← Book details Zaujatu Jinnul Ashiq Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 86 OF 110

Sashe 86

Zaujatu Jinnul Ashiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Sannu a hankali haka rayuwa ta ci gaba da tafiya Raihan na zaman haƙuri da kai zuciya nesa, kusan kullin sai sun yi waya da Mommy amma bata taɓa gaya mata halin da take ciki ba saboda ta fahimci abin da mommy take guje mata, kuma gani take da kunya ta faɗi irin zaman da take yi. Tsakaninta da Al'amin daga gaisuwa sai saka aiki bayan wannan babu wata hira da take shiga tsakaninsu, tana ji tana gani suke shan soyayya tsakaninsa da Sumayya har sai da ta ji ina ma ita ce yake riritawa haka. Idan ta ga abin zai ɓata mata rai sai dai ta koma ɗakinta ta ɗauki waya ta shiga Whatsappa, mostly ta fi sha'awar karanta littafan Ameera Adam don ba ƙaramin birgeta suke yi ba musamman na barkwanci don ko ranta a ɓace yake sai zuciyarta ta yi wasai, wani lokacin idan tana karantawa tana dariya har falo Sumayya take jiyo dariyarta, wannan lamarin ba ƙaramin tunzura zuciyarta yake yi ba. Hakan ne ya sa wataran ta tura ƙofar ɗakin Raihan ta gaggasa mata magana, uffan Raihan bata gaya mata ba sai ma ta ci gaba da dariyarta don ta zo wurin da Ɗan tsoho mai buhu ya zuba ihu haɗe da wurgar da buhun hanunsa ya nausa daji, a daidai lokacin da ya ji passingers ɗin motarsu za su kamo shi da ƙarfi su mayar da shi motar da ta gama yin hayaƙi. (LITTAFIN YAWON SALLAR HAJIYA IYA.) Haushi ne ya kama Sumayya ta fice daga ɗakin, Al'amin kuwa na dawowa ta shirya masa ƙarya da gaskiya ta gaya masa nan take ya rufe Raihan da faɗa ba tare da ya bi ba'asi ba. A hana ya ƙare kwanakinsa bakwai cif na ɗakin Sumayya a ranar da zai koma ɗakin Raihan Sumayya har da kukanta, har sai da ta saka shi a gaba ya yi mata alƙawari akan babu wani abu da zai shiga tsakaninsa da Raihan. Alƙawari ya ɗaukar mata don shi kansa gani yake babu wani abu da zai nema a wurin Raihan bayan wanda ya samu a wurin Sumayyansa. Tun bayan magriba Raihan take zuba idon ganin Al'amin amma har bayan tara na dare ba ta ji motsinsa ba, akan dole ta haƙura ta yi kwanciyarta. Cikin bacci ta ji shigowarsa amma sai ta yi kamar bata ji shi ba, a gefenta ta ji ya kwanta ya juya bayansa nan take ƙirjinta ya buga ta sake naɗe wa wuri ɗaya. Da shigarsa ko minti goma bai yi ba suka ji bugun ƙofar Sumayya tana bugu tana kuka wai tsoro take ji ta ga gilmawar wani abu ba za ta iya kwana ita kaɗai ba, a zabure Al'amin ya miƙe ya nufi ɗakin nata. Ya duba ko'ina amma babu wani abu da ya gani, don haka ya zauna yana gadin sumyya da niyyar idan ta yi bacci sai ya koma ɗakin Raihan don ya fita haƙƙinta saboda ko da baya santa ya san tana da haƙƙi akansa, ada bai yi niyyar haɗa komai da ita amma da ya tuna Ubangiji da haƙƙoƙinta sai yake ƙoƙarin saukewa. Haka Summaya ta riƙa yi yau ta tsiro wannan gobe ta tsiro wannan har kwana ta taɓa yi a ɗakin Raihan don kar ta bari wani abu ya shiga tsakaninsu. Saboda a yanda ta san Al'amin zai yi wuya ya shafe kwanaki bakwai ba tare da wani abu ya shiga tsakaninsu ba, saboda mutum ne mai taƙatsantsan da rashin son shiga haƙƙin na ƙasa da shi. A haka har su Raihan suka shafe wata guda ba tare da ya wani abu ya shiga tsakaninsu ba, ana cikin haka Sumayya ta fara wani irin laulayi mai saka bacci don a daddafe take iya yin sallar Isha'i. A ranar wata juma'a Al'amin ya yi niyyar sauke nauyin Raihan da ke kansa, siyayya ya yi musu kamar yadda ya saba duk dare kowacce ya miƙa mata. Ganin yanayinsa ba ƙaramin faranta mata rai ya yi ba, alwala ya sata ta ɗauro bayan sun gama cin abinci don yanzu idan yana ɗakinta har yana yadda ta zuba masa abinci ya ci a ɗakin, bayan sun gabatar da sallar Nafila Al'amin ya jima yana yi musu addu'o'i sannan ya shafa. Jikin Raihan ba ƙaramin sanyi ya yi ba gabanta na faɗuwa, hannunta ya kama suka wuce kan gado sannu a hankali ya fara sarrafata cikin ƙarfin hali don ko kaɗan babu ɗigon soyayyar Raihan a zuciyarsa. Sai dai yanayin surarta ba ƙaramin hargitsa tunaninsa ta yi ba har ya gagara bambamce Sumayya da Raihan wacce ta fi wata. Hannunsa ya saka yana yawo da shi cikin jikinta, jikin Raihan ban da rawa babu abin da yake yi ana cikin haka ta ji Al'amin na ƙoƙarin...

Allah ya sani ina taya Kabiru kishi ba zan ƙarasawa ba sai Allah ya kaimu😰

Littafin kuɗi ne 300 idan kina buƙata ki min mgn +234 706 206 2624.

45
Chapter 86 · 0% Book details