Sashe 74
Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wayar ta da yayi ringing ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi, sunan da ta gani na yawo a saman screen d'in wayar yasa bata san sanda ta saki kayataccen murmushi ba, cike da dauki ta daga wayar tare da cewa "Assalamu alaiki yake ummin mu" daga daya bangaren ummi tayi murmushi mai sauti sannan ta amsa mata da "wa'alaikissalam Asma'ul-husnah fatan kuma lafiya ya my son yake da fatan ana kula da shi sosai ko" murmushi tayi cike da jin kunyar maganar ummi tace "yana lafiya umminmu" ummi tace " masha allah yana gida ne ko ya fita don nata kiran wayar shi yanzu kafin na kira naki bai daga ba" Asmah tace "gsky bansan ko yana nan ba ko ya fita" ummi cikin zare ido tace "na shiga uku ni Aminatu, ban gane bakisan ko yana nan ko ya fita ba" Asmah cikin ko in kula tace "wlh umminmu ni rabona da shi tunda safe" ji tayi ummi ta rabka wani uban salati, kafin tace "Asma'u! kardai kice min zaman da kukeyi kanan ke da Aslam d'in wata da watan ni, Ashe baki da wayau ke shashasha ce ban Sani ba" tuni Asmah ta shiga zazzaro ido jin kalmomin dake fitowa daga bakin ummi, take ummi ta rufeta da fada ta inda take shiga bata nan take fita ba, hankalin Asmah bai kara tashi ba saida ta tsinci muryar ummi na cewa "nasani, nasan abinda yasa kika ki bama Aslam dama duk da irin tarin soyayyar daya yake miki, kamal ne ko? To wlh ki kama kanki dan kamalu tuni ya shafe babinki, yanzu haka zancen da nake miki Nana Khadijah ciki ne da ita har na wata biyu, ke kina nan kin tsaya wasa da daman ki " tuni hawaye ya gama wanke fuskar Asmah, cikin muryan kuka ta bude baki tace "ummi wlh b" cikin tsawa ummi ta katseta da cewa "wlh me? ni babu abida zaki gaya min a yanzu, ki Sani shi so da kike gani tamkar tsuntsune dake sauka akan bishiya domin yayi kiwo, idan ya sauka a bishiya ya rasa abin da zai kiwata dole zai fira daga wannan bishiyar ya koma wata, idan kuma ba'ayi a hankali ba bazai sake wai wayar wannan bishiyar ba kenan har abada, idan zaki kama kanki ki kama, Aslam yayi miki laifi mai girma a baya kuma ya gane kurensa, tunda kika ga Allah ya sake hada ku a karo na biyu shi kadai yasan abinda ya boye a tsakanin ku, kiyi hakuri ki rungumi kaddararki da hannu bibbiyu, bari na tuna miki wani abinda kika manta kinsan dai bake kadai bace mace a gurin Aslam ba ko? ina fatan kina tune da zainab" take gabanta yayi wani irin faduwa,jin abinda ummi ta fada tabdijam har ga Allah ta manta da wata zainab matar Aslam, wahayenta ne suka kara karfin gudu, take ta kara yunkurin yin magana dan ta kare kanta, ummi lura da ta yi jikinta ya gama yin sanyi yasa wannan karon ta bata daman cewa wani Abu, baki na rawa tace"wlh umminmu ba abinda kike tunani bane, wlh ummi a halin yanzu babu burbushin soyyayar ya kamal ko digo a zuciyata," take kuma ta shiga bama ummi labarin abinda ya faru yanzu yan mintocin da suka gabata, kasancewar basa iya boye ma ummi komai dake damunsu a rayuwar su.
Sauke ajiyar zuciya ummi tayi yanzu hankalin ta yadan kwanta jin hakan daga bakin Asmah, tasan komai zaizo sa sauki tunda babu kowa yanzu a zuciyarta, kwantar da murya ummi tayi cikin sigar lallashi ta fara cewa" alhmdllh naji dadin jin wannan maganar daga bakin ki Asmah, yanzu kuma lokacin yayi da zakiba Aslam dama domin ya mallaki wani fili daga zuciyar ki, Aslam yayi miki laifi kuma ya gane kurensa a halin yanzu ya kamata ki saurare shi, tunda kikaga haka Allah kadai yasan menene ya boye a tsakanin ku, kuma nasan keme bazakice a yanzu bakijin Aslam ko kadan bane a ranki, ko nayi karya?" Ummi ta tambaya, shiru Asmah tayi ta kasa bata amsa, dan kam idan har tace batajin shi a ranta yanzu tayi ma Allah karya, jin shiru yayi yawa yasa ummi tace "uhummm ke nake saurare fa" cikin sanyin murya tace "umminmu a halin yanzu wlh bana jin kin yaya Aslam a raina kuma kai tsaye bazan iya cewa ina sonsa ba,nasan dai ina jin matsanancin tausayin shi a raina, kuma nakan ji kewan shi idan baya kusa dani bayan wadanan, bazance ga wani Abu da nake ji game da shi ba Ummi" murmushi ummi tayi a daya bangaren a zuciyarta tace ahaf magana ya kare, a fili kuma tace "naji hakan ma wani ci gaba ne da sannu zaki soshi, amma fa sai kin saka ma ranki hakan, nidai yanzu abinda nake so dake, idan har bakyaso nayi mummunan fushi dake, na baki nan da sati guda naji kyakkyawan sauyi, a zaman takewarku, idan kuma ba haka ba wlh zanje na samu Alhaji baba, da mallam na gaya musu, sannan kuma na samu mummyn ku da daddy na gaya musu suma, kinsan dai wanene Aslam a gare su baza suji dadi ba idan sukaji abida kike masa" girgiza kai takeyi kamar a gaban ummi take, ummi nayin shiru ta shiga cewa a firgice "dan Allah ummi kiyi hakuri kar ki gaya musu Wlh zan sauya, insha Allah zan karbi kaddarata da hannu bibbiyu" wani wahalallan ajiyar zuciya Ummi ta sauke sannan tace "alhamdulillahi naji dadin hakan, kuma ina nan ina tsumayen jin daddadan labari, nifa so nake kafin shekara ta zagayo kowaccen ku ta ajiye min jika, inso samu ne ma yan bibbiyu ko uku uku nake so" dariya Asmah ta kwashe dashi, daga nan kuma ummi ta shiga janta da wasa kamar wasu kawaye , karshe kuma ta shiga koyar da ita dabaru kala kala wadan da zasu amfaneta sosai nan gaba , Asmah taji dadin hakan sosai, nan ta bude memory tana ta saving dinsu, suààaààà£
Aàqnfi awa biyu suna waya kafin sukayi sallama.
Komawa tayi da baya ta kwantap akan bed dinta tayi lamo maganganun da sukayi da ummi ya matukar shigar ta , jikinta gaba daya yayi sanyi kalau, musamman kan cewa da ummi tayi zata fadama su mummy abinda ke faruwa,koba komai mummy da daddy sune mutanen da take matukar so bayan iyayenta, kuma baza suji dadi ace taki abinda suka haifa ba, koba komai Aslam jininsu kuma jinin mutum mafi daraja a idanunta Alhaji baba...........
Oum ummeetarh
07041130088
Share
And
Comment
Fisabillilah🙏
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu}
Page 106
Haka suka ƙare wannan yinin cike da damuwa a zuciyar kowannen su, a bangaren Asmah Abu biyu ke damunta, maganganun da sukayi da ummi ɗazu, sai kuma, tunani da kewar Aslam daya addabi zuciya da ruhinta, gaba ɗaya jinta take kamar wata Mara lafiya, a haka har lokacin kwanciya barci yayi, koda ta kwanta kasa bacci tayi sai juyi kawai takeyi a makeken bed dinta, karshe ta janyo pillow ta rungume a kirjinta kamar yadda ta saba amma a banza, ji takeyi kamar ta tashi ta fita ta ganshi koda a boye ne,ba tare daya ganta ba,ba karamin dauriya tayi ba da ta hana kanta aikata hakan, daga karshe ta kwabi kanta da cewa, ya kamata ta kama ajinta koba komai ai shiya mata laifi shi ya kamata ya fara nemanta ba ita ya kamata ta fara neman shi ba.
A bangaren Aslam kam ya ma fita shiga damuwa, har karfe goman dare ya kai a falo yana zaman jiran tsamanin fitowarta, amma shiru gashi shi kuma ya kasa zuwa ya tunkareta, ganin goma da kwata yasa ya mike jiki ba kwari ya nufi dakin shi, wanka yayi tare da shirin bacci, kashe wuta yayi ya haye bed dinshi ya kwanta, saidai koda gigin wasa babu alamar bacci a idanun shi, gani yayi ma gadon ya mishi wani irin mugun fadi da girma, kai gaba daya ɗakin ma, ga wani irin sanyi da yakeji yana shigar shi duk da kuwa ƙudundunewa da yayi da katon bargo.
Idanun shi a bude kerr agogo ya buga 12am dai dai, kasa daurewa yayi ya mike ya kunna wutan dakin tare da zura slipas dinshi ya fice daga ɗakinshi ya doshi nata gaban shi Na faduwa, gara yaje ya tunkareta ayi wacce za'ayi komai ta fanjama fanjam, don ya tabbatar idan bai sanyata a idanunshi yau ba lallai bazai iya rintsawa ba.
Saida yayi tsayuwar kusan minti goma a bakin kofar yana tunanin anya kofar ma a bude take ko a kulle, a hankali yakai hannunshi kan handle din kofar ya murda tare da tura kofar a hankali, wani wawan ajiyar zuciya ya sauke jin kofar a bude.
Ware idanunta tayi daga lumshesun da tayi jin motsin ƙarar taba ƙofar dakinta, kafin tayi tunanin wani Abu ta ga ya tura kofar ya shigo dauke da munafukar sallama a bakin shi, ita ba a boye ba kuma baza'a kirata a fili ba ,wani irin mugun dadi ne ya ziyarceta, take ta sauke wani boyayyan ajiyar zuciya, a halin da zuciyarta ke ciki kiriss ya rage ta tashi ta bishi a cikin tsakiyar daren nan, saidai gashi Allah ya kawo mata shi, lamo tayi tana kare mai kallo ta cikin hasken kofar daya bari a buɗe.
Shikam Aslam bai ganta ba kasancewar dakin dimdim yake da duhu, kuma daga haske ya fito,idanunshi baya iya ganin komai sai duhu, jin bata amsa sallaman shi ba, hakan ya Tabbatar masa tayi bacci, wayar shi ya kunnu ya haska dakin ganin haka yasa tayi saurin rintse idanunta ba tare da ya ganta ba, lallabawa yayi a hankali ya kwanta a bayanta, duk abinda yakeyi tana jinsa, shiru sukayi daga ita har shi Na kusan 20 minutes, shi yana tunanin tayi bacci, ita kuma mamakin karfin halin shi na neman kashe ta, tayi shiru tana jiran taga mai yake shirin aikatawa.
A hankali ya dinga matsawa kaɗan kaɗan jikinta, har ya manna kirjin shi da bayanta, jin shiru bata motsaba yasa ya mike hannu a hankali ya rungumota jikin shi sosai, yana sauke ajiyar zuciya.
Sauke ajiyar zuciya ummi tayi yanzu hankalin ta yadan kwanta jin hakan daga bakin Asmah, tasan komai zaizo sa sauki tunda babu kowa yanzu a zuciyarta, kwantar da murya ummi tayi cikin sigar lallashi ta fara cewa" alhmdllh naji dadin jin wannan maganar daga bakin ki Asmah, yanzu kuma lokacin yayi da zakiba Aslam dama domin ya mallaki wani fili daga zuciyar ki, Aslam yayi miki laifi kuma ya gane kurensa a halin yanzu ya kamata ki saurare shi, tunda kikaga haka Allah kadai yasan menene ya boye a tsakanin ku, kuma nasan keme bazakice a yanzu bakijin Aslam ko kadan bane a ranki, ko nayi karya?" Ummi ta tambaya, shiru Asmah tayi ta kasa bata amsa, dan kam idan har tace batajin shi a ranta yanzu tayi ma Allah karya, jin shiru yayi yawa yasa ummi tace "uhummm ke nake saurare fa" cikin sanyin murya tace "umminmu a halin yanzu wlh bana jin kin yaya Aslam a raina kuma kai tsaye bazan iya cewa ina sonsa ba,nasan dai ina jin matsanancin tausayin shi a raina, kuma nakan ji kewan shi idan baya kusa dani bayan wadanan, bazance ga wani Abu da nake ji game da shi ba Ummi" murmushi ummi tayi a daya bangaren a zuciyarta tace ahaf magana ya kare, a fili kuma tace "naji hakan ma wani ci gaba ne da sannu zaki soshi, amma fa sai kin saka ma ranki hakan, nidai yanzu abinda nake so dake, idan har bakyaso nayi mummunan fushi dake, na baki nan da sati guda naji kyakkyawan sauyi, a zaman takewarku, idan kuma ba haka ba wlh zanje na samu Alhaji baba, da mallam na gaya musu, sannan kuma na samu mummyn ku da daddy na gaya musu suma, kinsan dai wanene Aslam a gare su baza suji dadi ba idan sukaji abida kike masa" girgiza kai takeyi kamar a gaban ummi take, ummi nayin shiru ta shiga cewa a firgice "dan Allah ummi kiyi hakuri kar ki gaya musu Wlh zan sauya, insha Allah zan karbi kaddarata da hannu bibbiyu" wani wahalallan ajiyar zuciya Ummi ta sauke sannan tace "alhamdulillahi naji dadin hakan, kuma ina nan ina tsumayen jin daddadan labari, nifa so nake kafin shekara ta zagayo kowaccen ku ta ajiye min jika, inso samu ne ma yan bibbiyu ko uku uku nake so" dariya Asmah ta kwashe dashi, daga nan kuma ummi ta shiga janta da wasa kamar wasu kawaye , karshe kuma ta shiga koyar da ita dabaru kala kala wadan da zasu amfaneta sosai nan gaba , Asmah taji dadin hakan sosai, nan ta bude memory tana ta saving dinsu, suààaààà£
Aàqnfi awa biyu suna waya kafin sukayi sallama.
Komawa tayi da baya ta kwantap akan bed dinta tayi lamo maganganun da sukayi da ummi ya matukar shigar ta , jikinta gaba daya yayi sanyi kalau, musamman kan cewa da ummi tayi zata fadama su mummy abinda ke faruwa,koba komai mummy da daddy sune mutanen da take matukar so bayan iyayenta, kuma baza suji dadi ace taki abinda suka haifa ba, koba komai Aslam jininsu kuma jinin mutum mafi daraja a idanunta Alhaji baba...........
Oum ummeetarh
07041130088
Share
And
Comment
Fisabillilah🙏
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu}
Page 106
Haka suka ƙare wannan yinin cike da damuwa a zuciyar kowannen su, a bangaren Asmah Abu biyu ke damunta, maganganun da sukayi da ummi ɗazu, sai kuma, tunani da kewar Aslam daya addabi zuciya da ruhinta, gaba ɗaya jinta take kamar wata Mara lafiya, a haka har lokacin kwanciya barci yayi, koda ta kwanta kasa bacci tayi sai juyi kawai takeyi a makeken bed dinta, karshe ta janyo pillow ta rungume a kirjinta kamar yadda ta saba amma a banza, ji takeyi kamar ta tashi ta fita ta ganshi koda a boye ne,ba tare daya ganta ba,ba karamin dauriya tayi ba da ta hana kanta aikata hakan, daga karshe ta kwabi kanta da cewa, ya kamata ta kama ajinta koba komai ai shiya mata laifi shi ya kamata ya fara nemanta ba ita ya kamata ta fara neman shi ba.
A bangaren Aslam kam ya ma fita shiga damuwa, har karfe goman dare ya kai a falo yana zaman jiran tsamanin fitowarta, amma shiru gashi shi kuma ya kasa zuwa ya tunkareta, ganin goma da kwata yasa ya mike jiki ba kwari ya nufi dakin shi, wanka yayi tare da shirin bacci, kashe wuta yayi ya haye bed dinshi ya kwanta, saidai koda gigin wasa babu alamar bacci a idanun shi, gani yayi ma gadon ya mishi wani irin mugun fadi da girma, kai gaba daya ɗakin ma, ga wani irin sanyi da yakeji yana shigar shi duk da kuwa ƙudundunewa da yayi da katon bargo.
Idanun shi a bude kerr agogo ya buga 12am dai dai, kasa daurewa yayi ya mike ya kunna wutan dakin tare da zura slipas dinshi ya fice daga ɗakinshi ya doshi nata gaban shi Na faduwa, gara yaje ya tunkareta ayi wacce za'ayi komai ta fanjama fanjam, don ya tabbatar idan bai sanyata a idanunshi yau ba lallai bazai iya rintsawa ba.
Saida yayi tsayuwar kusan minti goma a bakin kofar yana tunanin anya kofar ma a bude take ko a kulle, a hankali yakai hannunshi kan handle din kofar ya murda tare da tura kofar a hankali, wani wawan ajiyar zuciya ya sauke jin kofar a bude.
Ware idanunta tayi daga lumshesun da tayi jin motsin ƙarar taba ƙofar dakinta, kafin tayi tunanin wani Abu ta ga ya tura kofar ya shigo dauke da munafukar sallama a bakin shi, ita ba a boye ba kuma baza'a kirata a fili ba ,wani irin mugun dadi ne ya ziyarceta, take ta sauke wani boyayyan ajiyar zuciya, a halin da zuciyarta ke ciki kiriss ya rage ta tashi ta bishi a cikin tsakiyar daren nan, saidai gashi Allah ya kawo mata shi, lamo tayi tana kare mai kallo ta cikin hasken kofar daya bari a buɗe.
Shikam Aslam bai ganta ba kasancewar dakin dimdim yake da duhu, kuma daga haske ya fito,idanunshi baya iya ganin komai sai duhu, jin bata amsa sallaman shi ba, hakan ya Tabbatar masa tayi bacci, wayar shi ya kunnu ya haska dakin ganin haka yasa tayi saurin rintse idanunta ba tare da ya ganta ba, lallabawa yayi a hankali ya kwanta a bayanta, duk abinda yakeyi tana jinsa, shiru sukayi daga ita har shi Na kusan 20 minutes, shi yana tunanin tayi bacci, ita kuma mamakin karfin halin shi na neman kashe ta, tayi shiru tana jiran taga mai yake shirin aikatawa.
A hankali ya dinga matsawa kaɗan kaɗan jikinta, har ya manna kirjin shi da bayanta, jin shiru bata motsaba yasa ya mike hannu a hankali ya rungumota jikin shi sosai, yana sauke ajiyar zuciya.