Sashe 1
Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
Page 1&2
Bismillahirramanirrahim
Wasu k'wawawan motocine masu rai da lpy ke tafiya akan shimfidedden kwaltan dake unguwar London road dake garin minna,
Duk Wanda yasan unguwan London road. Yasan unguwace ta manyan mutane .musamman manyan yan kasuwa,
Kofar wani katafaren gida motocin nan sukayi parking gidane mai kyau. kuma ga dukkan alamu sabon gini ne ba a kai ga tarewa cikin saba,
Ahankali marafen motocin suka fara budewa. Mataye ne suka fara fitowa daga cikin motocin nan.
Yawancin matayen sanye suke da ankon wani hadadden atamfa yellow and brown colour. wasunsu kuma sanye da shiga ta alfarma,
Saida suka gama fitowa kaf d'insu na lura da wata mota guda daya daga cikin motocin nan wadda ba a bude ba balle a kai ga fitowa daga cikinta,
duka matayen nan tsayawa sukayi suna kallon motar nan. da alama jira sukeyi na cikin motar su fito ,
Marfin motar ne ya bude. A hankali wata dattijuwar mata da akalla zatakai shekara hamsin da haihuwa ta fito a motar cikin shiga ta alfarma. Sai kuma wata ta bude gaban motar ta fito ita muka sanye take da ankon dake jikinyawan cin matayen,
Hannu yar dattijuwar data fara fitowa a motar ta miqa ta kamo hannu waccce ta rage a cikin motar.wacce nake tsammanin duka matayen nan ita suke zaman jiran fitowarta ,
A hankali ta sako fararen qafafunta waje Wanda yasha wani irin design na black and red henna.
dai dai lokacin wasu daga cikin matayen nan suka saki bud'a ji kake "ayyiririririyyyyyy" wuri ya haustine da bud'a gwanin birgewa,
Sai alokaci na fahimci meke faruwa a wurin wato dai amaryace aka kawo sabon gidan nan
A hankali na qare ware idanuna akan amaryan sanye take da wani ubansun lace maroon colour mai duhu Wanda yayi masifar yima farar fatarta kyau an lilla'be mata kanta da wani babban mayafi peach colour kafarta da yasha design sanye da takalmi mai tsini shima peach dukda banga fuskar ta ba nasan wannan amaryar masha zatayi kyau ba qarya,
Matan nan biyu da suka fito mota daya da itane suka sanya ta a tsakiya suna nufar gidan sannan sauran matan suka rufa musu baya.
Dai dai get suka tsaya wannan dattijuwar matar tana karanta mata wani addua tana amsawa cikin sanyin muryarta daya shaqe tsabar kukan da tasha,
Da bismilllah ta sanya qafarta cikin gidan . wasu matane suka taso cike da fara,a suka tarbesu har cikin babban plat din dake farkon gidan
Masha Allah ginin bene ne babba Wanda ya gama tsaruwa kamar a Turai an qawatashi da kayan more Rayuwa na alfarma , saida suka sadata da bed room dinta dake upstair sannan suka firfito wasu suka zauna a falonta na sama wasu kuma suka sauqo kasa.. Nan aka gabatar musu da abincin tarbar amarya mai rai da lafiya kowa yaci abinda ranshi keso ya qoshi . nan dai wasu suka zazzaga gidan .. Gidan kam ya hadu sai sambarka
Amarya kam tunda suka sadata da bed room dinta suka zaunar da ita a gefen bed dinta kanta me duqe lilli'be da mayafinta . kuka takeyi sosai kamar ranta zai fits sai shesheqa takeyi kamar zata shiqe. Ita kadai tasan abinda me damun zuciyarta game da wannan qadddararren auren ..dasun San halin da take ciki game da wannan auren da dukkansu sun tayata kukan baqin ciki,
Dama ace zata iya bijirema Alhj baba akan wannan auren hadin daya hada data bijire mai,
Saidai kuma kash ko giyar wake tasha bazata taba iya bijire masa ba , saidai mijin da aka aura matan ya kasheta kamar yadda yay ikirarin cewa. tayarda ya kashetan akan ta zama butulu gurin bijirna umarnin alhj baba..
Tunaninta ne ya katse jin motsin mutane suna nufowa dakin da take domin yi mata sallama .
shigowa suka dingayi suna mata sallama da fatan alkhairi wasunsu na mata addua da tayata farin ciki yayinda wasu zuciyarsu kamar tayi bindiga ta fashe don tsananin baqin ciki .
Wani kukane ya
kufce mata ganin da gaske tafiya za suyi su barta a cikin wannan baqin gidan da ta tabbata shine ajalinta,
Rarrashinta suka shiga yi da bata baki yayi da masu Jin haushinta musamman yan matan dake son auren mijin nata dakuma wadanda kema yayansu ko kannensu kwadayin auren wtakeyiba
ya'kyawan santalelen matashin saurayin mai ji da kudi ga kyau ga 'kuruciya, ke mata kallon wawiya wacce batasan abinda takeyiba
Shere and comment
Fisabilillah🙏🏻
💖DAMA TA BIYU💖
BY
{AYSHA NALADO}
FREE BOOK
Page 3 & 4
Wata mataCikin yan kawo amarya ta karasa kusa da amaryan ta tsuguna a gabanta ta mi'ka hannuta ta daura akan cinyoyinta a hankali cikin kwantar da murya tace
"haba ASMA'U kukan ya isa haka mana tun jiya kike abu daya sai kace wacce aka kashewa iyaye ya kamata kibar kukan nan haka kodan lafiyarki"
Wata kyakkyawan tsohuwa ta karbe zancen da cewa " ke da allah ya dubi maraicinki ya baki miji na bugawa a jarida. mijin da duk wacce ta sameshi ta gama more miji. kinsan yan mata nawa ne ke neman wannan damar amma allah bai basu ba ke ya baki, ba kuka ya kamata kiyi ba godema Allah ya kamata kiyi daya mallaka miki Muhammad aslam a matsayin mijin auren ki.
Koda yake bazan ma ce kiyi shiru ba. yi tayi kinga idan ASLAM ya zo ya sameki da ido jajur dole ya lallabo ya dawo wurina tinda dama nice uwargida ran gida nice ta karfen "
ta qarashe maganar cikin d'an zaulaya.
Matar datayi magana dazu ne ta sake cewa tana kallon mutane dakin"jama a ya kamata muyi haramar tafiya magariba Na gabatowa motocin da suka kawomu suna waje suna jiran mu Allah ya basu zaman lapiya" da amin wasu suka amsa a fili wasu a zuciya yayinda wasu ke fadin ba amin ba a zuciyarsu.
Wucewa duka yan kawo amaryan sukayi aka barta daga ita sai kawayenta kuma yan uwanta amira , zahra , da batool sai kuma kanwarta Khadijah.
*********************
Misalin karfe shidda da Rabi Na yammacin ranar asabar zaune yake a bakin gadon dakin hotel da ya kama yau kimanin kwana uku kenan.
sanye yake da singlet fari qal da wando 3quater, matashin sauryine Wanda a kalla zaikai shekara 30 da haihuwa.
Kallo daya zaka masa kasan dolenema yan mata su haukace akan shi domin ya gama haduwa ta ko ina. fatar jikinshi kawai idan ka kalla kasan Hutu da jin dadin sun gama zama a jikin shi komai Na jikin shi me kyau ne tun daga sumar kanshi mai dauke da baqin saisayayyen gashi mai taushin gaske, fusskarshi mai dauke da kyakkyawan bakin saje a zagaye dashi. ga kuma wani Dan madaidaicin gemu daya tsayar irin na samari yan kwalisa masu ji da gayu, zuwa yanayin tsarin halilltar jikinsa irin Na cikakkun maza masu kyawun sura, Muhammad aslam kenan ,aslam mutum ne Mara, son hayaniya shiyasa da wuya ka ganshi yana magana indai ba mai mahimmanci bane, akoda yaushe fuskarshi a kame take,
bai cika kyalkyata dariyaba saidai yayi murmushi .shima ba kowani lokaciba hakan yasa yan matan dake Neman kawo mishi wargi suke matugar shakkarsa. Yanada riqo da addini baya wasa da ibadah yana matuqar girmama iyayen shi hakan kuma ya samo asaline ganin yadda iyayen nashi ke girmama nasu iyayen suma, Abu daya ke bani mamaki ga rayuwarshi shine rashin son raini kwata kwata aslam baya son raini duk abinda zaiyi a rainashi ko cikin
abokaine bayaso balle kuma a gurin qannen shi, hakan yasa qannwnshi ke kwasan gwale-gwale a hannunshi baya wasa dash ko kadan tsakanin shi dasu girmamawane
Shere
And
Comment
Fisabillillah🙏🏻💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Na sadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu}
Page 5
Wayarsace dake gefensa ta fara ringing ko bai kalla ba yasan bazai wuce amir ba, miqa hannu yayi ya dauki wayar ya duba, kamar yadda yayi tsammani kuwa amir d'inne,
Kamar ko wani lokaci mayar da wayar yayi ya ajiye baiyi receiving ba, jota da biron da ke ajiye gefensa ya dauka,
sai da ya tsaya yayi Dan Jim kafin daga bisani yayi rubutun da bai wuce layi uku ba ya falle page din ya linke ya ajiye ,
Kallon agogo dake manne a dakin hotel din yayi ganin 6:40pm yasa ya mike ya shiga toilet domin ya dauro alwala,
Yana fitowa jallabiya ya dauka ya daura akan 'kananan kayan dake jikinsa. Paper da yayi rubutu da key ya dauka ya saka a aljihu ya fito d'akin d'auke da wayoyin shi a hannu ,
Kulle kofar dakin yayi ya fito a cikin hotel din ya nufi masallacin kusa da hotel din,
Daf da zai shiga masallacin wayarshi ta fara qarar alamar saqo ya shigo, Dan dakatawa yayi ya duba message din ganin saqon da aka turo ya saka shi dialing number da aka turo message din, picking akayi cike da girmamawa Wanda ya kira din ke fading
"yallabai gani nan Na karaso hotel din "
A daqile yace
"kasame ni a masallaci"
Ya kashe wayar ya shige cikin masallacin, saida aka idar da sallan magriba suka samu ganin juna, bayan sun gaisa hannu yasa a aljihu ya Ciro paper dayayi Dan note dazu ya miqa mishi tare da fadin. "ka kai ma waccen yarinyar"
Amsa yayi da hannu biyu amma ga dukkan alamu bai game wacce yarinya yake nufi ba , Dan sada kansa qasa kadan yayi alamar girmamawa sannan yace "yallabai wacce yarinya kake nufi"
Kallon shi aslam yayi ya dauke kai yace" yarinyar da suka kai gida Na dazu"
Murmushi ne ya kufce a fuskar bello yana Dan Sosa qeya yace
"yallabai amarya kake nufi"
Wani mugun kallo ya watsawa bello dayasa lokaci daya murmushin fuskarshi gimtsewa, Juyawa yayi zai wuce aiken da aka mai yana cewa "a huta lpy yallabai"
Saida yayi taku kamar biyar aslam ya kira sunan sa "bello" juyowa bello yayi ya dawo yadan risina yace "yallabai gani". Saida ya bushi iska yace "kada kowa yasan ina nan ciki harda daddy da amir, babu wani mahalukin dayasan inda nake sai kai kad'ai don haka take care" yana gama fadin haka ya duya ya shige cikin hotel din abinshi..
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
Page 1&2
Bismillahirramanirrahim
Wasu k'wawawan motocine masu rai da lpy ke tafiya akan shimfidedden kwaltan dake unguwar London road dake garin minna,
Duk Wanda yasan unguwan London road. Yasan unguwace ta manyan mutane .musamman manyan yan kasuwa,
Kofar wani katafaren gida motocin nan sukayi parking gidane mai kyau. kuma ga dukkan alamu sabon gini ne ba a kai ga tarewa cikin saba,
Ahankali marafen motocin suka fara budewa. Mataye ne suka fara fitowa daga cikin motocin nan.
Yawancin matayen sanye suke da ankon wani hadadden atamfa yellow and brown colour. wasunsu kuma sanye da shiga ta alfarma,
Saida suka gama fitowa kaf d'insu na lura da wata mota guda daya daga cikin motocin nan wadda ba a bude ba balle a kai ga fitowa daga cikinta,
duka matayen nan tsayawa sukayi suna kallon motar nan. da alama jira sukeyi na cikin motar su fito ,
Marfin motar ne ya bude. A hankali wata dattijuwar mata da akalla zatakai shekara hamsin da haihuwa ta fito a motar cikin shiga ta alfarma. Sai kuma wata ta bude gaban motar ta fito ita muka sanye take da ankon dake jikinyawan cin matayen,
Hannu yar dattijuwar data fara fitowa a motar ta miqa ta kamo hannu waccce ta rage a cikin motar.wacce nake tsammanin duka matayen nan ita suke zaman jiran fitowarta ,
A hankali ta sako fararen qafafunta waje Wanda yasha wani irin design na black and red henna.
dai dai lokacin wasu daga cikin matayen nan suka saki bud'a ji kake "ayyiririririyyyyyy" wuri ya haustine da bud'a gwanin birgewa,
Sai alokaci na fahimci meke faruwa a wurin wato dai amaryace aka kawo sabon gidan nan
A hankali na qare ware idanuna akan amaryan sanye take da wani ubansun lace maroon colour mai duhu Wanda yayi masifar yima farar fatarta kyau an lilla'be mata kanta da wani babban mayafi peach colour kafarta da yasha design sanye da takalmi mai tsini shima peach dukda banga fuskar ta ba nasan wannan amaryar masha zatayi kyau ba qarya,
Matan nan biyu da suka fito mota daya da itane suka sanya ta a tsakiya suna nufar gidan sannan sauran matan suka rufa musu baya.
Dai dai get suka tsaya wannan dattijuwar matar tana karanta mata wani addua tana amsawa cikin sanyin muryarta daya shaqe tsabar kukan da tasha,
Da bismilllah ta sanya qafarta cikin gidan . wasu matane suka taso cike da fara,a suka tarbesu har cikin babban plat din dake farkon gidan
Masha Allah ginin bene ne babba Wanda ya gama tsaruwa kamar a Turai an qawatashi da kayan more Rayuwa na alfarma , saida suka sadata da bed room dinta dake upstair sannan suka firfito wasu suka zauna a falonta na sama wasu kuma suka sauqo kasa.. Nan aka gabatar musu da abincin tarbar amarya mai rai da lafiya kowa yaci abinda ranshi keso ya qoshi . nan dai wasu suka zazzaga gidan .. Gidan kam ya hadu sai sambarka
Amarya kam tunda suka sadata da bed room dinta suka zaunar da ita a gefen bed dinta kanta me duqe lilli'be da mayafinta . kuka takeyi sosai kamar ranta zai fits sai shesheqa takeyi kamar zata shiqe. Ita kadai tasan abinda me damun zuciyarta game da wannan qadddararren auren ..dasun San halin da take ciki game da wannan auren da dukkansu sun tayata kukan baqin ciki,
Dama ace zata iya bijirema Alhj baba akan wannan auren hadin daya hada data bijire mai,
Saidai kuma kash ko giyar wake tasha bazata taba iya bijire masa ba , saidai mijin da aka aura matan ya kasheta kamar yadda yay ikirarin cewa. tayarda ya kashetan akan ta zama butulu gurin bijirna umarnin alhj baba..
Tunaninta ne ya katse jin motsin mutane suna nufowa dakin da take domin yi mata sallama .
shigowa suka dingayi suna mata sallama da fatan alkhairi wasunsu na mata addua da tayata farin ciki yayinda wasu zuciyarsu kamar tayi bindiga ta fashe don tsananin baqin ciki .
Wani kukane ya
kufce mata ganin da gaske tafiya za suyi su barta a cikin wannan baqin gidan da ta tabbata shine ajalinta,
Rarrashinta suka shiga yi da bata baki yayi da masu Jin haushinta musamman yan matan dake son auren mijin nata dakuma wadanda kema yayansu ko kannensu kwadayin auren wtakeyiba
ya'kyawan santalelen matashin saurayin mai ji da kudi ga kyau ga 'kuruciya, ke mata kallon wawiya wacce batasan abinda takeyiba
Shere and comment
Fisabilillah🙏🏻
💖DAMA TA BIYU💖
BY
{AYSHA NALADO}
FREE BOOK
Page 3 & 4
Wata mataCikin yan kawo amarya ta karasa kusa da amaryan ta tsuguna a gabanta ta mi'ka hannuta ta daura akan cinyoyinta a hankali cikin kwantar da murya tace
"haba ASMA'U kukan ya isa haka mana tun jiya kike abu daya sai kace wacce aka kashewa iyaye ya kamata kibar kukan nan haka kodan lafiyarki"
Wata kyakkyawan tsohuwa ta karbe zancen da cewa " ke da allah ya dubi maraicinki ya baki miji na bugawa a jarida. mijin da duk wacce ta sameshi ta gama more miji. kinsan yan mata nawa ne ke neman wannan damar amma allah bai basu ba ke ya baki, ba kuka ya kamata kiyi ba godema Allah ya kamata kiyi daya mallaka miki Muhammad aslam a matsayin mijin auren ki.
Koda yake bazan ma ce kiyi shiru ba. yi tayi kinga idan ASLAM ya zo ya sameki da ido jajur dole ya lallabo ya dawo wurina tinda dama nice uwargida ran gida nice ta karfen "
ta qarashe maganar cikin d'an zaulaya.
Matar datayi magana dazu ne ta sake cewa tana kallon mutane dakin"jama a ya kamata muyi haramar tafiya magariba Na gabatowa motocin da suka kawomu suna waje suna jiran mu Allah ya basu zaman lapiya" da amin wasu suka amsa a fili wasu a zuciya yayinda wasu ke fadin ba amin ba a zuciyarsu.
Wucewa duka yan kawo amaryan sukayi aka barta daga ita sai kawayenta kuma yan uwanta amira , zahra , da batool sai kuma kanwarta Khadijah.
*********************
Misalin karfe shidda da Rabi Na yammacin ranar asabar zaune yake a bakin gadon dakin hotel da ya kama yau kimanin kwana uku kenan.
sanye yake da singlet fari qal da wando 3quater, matashin sauryine Wanda a kalla zaikai shekara 30 da haihuwa.
Kallo daya zaka masa kasan dolenema yan mata su haukace akan shi domin ya gama haduwa ta ko ina. fatar jikinshi kawai idan ka kalla kasan Hutu da jin dadin sun gama zama a jikin shi komai Na jikin shi me kyau ne tun daga sumar kanshi mai dauke da baqin saisayayyen gashi mai taushin gaske, fusskarshi mai dauke da kyakkyawan bakin saje a zagaye dashi. ga kuma wani Dan madaidaicin gemu daya tsayar irin na samari yan kwalisa masu ji da gayu, zuwa yanayin tsarin halilltar jikinsa irin Na cikakkun maza masu kyawun sura, Muhammad aslam kenan ,aslam mutum ne Mara, son hayaniya shiyasa da wuya ka ganshi yana magana indai ba mai mahimmanci bane, akoda yaushe fuskarshi a kame take,
bai cika kyalkyata dariyaba saidai yayi murmushi .shima ba kowani lokaciba hakan yasa yan matan dake Neman kawo mishi wargi suke matugar shakkarsa. Yanada riqo da addini baya wasa da ibadah yana matuqar girmama iyayen shi hakan kuma ya samo asaline ganin yadda iyayen nashi ke girmama nasu iyayen suma, Abu daya ke bani mamaki ga rayuwarshi shine rashin son raini kwata kwata aslam baya son raini duk abinda zaiyi a rainashi ko cikin
abokaine bayaso balle kuma a gurin qannen shi, hakan yasa qannwnshi ke kwasan gwale-gwale a hannunshi baya wasa dash ko kadan tsakanin shi dasu girmamawane
Shere
And
Comment
Fisabillillah🙏🏻💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Na sadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu}
Page 5
Wayarsace dake gefensa ta fara ringing ko bai kalla ba yasan bazai wuce amir ba, miqa hannu yayi ya dauki wayar ya duba, kamar yadda yayi tsammani kuwa amir d'inne,
Kamar ko wani lokaci mayar da wayar yayi ya ajiye baiyi receiving ba, jota da biron da ke ajiye gefensa ya dauka,
sai da ya tsaya yayi Dan Jim kafin daga bisani yayi rubutun da bai wuce layi uku ba ya falle page din ya linke ya ajiye ,
Kallon agogo dake manne a dakin hotel din yayi ganin 6:40pm yasa ya mike ya shiga toilet domin ya dauro alwala,
Yana fitowa jallabiya ya dauka ya daura akan 'kananan kayan dake jikinsa. Paper da yayi rubutu da key ya dauka ya saka a aljihu ya fito d'akin d'auke da wayoyin shi a hannu ,
Kulle kofar dakin yayi ya fito a cikin hotel din ya nufi masallacin kusa da hotel din,
Daf da zai shiga masallacin wayarshi ta fara qarar alamar saqo ya shigo, Dan dakatawa yayi ya duba message din ganin saqon da aka turo ya saka shi dialing number da aka turo message din, picking akayi cike da girmamawa Wanda ya kira din ke fading
"yallabai gani nan Na karaso hotel din "
A daqile yace
"kasame ni a masallaci"
Ya kashe wayar ya shige cikin masallacin, saida aka idar da sallan magriba suka samu ganin juna, bayan sun gaisa hannu yasa a aljihu ya Ciro paper dayayi Dan note dazu ya miqa mishi tare da fadin. "ka kai ma waccen yarinyar"
Amsa yayi da hannu biyu amma ga dukkan alamu bai game wacce yarinya yake nufi ba , Dan sada kansa qasa kadan yayi alamar girmamawa sannan yace "yallabai wacce yarinya kake nufi"
Kallon shi aslam yayi ya dauke kai yace" yarinyar da suka kai gida Na dazu"
Murmushi ne ya kufce a fuskar bello yana Dan Sosa qeya yace
"yallabai amarya kake nufi"
Wani mugun kallo ya watsawa bello dayasa lokaci daya murmushin fuskarshi gimtsewa, Juyawa yayi zai wuce aiken da aka mai yana cewa "a huta lpy yallabai"
Saida yayi taku kamar biyar aslam ya kira sunan sa "bello" juyowa bello yayi ya dawo yadan risina yace "yallabai gani". Saida ya bushi iska yace "kada kowa yasan ina nan ciki harda daddy da amir, babu wani mahalukin dayasan inda nake sai kai kad'ai don haka take care" yana gama fadin haka ya duya ya shige cikin hotel din abinshi..