Sashe 43
Zaujatu Jinnul Ashiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Kafin Mommy ta dawo tuni Raihan ta dawo hayyacinta, sai Mama Uwani ce take sanarwa da Mommy abin da ya faru. Ba ƙaramin tausayi su Inno suka bata ba, tun daga ranar idan za ta fita unguwa ta daina barinta da su a cikin gida dukda dai akwai Mama Uwani. Haka rayuwa ta ci gaba da tafiya yau ciwon Rihan ya tashi anjima ya lafa, har ta fara girma ta fara nisa a makaranta. Tana gama firamare sai kuma ciwonta ya fara yin sanyi wani lokacin sai ta shafe wata shida wani abu bai faru da ita ba, sai kuma ya zamana idan ciwon nata zai zo ma sai dai ta yanke jiki ta faɗi kamar mai farfaɗiya sai ta kusa wuni guda bata farko ba. Ita ba mai bacci ba ita ba ido biyu ba. Tun da mommy ta duba yanayin ciwon Raihan babu yadda bata yi a nemar mata magani ba amma abin ya ci tura, daga ƙarshe ma ɗaukanta ya yi da Mommy suka sakamakon harkar ƙaro da ya fara yin safararsa daga nan gida najeriya. Ba ƙaramin samu yake yi ba don haka ya ce zamansu a can yafi don a can ne za a newa wa Raihan lafiya yadda ya kamata. Ko kaɗan Mommy bata so ba amma babu yadda ta iya haka suka tafi suka bar su Inno da Mama Uwani a gidan, lokaci bayan lokaci Daddy na turowa ɗaya daga cikin yaran kawunsa kuɗi yana yi wa su Inno duk siyayyar da ta dace.
Daddy da iyalansa ba su suka dawo Nigeria ba sai da Raihan ta gama secondry school a lokacin tana da shekara goma sha shida, sai dai an samu sauki sosai don ciwon nata yana jimawa har fin shekara bai tashi ba, musamman da su Mommy suke kiyaye abubuwan da yake tayar mata da ciwon, amma sukan zo gida lokaci zuwa lokaci a lokacin ƙanwar Mommy wurin haihuwarta biyar. Duk wannan tsahon shekarun da aka ɗauka Mama Uwani tana tare da su Inno suna zaune gwanin birgewa, dawowarsu Nijeriya samari da dama ƴaƴan abokan Daddy sun nuna soyayayrsu ga Raihan, sai dai gabaɗaya babu wanda ta taɓa aminta da shi. Hasalima daga ranar da ka ce kana sonta shi kenan ta yanke duk wata alaƙa da kai, ko kaɗan abin bai damu Daddy ba da yake dama bai yi niyyar aurar da ita a lokacin ba. Ya ci burin sai ta yi karatu mai zurfi ta karanci harkar lafiya, amma ita Raihan sam karatun likitanci ba shi ne a gabanta ba tafi sha'awar lecturing. Mommy tun tana ɗaukan abin wasa da shirmen ƙuruciya har abin ya fara damunta a zuciya, don har Raihan ta kai shekara goma sha takwas babu wanda ya taɓa fitowa ya ce yana sonta ta amshi tayinsa. Hasalima daga ƙarshe samarin ma daina zuwa suka yi, idan mommy ta yi wa Daddy magana sai dai ya rufe ta da faɗa ya ce Raihan nawa take da don bata yi saurayi ba har za a damu. Daga ƙarshe Mommy daina bin ta kansa ta yi, ita ma Raihan ɗin idan mommy ta yi mata magana sai dai ta ce mata ita fa tana da mijin aure. Kusan kullin sai Mommy ta yi nafilar dare ta kaiwa Allah kukanta akan ya bayyana musu abin da yake daminta dan kuma jinkirin aure ne ya sa jinkirin ya zama alƙairi.
MU DAWO LABARI.
Jin Huzaifa ya datse maganar da ya fara yi ya sa Malam Usman ya ce, "Idan baka da abin faɗa Huzaifa kar ka ɓata min lokaci." Huzaifa ya sake numfasawa sannan ya ce, "Wata rana ina shawagi a sararin samaniya ranar ina cikin farinciki, kawai ta raya min na bi gidajen Bil'adam ko na kashe ƙwarƙwatar idona, a wani gida na ci karo da Raihan a lokacin bata fi shekara huɗu a duniya ba. Cikin dare ne don dare ya tsala sosai, tana kwance a ɗakinta wanda ya ƙayatu fa ƴar tsanoni kala-kala, daga gefen gadonta Mahaifinta ne a zaune yana ɗan danne-danne a laptop. Sai wayarsa da take fitar da sautin sasaanyar waƙa turawa, har na yi hiyyar giftawa na hangi surara yarinyar gwanin birgewa kanta ba ɗankwali gashi tana rungume da wani teddy. Shafata na yi nan take naji wani sabon yanayi da ban taɓa ji a jikina ba, dukda na yi mu'amala da matan bil'adam babu adadi amma yanayin da na ji game da ita na musamman ne. Ina cikin wannan yanayin Mahaifiyarta ta shigo ɗakin tana yi wa mahaifinta magana, "Haba Daddyn Raihan. Dare fa mahutar bawa ne ka rinƙa hutawa ranka mana, ga shi ka kunna waƙa biyu saura fa. Ni ma daga yin shafa'i da wuturi shikenan bacci ya yi gaba da ni, yarinyar nan ban san lokacin da ka kwnatar da ita ba." Ina kallo mahaifinta ya miƙe yace, "Ai na gama mu wuce kawai." Mahaifiyarta ce ta ƙaraso wurin da nake rungume da Raihan ta fara yi mata addu'a ba shiri na tashi daga wurin daga ƙarshe ma karatun kur'ani ta kunna mata a waya akan dole na haƙura da gidan gabaɗaya."
Wash🤠yau na sha typin.
Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ki min mgna 0706 206 2624
23
Daddy da iyalansa ba su suka dawo Nigeria ba sai da Raihan ta gama secondry school a lokacin tana da shekara goma sha shida, sai dai an samu sauki sosai don ciwon nata yana jimawa har fin shekara bai tashi ba, musamman da su Mommy suke kiyaye abubuwan da yake tayar mata da ciwon, amma sukan zo gida lokaci zuwa lokaci a lokacin ƙanwar Mommy wurin haihuwarta biyar. Duk wannan tsahon shekarun da aka ɗauka Mama Uwani tana tare da su Inno suna zaune gwanin birgewa, dawowarsu Nijeriya samari da dama ƴaƴan abokan Daddy sun nuna soyayayrsu ga Raihan, sai dai gabaɗaya babu wanda ta taɓa aminta da shi. Hasalima daga ranar da ka ce kana sonta shi kenan ta yanke duk wata alaƙa da kai, ko kaɗan abin bai damu Daddy ba da yake dama bai yi niyyar aurar da ita a lokacin ba. Ya ci burin sai ta yi karatu mai zurfi ta karanci harkar lafiya, amma ita Raihan sam karatun likitanci ba shi ne a gabanta ba tafi sha'awar lecturing. Mommy tun tana ɗaukan abin wasa da shirmen ƙuruciya har abin ya fara damunta a zuciya, don har Raihan ta kai shekara goma sha takwas babu wanda ya taɓa fitowa ya ce yana sonta ta amshi tayinsa. Hasalima daga ƙarshe samarin ma daina zuwa suka yi, idan mommy ta yi wa Daddy magana sai dai ya rufe ta da faɗa ya ce Raihan nawa take da don bata yi saurayi ba har za a damu. Daga ƙarshe Mommy daina bin ta kansa ta yi, ita ma Raihan ɗin idan mommy ta yi mata magana sai dai ta ce mata ita fa tana da mijin aure. Kusan kullin sai Mommy ta yi nafilar dare ta kaiwa Allah kukanta akan ya bayyana musu abin da yake daminta dan kuma jinkirin aure ne ya sa jinkirin ya zama alƙairi.
MU DAWO LABARI.
Jin Huzaifa ya datse maganar da ya fara yi ya sa Malam Usman ya ce, "Idan baka da abin faɗa Huzaifa kar ka ɓata min lokaci." Huzaifa ya sake numfasawa sannan ya ce, "Wata rana ina shawagi a sararin samaniya ranar ina cikin farinciki, kawai ta raya min na bi gidajen Bil'adam ko na kashe ƙwarƙwatar idona, a wani gida na ci karo da Raihan a lokacin bata fi shekara huɗu a duniya ba. Cikin dare ne don dare ya tsala sosai, tana kwance a ɗakinta wanda ya ƙayatu fa ƴar tsanoni kala-kala, daga gefen gadonta Mahaifinta ne a zaune yana ɗan danne-danne a laptop. Sai wayarsa da take fitar da sautin sasaanyar waƙa turawa, har na yi hiyyar giftawa na hangi surara yarinyar gwanin birgewa kanta ba ɗankwali gashi tana rungume da wani teddy. Shafata na yi nan take naji wani sabon yanayi da ban taɓa ji a jikina ba, dukda na yi mu'amala da matan bil'adam babu adadi amma yanayin da na ji game da ita na musamman ne. Ina cikin wannan yanayin Mahaifiyarta ta shigo ɗakin tana yi wa mahaifinta magana, "Haba Daddyn Raihan. Dare fa mahutar bawa ne ka rinƙa hutawa ranka mana, ga shi ka kunna waƙa biyu saura fa. Ni ma daga yin shafa'i da wuturi shikenan bacci ya yi gaba da ni, yarinyar nan ban san lokacin da ka kwnatar da ita ba." Ina kallo mahaifinta ya miƙe yace, "Ai na gama mu wuce kawai." Mahaifiyarta ce ta ƙaraso wurin da nake rungume da Raihan ta fara yi mata addu'a ba shiri na tashi daga wurin daga ƙarshe ma karatun kur'ani ta kunna mata a waya akan dole na haƙura da gidan gabaɗaya."
Wash🤠yau na sha typin.
Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ki min mgna 0706 206 2624
23