, bata iya amsawa sai smiling kawai take musu, lokacin da aka bata babyn kuwa tsura mishi idanu tayi tana binshi da wani irin kallo, babu abinda take gani a fuska da jikin yaron sai Aslam dinta, take wani irin kewa da kaunar mijinta ya turniketa, rungume yaron tayi sosai a jikinta tana jin wani irin kaunar shi na huda zuciyar ta, bata San sanda ruwan hawaye ya wanke mata fuska ba, ta shiga risgan kuka harda sheshsheka, ganin haka yasa mum ta miƙa mata hannu alamar ta bata yaron girgiza mata kai tayi alamar A'a dole mum tayi hakuri ta bar mata abinta.
Zuwa dare babyn ya fara kuka, Dr yace ya kamata a bashi abinci yunwa yakeji, Dad yace Dr ya rubuta musu madaran da za'a dinga bashi yaje ya siyo, da mamakin su ji sukayi zee tace , A'a kar a siyo madaran ita zata shayar da ɗanta, Dr yace well dama haka ake bukata, nan wata nurse ta gyara mata shi sosai ta koya mata yadda zata rikeshi a yayinda da zata shayar da shi, nonon aka sa mai a baki ba shiri kuwa yaro ya kama yana tsotsa, duk da matsanancin zafin da takeji hakan baisa ta fasa shayar dashi ba, nurse din data fahimci tanajin zafi ta shiga kwantar mata da hankali da cewa karta damu zai daina, idan ya kwana biyu yana sha, shikenan baza ta kara jin zafi ba kuma.
A asibitin suka kwana zuwa washe gari ta ƙara samun sauki sosai don haka Dr ya rubuta musu sallama suka dawo gida, kulawa sosai zee ke samu daga gurin iyayenta ita da little Aslam dinta, wata babban nurse mai zaman kanta, wayayya mai wadataccen ilmi Dad ya daukar musu ita ke kula da komai nasu ita da babyn bangaren wanka tsaftar su da abincinsu, kai komai ma daya shafe su.
Zee taji dadin yadda iyayenta suka karbi yaron da yadda suke nuna mai kauna da kulawa, bata taɓa zaton haka ba, ganin yadda suka dauki karan tsana suka dorawa uban ɗan.
Kafin sati ya zagayo tayi bulbul ita da babynta gwanin sha'awa, jego takeyi na yayan gata, baza ayi taron suna ba, raɗin suna kawai za'ayi dad ne ya siya duk wani abinda ake bukata na radin suna kamar rago da sauransu,tambayarta sukayi sunan da take so a saka ma ɗanta babu kunya ko kara tace Muhammad Aslam, haka ko akayi, duk da Dad yaso ace sunanshi ta zabar wa yaron.
(kuji min Dad da ƙoƙari wai da sunanshi ta zaba😒 babu kunya ba tsoron allah cikin da yayi niayyar hallakawa)
Hankali kwance take jegonta bata da matsalar komai babu abida ke damunta sai kewar mijinta, bayan haihuwartan nan , abin ma saiya daɗa nunkuwà, kullum dashi take kwana take tashi a zuciyarta ji take kamar tayi tsunstuwa ta ganta a agabanshi, ta mika mishi ɗanshi, cikin farin ciki,ta kusa kai matakin da baza ta iya jurewa ba, jira takeyi yaronta yayi kwari, ta lashi takobin zata koma gidan mijinta koda son ransu ko babu, koda tsiya koda tsiya tsiya.
~9ja~
Yau kimanin wata biyar kanen da auren yan matan mummy,kuma har zuwa wannan lokacin cikinsu babu wacce ta taba zuwa gida da sunan ganin gida, kowacce tana gidanta hankali kwance, duk da kuwa cikinsu ba wacce batayi nacin son zuwa gida ba amma mazajen suka hana wannan kuwa umarnin alhaji baba ne.
Soyayya kamal da khadija ba'a magana, tattalin da kulawa suke ba juna na musamman, idan kaga yadda suke gudanàr da rayuwarsu zaka dauka sunyi shekara goma suna soyayya kafin suyi aure, a halin yanzu Khadijah Nada cikin ta dan wata huɗu.
Haka ma Amir da Amira sukam bama a magana, kalar nasu salon soyayya ta dabance, basa jin kunyar uban kowa a gaban kowa nuna ma juna soyayya sukeyi, ƙiri ƙiri mutane suka guji zuwa gidansu, saboda idan kaje indai kana da kunya, ta baza ka iya awa ɗaya a gidan ba,suma dai a kwai cikin ɗan luv, saidai fatan Allah ya raba lafiya.
Su batool ma yanzu komai nomal,babu abinda suke sai shan soyayya da cokali mai yatsu, bangaren yadda sukeji da cikin su kuwa ba'a cewa komai,tunkan a haife shi, shikaran kanshi cikin yasan shi dan gata ne, abinka da masu abin duk sati ake scanning, ta bangaren maah ma ba'a barta a baya ba, duk abinda ta gani indai na jariri ne siya takeyi ta ajiye, abin kwalama kuwa na masu cikin kullum cikin yi takeyi tana aikama batool dashi, bama ci takeyi ba wani bin saidai Dr yaci idan Wanda zai iya cine, ita dai barta da cabbage dinta, yanzu kam an samu ci gaba ta daina cinshi gaya, saidai ta kwada da kulikuli taci, rigima kam yayi sauƙi a gurin batool saidai kunsan ance mai hali baya fasa halinsa, duk da haka duk randa ya tabota haka zata kwana tana masifa, musamman yanzu da wata Dr a gurin aikinsu ta nace tana sonsa, tunda batool ta samu labari ya shiga uku ko minti talatin ya kara akan lokacin da yake dawowa haka zai sameta ta cika tayi fam, komai zai ce mata baza ta yarda ba kawai gurin Dr basira ya tsaya, kishin sa take sosai da sosai ji take da tana da hali da nikab zata saka shi ya dinga sakawa, saukin shi ma yanzu yana da loggonta data fara zai lalubeta ya fara sakar mata zafafan romance daga nan zancen zai mutun sai kuma na gobe.
A bangaren zahra kam, yanzu babu abida zamu ce sai alhmdllh, tsakaninta da miji babu komai sai tsantsar soyayya da kaunar juna, da gasken fa baby take a gurin Barr Adam ji yake da ita kamar Yar jinjira, musamman yanzu data samu ciki, kula yake bata na musamman kamar ya hadiyeta, tsakanin da maryama yanzu kuwa babu komai sai girmama juna da mutunta juna, dama zahra kwata kwata bata da matsala, matsalar daga maryama ne, kuma a halin yanzu gaba daya tayi laushi, bayan dawowarta Barr a gaba ya sakata ya mata nasiha tare da sanar da ita wlh ta gode ma Allah daya haɗa ta da kishiya irin Zahra bata samu mai irin halinta, nan ya sanar da ita cewa zahra ce ta tirsasa shi ya dawo da ita badan haka ba da har yanzu tana cen, take taji wani nadama ya shige ta lallai ta gode ma Allah dabai haɗa ta da mai irin mugun halinta ba don ta Tabbatar inda itace a matsayin zahra,da wlh zahra tabar gidan kenan har a bada asaidai a bita da takardan ta, tayi nadama, ta tuba taubatan nasuha, washe gari kuwa har part ɗin zahra taje ta same ta nemi gafarar abinda ta mata, Allah sarki zahra dama bata riketa a raiba, nan dai tace ta yafe mata, tashi tayi ta rungume ta tana mata godiya, a haka Barr ya samesu, ba karamin dadi yaji a ranshi ba, take ya haɗa su ya nusu nasiha, tare da nuna musu irin tsantsar farin cikin da yake ciki a ranar saboda hada Kansu da sukayi, tun daga ranar kuwa suke zaune lafiya abin su, yara yanzu sun zama yan gata masu uwaye biyu, maryama suna kiranta da mummy zahra kuma suna kiranta da mum, dakinsu nanan a part din zahra data ware musu, lafiyayye Dan yama fi dakinsu na part din maryama haɗuwa, in sunga dama su kwana a gurin mummy insun ga dama su kwana gurin mum, maryama ce ta fara gane zahra nada ciki, aiko dai tayi farin ciki har zuciyar ta, take ta shiga tsokanarta tana kiranta da maman yan biyu, tun zahra na daukar abin da wasa har dai lamarin ya tabbata, saidai muyi fatan Allah ya raba lafiya.
A bangaren su Asmah kam yanzu sun wuje romeo da Juliet, soyayya suke zubawa kamar zasu cinye juna, da'ker da sidin goshi Asmah ta samu Aslam ya koma wajen aiki, shima da yarjejeniyar, yana aiki suna video call, haka dai tace mishi ta yarda, ta samu ta lallabashi ya tafi ranar farko daya fara zuwa, yana isa ko office bai shiga ba ya kirata ƙin ɗagawa tayi dan burinta a halin yanzu bai wuce ya maida hankali kan aikinshi ba, cikin abinda baifi awa daya ba ya mata missed call yafi hamshi ta share, aiko dai ko Rabin a waya bai kara ba saijin horn din motar shi tayi ya dawo, washe gari kuwa kin tafiya aikin yayi, ganin dai da gaske yakeyi, yasa itama ta ɓata rai ta daina kula shi ta fita sabgarshi, ta daina kwana tare dashi, kwana biyu suka kwashe a haka gaba dayan su sunji jiki, ba shiri yace mata yaji ya yarda zai koma aiki, amma sai inzasu dinga yin waya duk bayan awa ɗaya, ba yacce ta iya haka ta amice, amma da sharidin duk kira ɗaya bazai wuce 5 minutes ba, shima haka ya amince, da haka ta samu ya koma office.
Gaba ɗaya sun shagala da kallon yaron saida sukaji, muryar nurse tana musu magana sannan suka dawo hayyacinsu,saƙon Dr ta sanar musu na cewa da yayi su same shi a office, Dad ne yabi bayan nurse din zuwa office ɗuin Dr yayinda mum ta rungume yaron tsam a kirginta tanajin wani irin son shi da kaunar shi na huda kofofin zuciyarta.
Saida zee ta kwashe awa shidda kwarara tana barci kafin ta farka, wuraren la'asar, zuwa lokacin kam asibiti ya cika makil da yan'uwa da abokan arziki yan gayu masu abin hannu,yawancin su ma turawa ne wadan da su mum ke hulɗa dasu, kowa ya dauki yaron nan kallon daya zakaji ya shiga ranka, da alama dai baiwarsa ce hakan.
Zee ta farka da sauƙi sosai don bayan Dr ya duba ta, ya tabbatar musu nan da gobe ma za'a iya sallamarta taje gida abinta, bayan mum ta bata shayi mai zafi tasha ta kuma sha magunguna, sannan aka bada daman mutane su shiga su dubata, kowa barka yake mata, bata iya amsawa sai smiling kawai take musu, lokacin da aka bata babyn kuwa tsura mishi idanu tayi tana binshi da wani irin kallo, babu abinda take gani a fuska da jikin yaron sai Aslam dinta, take wani irin kewa da kaunar mijinta ya turniketa, rungume yaron tayi sosai a jikinta tana jin wani irin kaunar shi na huda zuciyar ta, bata San sanda ruwan hawaye ya wanke mata fuska ba, ta shiga risgan kuka harda sheshsheka, ganin haka yasa mum ta miƙa mata hannu alamar ta bata yaron girgiza mata kai tayi alamar A'a dole mum tayi hakuri ta bar mata abinta.
Zuwa dare babyn ya fara kuka, Dr yace ya kamata a bashi abinci yunwa yakeji, Dad yace Dr ya rubuta musu madaran da za'a dinga bashi yaje ya siyo, da mamakin su ji sukayi zee tace , A'a kar a siyo madaran ita zata shayar da ɗanta, Dr yace well dama haka ake bukata, nan wata nurse ta gyara mata shi sosai ta koya mata yadda zata rikeshi a yayinda da zata shayar da shi, nonon aka sa mai a baki ba shiri kuwa yaro ya kama yana tsotsa, duk da matsanancin zafin da takeji hakan baisa ta fasa shayar dashi ba, nurse din data fahimci tanajin zafi ta shiga kwantar mata da hankali da cewa karta damu zai daina, idan ya kwana biyu yana sha, shikenan baza ta kara jin zafi ba kuma.
A asibitin suka kwana zuwa washe gari ta ƙara samun sauki sosai don haka Dr ya rubuta musu sallama suka dawo gida, kulawa sosai zee ke samu daga gurin iyayenta ita da little Aslam dinta, wata babban nurse mai zaman kanta, wayayya mai wadataccen ilmi Dad ya daukar musu ita ke kula da komai nasu ita da babyn bangaren wanka tsaftar su da abincinsu, kai komai ma daya shafe su.
Zee taji dadin yadda iyayenta suka karbi yaron da yadda suke nuna mai kauna da kulawa, bata taɓa zaton haka ba, ganin yadda suka dauki karan tsana suka dorawa uban ɗan.
Kafin sati ya zagayo tayi bulbul ita da babynta gwanin sha'awa, jego takeyi na yayan gata, baza ayi taron suna ba, raɗin suna kawai za'ayi dad ne ya siya duk wani abinda ake bukata na radin suna kamar rago da sauransu,tambayarta sukayi sunan da take so a saka ma ɗanta babu kunya ko kara tace Muhammad Aslam, haka ko akayi, duk da Dad yaso ace sunanshi ta zabar wa yaron.
(kuji min Dad da ƙoƙari wai da sunanshi ta zaba😒 babu kunya ba tsoron allah cikin da yayi niayyar hallakawa)
Hankali kwance take jegonta bata da matsalar komai babu abida ke damunta sai kewar mijinta, bayan haihuwartan nan , abin ma saiya daɗa nunkuwà, kullum dashi take kwana take tashi a zuciyarta ji take kamar tayi tsunstuwa ta ganta a agabanshi, ta mika mishi ɗanshi, cikin farin ciki,ta kusa kai matakin da baza ta iya jurewa ba, jira takeyi yaronta yayi kwari, ta lashi takobin zata koma gidan mijinta koda son ransu ko babu, koda tsiya koda tsiya tsiya.
~9ja~
Yau kimanin wata biyar kanen da auren yan matan mummy,kuma har zuwa wannan lokacin cikinsu babu wacce ta taba zuwa gida da sunan ganin gida, kowacce tana gidanta hankali kwance, duk da kuwa cikinsu ba wacce batayi nacin son zuwa gida ba amma mazajen suka hana wannan kuwa umarnin alhaji baba ne.
Soyayya kamal da khadija ba'a magana, tattalin da kulawa suke ba juna na musamman, idan kaga yadda suke gudanàr da rayuwarsu zaka dauka sunyi shekara goma suna soyayya kafin suyi aure, a halin yanzu Khadijah Nada cikin ta dan wata huɗu.
Haka ma Amir da Amira sukam bama a magana, kalar nasu salon soyayya ta dabance, basa jin kunyar uban kowa a gaban kowa nuna ma juna soyayya sukeyi, ƙiri ƙiri mutane suka guji zuwa gidansu, saboda idan kaje indai kana da kunya, ta baza ka iya awa ɗaya a gidan ba,suma dai a kwai cikin ɗan luv, saidai fatan Allah ya raba lafiya.
Su batool ma yanzu komai nomal,babu abinda suke sai shan soyayya da cokali mai yatsu, bangaren yadda sukeji da cikin su kuwa ba'a cewa komai,tunkan a haife shi, shikaran kanshi cikin yasan shi dan gata ne, abinka da masu abin duk sati ake scanning, ta bangaren maah ma ba'a barta a baya ba, duk abinda ta gani indai na jariri ne siya takeyi ta ajiye, abin kwalama kuwa na masu cikin kullum cikin yi takeyi tana aikama batool dashi, bama ci takeyi ba wani bin saidai Dr yaci idan Wanda zai iya cine, ita dai barta da cabbage dinta, yanzu kam an samu ci gaba ta daina cinshi gaya, saidai ta kwada da kulikuli taci, rigima kam yayi sauƙi a gurin batool saidai kunsan ance mai hali baya fasa halinsa, duk da haka duk randa ya tabota haka zata kwana tana masifa, musamman yanzu da wata Dr a gurin aikinsu ta nace tana sonsa, tunda batool ta samu labari ya shiga uku ko minti talatin ya kara akan lokacin da yake dawowa haka zai sameta ta cika tayi fam, komai zai ce mata baza ta yarda ba kawai gurin Dr basira ya tsaya, kishin sa take sosai da sosai ji take da tana da hali da nikab zata saka shi ya dinga sakawa, saukin shi ma yanzu yana da loggonta data fara zai lalubeta ya fara sakar mata zafafan romance daga nan zancen zai mutun sai kuma na gobe.
A bangaren zahra kam, yanzu babu abida zamu ce sai alhmdllh, tsakaninta da miji babu komai sai tsantsar soyayya da kaunar juna, da gasken fa baby take a gurin Barr Adam ji yake da ita kamar Yar jinjira, musamman yanzu data samu ciki, kula yake bata na musamman kamar ya hadiyeta, tsakanin da maryama yanzu kuwa babu komai sai girmama juna da mutunta juna, dama zahra kwata kwata bata da matsala, matsalar daga maryama ne, kuma a halin yanzu gaba daya tayi laushi, bayan dawowarta Barr a gaba ya sakata ya mata nasiha tare da sanar da ita wlh ta gode ma Allah daya haɗa ta da kishiya irin Zahra bata samu mai irin halinta, nan ya sanar da ita cewa zahra ce ta tirsasa shi ya dawo da ita badan haka ba da har yanzu tana cen, take taji wani nadama ya shige ta lallai ta gode ma Allah dabai haɗa ta da mai irin mugun halinta ba don ta Tabbatar inda itace a matsayin zahra,da wlh zahra tabar gidan kenan har a bada asaidai a bita da takardan ta, tayi nadama, ta tuba taubatan nasuha, washe gari kuwa har part ɗin zahra taje ta same ta nemi gafarar abinda ta mata, Allah sarki zahra dama bata riketa a raiba, nan dai tace ta yafe mata, tashi tayi ta rungume ta tana mata godiya, a haka Barr ya samesu, ba karamin dadi yaji a ranshi ba, take ya haɗa su ya nusu nasiha, tare da nuna musu irin tsantsar farin cikin da yake ciki a ranar saboda hada Kansu da sukayi, tun daga ranar kuwa suke zaune lafiya abin su, yara yanzu sun zama yan gata masu uwaye biyu, maryama suna kiranta da mummy zahra kuma suna kiranta da mum, dakinsu nanan a part din zahra data ware musu, lafiyayye Dan yama fi dakinsu na part din maryama haɗuwa, in sunga dama su kwana a gurin mummy insun ga dama su kwana gurin mum, maryama ce ta fara gane zahra nada ciki, aiko dai tayi farin ciki har zuciyar ta, take ta shiga tsokanarta tana kiranta da maman yan biyu, tun zahra na daukar abin da wasa har dai lamarin ya tabbata, saidai muyi fatan Allah ya raba lafiya.
A bangaren su Asmah kam yanzu sun wuje romeo da Juliet, soyayya suke zubawa kamar zasu cinye juna, da'ker da sidin goshi Asmah ta samu Aslam ya koma wajen aiki, shima da yarjejeniyar, yana aiki suna video call, haka dai tace mishi ta yarda, ta samu ta lallabashi ya tafi ranar farko daya fara zuwa, yana isa ko office bai shiga ba ya kirata ƙin ɗagawa tayi dan burinta a halin yanzu bai wuce ya maida hankali kan aikinshi ba, cikin abinda baifi awa daya ba ya mata missed call yafi hamshi ta share, aiko dai ko Rabin a waya bai kara ba saijin horn din motar shi tayi ya dawo, washe gari kuwa kin tafiya aikin yayi, ganin dai da gaske yakeyi, yasa itama ta ɓata rai ta daina kula shi ta fita sabgarshi, ta daina kwana tare dashi, kwana biyu suka kwashe a haka gaba dayan su sunji jiki, ba shiri yace mata yaji ya yarda zai koma aiki, amma sai inzasu dinga yin waya duk bayan awa ɗaya, ba yacce ta iya haka ta amice, amma da sharidin duk kira ɗaya bazai wuce 5 minutes ba, shima haka ya amince, da haka ta samu ya koma office.