Sashe 118
Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read
Oum Ummeetarh
07041130088
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya,Allah kajiqan iyayen}
Page 131
Mutuwar Dad ya girgiza zukatan mutane da dama, duk wanda ya tuna abin da ya faru kafin awa ashirin da hudu da suka shude, sai ya kara tsarkake lamarin ubangiji ya kuma kara tabbatar wa lallai rai ba'a bakin komai yake ba, lokacin da labarin rasuwar Dad ya riski zee kusan zaucewa tayi, take ta fisge daga rikon da Aslam ya mata ta nufi ɗakin da gawar Dad kwance da mahaukacin gudu, tana yin arba da gawar Dad take ta yanke jiki ta faɗi sumammiya. kwanan keso Dad yayi saboda da daddare ya cika. Washe gari Karfe tara Mom ta iso a birkice , bata yarda cewa Dad ya rasu ba saida tayi arba da shi kwance baya motsi lulluɓe da farin alawayyo, take ta ƙara birkicewa ta shiga zunduma ihu tana kururuwa da birgima kamar wata arniya maimakon ta mishi addu'a, rarrashin duniya an mata taƙi ta haƙura har aka gaji aka yi kyale ta, masu zagi da alawadai nayi masu tausayi nayi. Karfe goma daidai aka kai Dad makwancin shi na gaskiya, Aslam da duk wani makusancin shi sun halarci jana'izan Dad, tare dashi aka cigaba da karɓan gaisuwa a gidan alhaji Abdur-rahman. Har aka kai Dad aka watse zee bata cikin hayyacin ta, dan tunda ta sume aka kwashe ta aka sake bata gado a asibitin, likitoci suka duƙufa a kanta har aka samu ta farfaɗo, koda ta farfaɗo zabure zabure ta shiga yi tana ihu ce ihu ce lamarin kamar da bugun aljanu ganin haka yasa likita ya zunduma mata alluran barci mai karfin gaske, sai da Dad ya kwana ya wuni a kushewa sannan ta farko,cikin hukuncin ubangiji ta farka cikin hayyacinta sai dai kuma ruwan hawaye ya kasa ƙafewa a idanun ta, a ranar Dr ya bata sallama direct Aslam ya wuce da ita gidan Alhaji Abdur-rahman aka cigaba da zaman makoki tare da ita, duk yan gidan su Aslam sunje sunyi gaisuwa tun daga kan su mummy har su batool da mazajen su, Aslam da Asmah kam kullum nan suke wuni shi yana falon Alhaji Abdur-rahman ana karbar gaisuwa dashi ita kuma tana tare da zee tana kwantar mata da hankali, har zuwa ranar da akayi addu'an fidda'u na kwana uku. Sai da zee tayi kwana bakwai sannan Aslam ya dauko ta, har zuwa lokacin mutuwar Dad nanan daram a ranta, sai dai tayi amfani da shawarar da Asmah ke bata a kulkum ta daina yi mai kuka sai dai in abin ya ciyo ta tayi ta hawaye tana mai addu'a domin tasan shine abin da yafi buƙata a halin yanzu, part guda aka ware wa Mom a gidan Alhaji Abdur-rahman a nan take zaman takaban ta, Allah sarki Dad tasa ta ƙare wasu har sun manta dashi sai wa'inda ya zame wa dole kamar dai zee da Mom da Alhaji Abdur-rahman.
07041130088
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya,Allah kajiqan iyayen}
Page 131
Mutuwar Dad ya girgiza zukatan mutane da dama, duk wanda ya tuna abin da ya faru kafin awa ashirin da hudu da suka shude, sai ya kara tsarkake lamarin ubangiji ya kuma kara tabbatar wa lallai rai ba'a bakin komai yake ba, lokacin da labarin rasuwar Dad ya riski zee kusan zaucewa tayi, take ta fisge daga rikon da Aslam ya mata ta nufi ɗakin da gawar Dad kwance da mahaukacin gudu, tana yin arba da gawar Dad take ta yanke jiki ta faɗi sumammiya. kwanan keso Dad yayi saboda da daddare ya cika. Washe gari Karfe tara Mom ta iso a birkice , bata yarda cewa Dad ya rasu ba saida tayi arba da shi kwance baya motsi lulluɓe da farin alawayyo, take ta ƙara birkicewa ta shiga zunduma ihu tana kururuwa da birgima kamar wata arniya maimakon ta mishi addu'a, rarrashin duniya an mata taƙi ta haƙura har aka gaji aka yi kyale ta, masu zagi da alawadai nayi masu tausayi nayi. Karfe goma daidai aka kai Dad makwancin shi na gaskiya, Aslam da duk wani makusancin shi sun halarci jana'izan Dad, tare dashi aka cigaba da karɓan gaisuwa a gidan alhaji Abdur-rahman. Har aka kai Dad aka watse zee bata cikin hayyacin ta, dan tunda ta sume aka kwashe ta aka sake bata gado a asibitin, likitoci suka duƙufa a kanta har aka samu ta farfaɗo, koda ta farfaɗo zabure zabure ta shiga yi tana ihu ce ihu ce lamarin kamar da bugun aljanu ganin haka yasa likita ya zunduma mata alluran barci mai karfin gaske, sai da Dad ya kwana ya wuni a kushewa sannan ta farko,cikin hukuncin ubangiji ta farka cikin hayyacinta sai dai kuma ruwan hawaye ya kasa ƙafewa a idanun ta, a ranar Dr ya bata sallama direct Aslam ya wuce da ita gidan Alhaji Abdur-rahman aka cigaba da zaman makoki tare da ita, duk yan gidan su Aslam sunje sunyi gaisuwa tun daga kan su mummy har su batool da mazajen su, Aslam da Asmah kam kullum nan suke wuni shi yana falon Alhaji Abdur-rahman ana karbar gaisuwa dashi ita kuma tana tare da zee tana kwantar mata da hankali, har zuwa ranar da akayi addu'an fidda'u na kwana uku. Sai da zee tayi kwana bakwai sannan Aslam ya dauko ta, har zuwa lokacin mutuwar Dad nanan daram a ranta, sai dai tayi amfani da shawarar da Asmah ke bata a kulkum ta daina yi mai kuka sai dai in abin ya ciyo ta tayi ta hawaye tana mai addu'a domin tasan shine abin da yafi buƙata a halin yanzu, part guda aka ware wa Mom a gidan Alhaji Abdur-rahman a nan take zaman takaban ta, Allah sarki Dad tasa ta ƙare wasu har sun manta dashi sai wa'inda ya zame wa dole kamar dai zee da Mom da Alhaji Abdur-rahman.