Sashe 103
Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gaban ta ne ya yanke yayi wani irin faɗuwa rass, take ta ƙure yaron da kallo bata ko keftawa, ba kowa take gani ba fa ce Aslam a wasu shekaru masu ɗan nisa da suka shuɗe, lokacin da aka auro ta gidan tana amarya.
Dago da kai tayi ta kara kallon zee ta sake kallon little, ko shakka babu wannan jinin Aslam ne, ko shakka babu wannan jinin daddy da Abba ne ko shakka babu wannan yaron jinin Alhaji baba ne, babu bukatar ta tambayi ɗan waye domin ko makaho ne kuwa ya laluba zai tabbatar da hakan balle kuma ace mai ido biyu.
Durkushewa tayi ta maida tsawonta daidai na little kafin kuma ta kaima yaron wani irin runguma sannan ta fashe da kuka, ba komai ne ya saka mami kuka a daidai wannan lokacin ba face tunawa da irin yadda Aslam yake kaunar yaga gudan jinin shi a duniya, kamar yadda yake ta faɗi tashi yaga ya samu ɗan kanshi a doron ƙasa, ta fi kowa sanin sirrin Aslam tafi kowa sanin yadda yake kaunar yaga ya haihu, yana iya boye ma kowa sirrin shi a duniya amma banda ita zata iya rantsuwa banda Asmah data kasance abokiyar rayuwar shi itace mutum ta biyu da zata bugi kirji ta faɗi wanene Aslam.
Ɗagowa tayi tana share hawaye ta kalli zee tace "Zainab muje cikin gida wannan lamarin ba abinda zaki tunkare ni da shi ni kaɗai bane." Daukar little tayi ta ta rungume ta doshi part din Alhaji baba,yayin da zee ta rufa mata baya.
Kabbara Alhaji baba ya shiga yi a bayyane yayin da hajiya mama ta shiga sharar kwallah, a lokacin da suka yi arba da little. Tuni jikin zee yiyi sanyi mekefaruwa ne,to kodai Aslam ya mutune, take gabanta yayi wani irin mummunar faɗuwa, take itama hawaye suka shiga wanke mata fuska hannun mami dake zaune kusa da ita ta damke da karfi Wanda saida mami ta juyo a firgice ta kalle ta, ganin hawaye a fuskarta yasa mami bule baki da sauri da nufin tambayar ta mekefaruwa saidai muryar ta ya katse ma mami hanzari, cikin sheshekar kuka tace"Mami ya mutu ko, Aslam ya mutu ya barni ko."Da sauri mami ta shiga girgiza mata kai kafin ta bule baki tace "A'a zainab karki sake faɗin wannan Kalmar Aslam bai mutu ba yana nan da ranshi da lafiyar shi." Zubawa mami idanu tayi tana kallon ta bawai dan ta yarda da abin da take gaya mata ba, ita yanzu idan ba ganin Aslam tayi ido da ido ba babu wanda zai ce mata yana raye ta amince.
Mummy ce ta fara shigowa falon domin amsa kiran gaggawar da Alhaji Baba ya mata, a ruɗe take matuƙa don tasan irin wannan kiran gaggawa daga Alhaji baba, ba karamin muhimmin Abu bane, tana shigowa idanun ta akan little dake rungume a jikin hajiya mama ya sauke, wani irin wawan burki ta taka, yayin da doguwar sallamar da ta rafko ya katse, bakin ta ne ya shiga rawa alamar tana son ta furta wani Abu amma kuma ta kasa buɗe baki, hajiya mama ne tace tana share hawayen farin ciki"kyayi abinda yafi haka ma Aisha karaso ciki." Mami ne ta Ƙarasa gare ta ta riƙo hannunta zuwa cikin falon ta zaunar da ita kusa da hajiya mama, mummy kam dama bata iya ruɗewa ba, lokacin da tayi arba da zee sai ta kura mata ido kamar tana son ta tuno inda tasan ta harga Allah ji tayi kamar an mata formatting lin komai daga kwakwalwar ta.
Daidai nan daddy ya shigo Amir na biye dashi ko zama basuyi ba Abba ma ya rafko sallama, duk da suma sun kaɗu da ganin zee tare da yaro mai kama da Aslam hakan baisa sun ruɗe ba kasancewar su mazaje masu dakkakkiyar zuciya.zama sukayi domin amsa kiran Alhaji baba, babu Wanda ya furta koda A ne daga cikin su, domin duk sanda Alhaji baba yayi irin wannan kiran kowa natsuwa yake yi ya saurare shi babu mai ikon yin magana har sai yaba da umarnin yin hakan, kamal ma ya karaso daga gurin aiki yake ma ya dauki excuse ya taso, Allah yasa ba sa wani Abu mai mahimmanci.
Aslam kawai ake zaman jira kasancewar an bashi umarnin ya taho harda Asmah, kuma yana office dole saiya biya gida ya dauko ta hakan yasa yayi jinkirin isowa, falo yayi tsit sai kallo kallo akeyi a tsananin juna, fuskar kowa cike da zaƙuwan sonjin ta yaya akayi matankaɗi ya shiga gora, domin dai dukkanin su kallo daya suka ma little suka tabbatar cewa lallai shiɗin jinin su ne, kamar yadda yaron ya kasance mai farin jini da saurin shiga rai tun haihuwar sa, farin jinin shi nanan har yau babu abinda ya dakushe a ciki saima ƙaruwa da yayi, domin dukkansu a kallo ɗaya yaron ya shiga ransu kaunar shi ya kama zuciyoyin su kowanne su burin shi ya ɗauki yaron saidai babu daman yin hakan saboda girmama wa ga Alhaji baba har sai ya gama fadar abin da yasa ya tarasu sannan zasu samu daman yin hakan.
Bayan kamar minti goma da haduwar kowa da kowa a falon Alhaji baba, motar Aslam ta faka a farfajiyar gidan, jiki a sanyaye ya buɗe motar ya fito, tunda ya tashi barci yau gaban shi keta faɗuwa lokaci zuwa lokaci har sai da takai ya gayawa Asmah, abin da ke damun shi, har yake cewa shi bai da tafiya bazai iya fita office ba, ita ta karfafa mai gwuiwa tare da cewa yayta ambaton innalillahi wainnailaihi rajiun, a haka ta samu ta lallaɓa shi ya tafi. Lokacin da kiran gaggawa daga Alhaji baba ya riskeshi ji yayi bugun da kirjinshi keyi ya nunku fiye dana da.
A bangaren Asmah kam ita ma kwarai da gaske jikin ta a sanyaye yake tunda maganar kiran nan ya risketa haka kawai take ji a jikin ta wani Abu Mara daɗi zai bakunci rayuwar ta.
Kasa fitowa daga motar tayi saida ya buɗe Mata tare da cewa "bismillah husnah muje Allah yana tare da mu koma meke ciki in-sha Allahu zaizo mana da sauƙi." Mika mata hannu yayi yana sakar mata murmushin karfafa gwuiwa, itama martanin murmushin ta mayar mai kafin ta mika hannun ta ta saka cikin nashi ya mayar ya damƙe gam kamar wani zai kwace mishi ita a haka suka doshi falon Alhaji baba hannun su cikin na juna............
Oum Ummeetarh
07041130088
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya,Allah kajiqan iyayen mu}
*ASSALAMUALAIKUM SISTERS*
abun d mamaki Tayanda watan axumi yaketa qaratowa cikin Dan taqin lokaci,
Me kika tanadarwa kanki dama yaranmu yar uwa?
Munada kyawawan kayan Yara na dinki masu kyau sosay d bama zakice dinkawa akayiba yaro/yarinya sufito gwanin burgewa kowa yanasan barka,07046881166
Kayanmu sauqinsu yyi har kamar kyautane,zaki iya samunsu dga 2k harzuwa abunda yyi Sama,kizo kiyi sarin kayanmu kisamu alkhairi me tarin yawa,07046881166
Akway takalma Suma kyawawa dgakan 1k zuwa sama,07046881166
Sannan munada tsala tsalan frames d madubai n gyaran gida masukyau d arha sosay,07046881166
Akway leshina d atamfofi,abayas sewanda kikazaba duk a farashi mesauki,07046881166
Karna cikaku d surutu ku kira:07046881166 domin qarin bayani,karku manta alkhairin Tari maganin mantuwa zaku iyashiga Instagram handle namu don ganin kayayyakinmu: everythng_handmade,
Semunjiku 07046881166
Page 124
A tare suka haɗa baki wurin yin sallama kafin su sa kai cikin falon hannun su sarƙe da juna. Tunda ta jiyo muryar shi yayi sallama , zuciyar ta ya shiga wani irin luguɗen bugu da karfin gaske. Ƙofar shigowa falon ta kafe da idanun ta tana kallon jiran tsammani. Shine ya fara bayyana a falon kafin ita, kamar had'in baki daga shi har ita idanun su, akan fuskar zee ya sauka,wani irin wawan burki ya taka daga bakin ƙofar, yana bin ta da wani irin kallo mai cike da tsantsar mamaki. A firgice ta mik'e tsaye tare da zaro dukkan girman idanun ta waje, furgici da tashin hankali ne suka bayyana ƙarara akan fuskar ta, kallon Asmah take yi kamar wacce keson ta tantance shin ita d'in ce kokuwa idanunta ne ke mata gizo, mayar da idanunta tayi kan hannayensu dake sarƙe dana juna, sannan ta ƙara sauke idanunta akan Aslam dake tsaye yana kallon ta kamar wata sabuwar halitta.
Gaba d'aya mutanen falon shiru sukayi suka zuba musu idanu, cikin su ukun an rasa Wanda zai fara janye idanun shi daga kan wani, kowanne da ma'anar kallon da yake bin ɗan uwan shi da shi. Zee tana bin Asmah da Aslam ne da kallon furgici da tsananin tashin hankali tare tambayar kanta shin meye alaƙar mijin ta da Asmah da har suka shigo cikin falon Alhaji baba a tare hannunsu sarƙe da juna, duk da tasan ita d'in burin shi ce zabin shi ce abar kaunar shi ce, tun kafin ta bar gidan shi, amma bata taɓa kawo tunanin cewa bayan bata zai mallake ta ba, saboda a gaban ta ranar Alhaji baba ya tsayar da lokacin bikin ta da kamal a wancen ranar, shin menene alakar su? Take zuciyar ta ta bata amsa da cewa Aure, ji tayi numfashin ta na neman gagarar ta ja, indai ko alaƙar aure ne a tsakanin mijin ta da Asmah ta shiga ukun ta, domin ita shaida ce akan irin tsananin so da kaunar da yake ma Asmah wanda tana da tabbacin ko rabin rabinshi baya mata.
Asmah kam kallo tsoro da zallar madarar kishi take bin zee da shi, shin meya dawo da ita rayuwar su a daidai wannan lokacin? me tazo nema me ya kawo ta? A daidai lokacin data shaku da Aslam ta zama shi ya zama ita ta miƙa mishi dukkan ragamar rayuwarta, lallai akwai gwarama, don a yadda take kaunar Aslam a halin yanzu bata jin zata iya raba shi da wata p
ƴa mace a duniya.
Dago da kai tayi ta kara kallon zee ta sake kallon little, ko shakka babu wannan jinin Aslam ne, ko shakka babu wannan jinin daddy da Abba ne ko shakka babu wannan yaron jinin Alhaji baba ne, babu bukatar ta tambayi ɗan waye domin ko makaho ne kuwa ya laluba zai tabbatar da hakan balle kuma ace mai ido biyu.
Durkushewa tayi ta maida tsawonta daidai na little kafin kuma ta kaima yaron wani irin runguma sannan ta fashe da kuka, ba komai ne ya saka mami kuka a daidai wannan lokacin ba face tunawa da irin yadda Aslam yake kaunar yaga gudan jinin shi a duniya, kamar yadda yake ta faɗi tashi yaga ya samu ɗan kanshi a doron ƙasa, ta fi kowa sanin sirrin Aslam tafi kowa sanin yadda yake kaunar yaga ya haihu, yana iya boye ma kowa sirrin shi a duniya amma banda ita zata iya rantsuwa banda Asmah data kasance abokiyar rayuwar shi itace mutum ta biyu da zata bugi kirji ta faɗi wanene Aslam.
Ɗagowa tayi tana share hawaye ta kalli zee tace "Zainab muje cikin gida wannan lamarin ba abinda zaki tunkare ni da shi ni kaɗai bane." Daukar little tayi ta ta rungume ta doshi part din Alhaji baba,yayin da zee ta rufa mata baya.
Kabbara Alhaji baba ya shiga yi a bayyane yayin da hajiya mama ta shiga sharar kwallah, a lokacin da suka yi arba da little. Tuni jikin zee yiyi sanyi mekefaruwa ne,to kodai Aslam ya mutune, take gabanta yayi wani irin mummunar faɗuwa, take itama hawaye suka shiga wanke mata fuska hannun mami dake zaune kusa da ita ta damke da karfi Wanda saida mami ta juyo a firgice ta kalle ta, ganin hawaye a fuskarta yasa mami bule baki da sauri da nufin tambayar ta mekefaruwa saidai muryar ta ya katse ma mami hanzari, cikin sheshekar kuka tace"Mami ya mutu ko, Aslam ya mutu ya barni ko."Da sauri mami ta shiga girgiza mata kai kafin ta bule baki tace "A'a zainab karki sake faɗin wannan Kalmar Aslam bai mutu ba yana nan da ranshi da lafiyar shi." Zubawa mami idanu tayi tana kallon ta bawai dan ta yarda da abin da take gaya mata ba, ita yanzu idan ba ganin Aslam tayi ido da ido ba babu wanda zai ce mata yana raye ta amince.
Mummy ce ta fara shigowa falon domin amsa kiran gaggawar da Alhaji Baba ya mata, a ruɗe take matuƙa don tasan irin wannan kiran gaggawa daga Alhaji baba, ba karamin muhimmin Abu bane, tana shigowa idanun ta akan little dake rungume a jikin hajiya mama ya sauke, wani irin wawan burki ta taka, yayin da doguwar sallamar da ta rafko ya katse, bakin ta ne ya shiga rawa alamar tana son ta furta wani Abu amma kuma ta kasa buɗe baki, hajiya mama ne tace tana share hawayen farin ciki"kyayi abinda yafi haka ma Aisha karaso ciki." Mami ne ta Ƙarasa gare ta ta riƙo hannunta zuwa cikin falon ta zaunar da ita kusa da hajiya mama, mummy kam dama bata iya ruɗewa ba, lokacin da tayi arba da zee sai ta kura mata ido kamar tana son ta tuno inda tasan ta harga Allah ji tayi kamar an mata formatting lin komai daga kwakwalwar ta.
Daidai nan daddy ya shigo Amir na biye dashi ko zama basuyi ba Abba ma ya rafko sallama, duk da suma sun kaɗu da ganin zee tare da yaro mai kama da Aslam hakan baisa sun ruɗe ba kasancewar su mazaje masu dakkakkiyar zuciya.zama sukayi domin amsa kiran Alhaji baba, babu Wanda ya furta koda A ne daga cikin su, domin duk sanda Alhaji baba yayi irin wannan kiran kowa natsuwa yake yi ya saurare shi babu mai ikon yin magana har sai yaba da umarnin yin hakan, kamal ma ya karaso daga gurin aiki yake ma ya dauki excuse ya taso, Allah yasa ba sa wani Abu mai mahimmanci.
Aslam kawai ake zaman jira kasancewar an bashi umarnin ya taho harda Asmah, kuma yana office dole saiya biya gida ya dauko ta hakan yasa yayi jinkirin isowa, falo yayi tsit sai kallo kallo akeyi a tsananin juna, fuskar kowa cike da zaƙuwan sonjin ta yaya akayi matankaɗi ya shiga gora, domin dai dukkanin su kallo daya suka ma little suka tabbatar cewa lallai shiɗin jinin su ne, kamar yadda yaron ya kasance mai farin jini da saurin shiga rai tun haihuwar sa, farin jinin shi nanan har yau babu abinda ya dakushe a ciki saima ƙaruwa da yayi, domin dukkansu a kallo ɗaya yaron ya shiga ransu kaunar shi ya kama zuciyoyin su kowanne su burin shi ya ɗauki yaron saidai babu daman yin hakan saboda girmama wa ga Alhaji baba har sai ya gama fadar abin da yasa ya tarasu sannan zasu samu daman yin hakan.
Bayan kamar minti goma da haduwar kowa da kowa a falon Alhaji baba, motar Aslam ta faka a farfajiyar gidan, jiki a sanyaye ya buɗe motar ya fito, tunda ya tashi barci yau gaban shi keta faɗuwa lokaci zuwa lokaci har sai da takai ya gayawa Asmah, abin da ke damun shi, har yake cewa shi bai da tafiya bazai iya fita office ba, ita ta karfafa mai gwuiwa tare da cewa yayta ambaton innalillahi wainnailaihi rajiun, a haka ta samu ta lallaɓa shi ya tafi. Lokacin da kiran gaggawa daga Alhaji baba ya riskeshi ji yayi bugun da kirjinshi keyi ya nunku fiye dana da.
A bangaren Asmah kam ita ma kwarai da gaske jikin ta a sanyaye yake tunda maganar kiran nan ya risketa haka kawai take ji a jikin ta wani Abu Mara daɗi zai bakunci rayuwar ta.
Kasa fitowa daga motar tayi saida ya buɗe Mata tare da cewa "bismillah husnah muje Allah yana tare da mu koma meke ciki in-sha Allahu zaizo mana da sauƙi." Mika mata hannu yayi yana sakar mata murmushin karfafa gwuiwa, itama martanin murmushin ta mayar mai kafin ta mika hannun ta ta saka cikin nashi ya mayar ya damƙe gam kamar wani zai kwace mishi ita a haka suka doshi falon Alhaji baba hannun su cikin na juna............
Oum Ummeetarh
07041130088
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya,Allah kajiqan iyayen mu}
*ASSALAMUALAIKUM SISTERS*
abun d mamaki Tayanda watan axumi yaketa qaratowa cikin Dan taqin lokaci,
Me kika tanadarwa kanki dama yaranmu yar uwa?
Munada kyawawan kayan Yara na dinki masu kyau sosay d bama zakice dinkawa akayiba yaro/yarinya sufito gwanin burgewa kowa yanasan barka,07046881166
Kayanmu sauqinsu yyi har kamar kyautane,zaki iya samunsu dga 2k harzuwa abunda yyi Sama,kizo kiyi sarin kayanmu kisamu alkhairi me tarin yawa,07046881166
Akway takalma Suma kyawawa dgakan 1k zuwa sama,07046881166
Sannan munada tsala tsalan frames d madubai n gyaran gida masukyau d arha sosay,07046881166
Akway leshina d atamfofi,abayas sewanda kikazaba duk a farashi mesauki,07046881166
Karna cikaku d surutu ku kira:07046881166 domin qarin bayani,karku manta alkhairin Tari maganin mantuwa zaku iyashiga Instagram handle namu don ganin kayayyakinmu: everythng_handmade,
Semunjiku 07046881166
Page 124
A tare suka haɗa baki wurin yin sallama kafin su sa kai cikin falon hannun su sarƙe da juna. Tunda ta jiyo muryar shi yayi sallama , zuciyar ta ya shiga wani irin luguɗen bugu da karfin gaske. Ƙofar shigowa falon ta kafe da idanun ta tana kallon jiran tsammani. Shine ya fara bayyana a falon kafin ita, kamar had'in baki daga shi har ita idanun su, akan fuskar zee ya sauka,wani irin wawan burki ya taka daga bakin ƙofar, yana bin ta da wani irin kallo mai cike da tsantsar mamaki. A firgice ta mik'e tsaye tare da zaro dukkan girman idanun ta waje, furgici da tashin hankali ne suka bayyana ƙarara akan fuskar ta, kallon Asmah take yi kamar wacce keson ta tantance shin ita d'in ce kokuwa idanunta ne ke mata gizo, mayar da idanunta tayi kan hannayensu dake sarƙe dana juna, sannan ta ƙara sauke idanunta akan Aslam dake tsaye yana kallon ta kamar wata sabuwar halitta.
Gaba d'aya mutanen falon shiru sukayi suka zuba musu idanu, cikin su ukun an rasa Wanda zai fara janye idanun shi daga kan wani, kowanne da ma'anar kallon da yake bin ɗan uwan shi da shi. Zee tana bin Asmah da Aslam ne da kallon furgici da tsananin tashin hankali tare tambayar kanta shin meye alaƙar mijin ta da Asmah da har suka shigo cikin falon Alhaji baba a tare hannunsu sarƙe da juna, duk da tasan ita d'in burin shi ce zabin shi ce abar kaunar shi ce, tun kafin ta bar gidan shi, amma bata taɓa kawo tunanin cewa bayan bata zai mallake ta ba, saboda a gaban ta ranar Alhaji baba ya tsayar da lokacin bikin ta da kamal a wancen ranar, shin menene alakar su? Take zuciyar ta ta bata amsa da cewa Aure, ji tayi numfashin ta na neman gagarar ta ja, indai ko alaƙar aure ne a tsakanin mijin ta da Asmah ta shiga ukun ta, domin ita shaida ce akan irin tsananin so da kaunar da yake ma Asmah wanda tana da tabbacin ko rabin rabinshi baya mata.
Asmah kam kallo tsoro da zallar madarar kishi take bin zee da shi, shin meya dawo da ita rayuwar su a daidai wannan lokacin? me tazo nema me ya kawo ta? A daidai lokacin data shaku da Aslam ta zama shi ya zama ita ta miƙa mishi dukkan ragamar rayuwarta, lallai akwai gwarama, don a yadda take kaunar Aslam a halin yanzu bata jin zata iya raba shi da wata p
ƴa mace a duniya.