Sashe 49
Zaujatu Jinnul Ashiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Sannu a hankali rayuwa ta ci gaba da tafiya abubuwa da dama suka shuɗe kwanaki na ƙarewa. A haka har lokacin bikin Salim da Raihan ya ƙarato, sai dai har lokacin idan Raihan ta tuna babu aminyarta Intisar za a yi aurenta tana jin babu daɗi a ranta. Daga ɓangaren su Mommy shirye-shirye sun yi nisa su Inno sai jiƙe-jiƙe suke yi wa Raihan a cewarsu sune ya kamata su yi Raihan gyaran da duk yakata a yi wa Amarya. Saura sati biyu biki aka kawo lefen aure daga gidansu Salim, lefe ne ɗan ubansu na kece raini dukda akwatuna shida Salim ya yi mata amma an zuba mata kaya masu tsada tare da ƙunshin kuɗi masu yawa. A ranar da aka kawo kayan lefen saboda farinciki Mommy kasa bacci ta yi, lokaci-lokaci take tuna wai Raihan ɗinta ce za ta yi aure. Ita kanta Raihan ba ƙaramin farinciki ta yi ba saboda murna har da ƙwallarta, daga ƙarshe ta tashi cikin dare ta yi sallar nafila tare da gode wa Allah bisa wannan ni'ima da ya yi mata.
"Ya ke abar bauta wannan shirin da muka yi gani nake kamar ya yi yawa, kina ganin Raihan gadan-gadan aure ta yi yanzu haka za mu saka ido nasarorin ƙungiya suna dakushe wa." Hatsabibiya ta yi maganar hankali a matuƙar ɓace. Abar bauta ta saki wata shu'umar dariyar sannan ta ce, "Auren Raihan ba zai hana mu gudanar da abin da muka yi niyya ba, ba na ganin auren Raihan zai kawo mana cikas domin yin aurenta shi zai ba mu damar aiwatar da duk abin da muke so, saboda idan ta yi aure duk wanu zarge-zarge da ake yi mata na jinnu zai kau za mu biyar da ita yadda muke so." Hatsabibiya ta lalubo hannun Mijinta ta saƙale shi sai da suka je bakin wata baƙar rijiya sannan ta ce, "Tabbas abar bauta ke ya cancanci ki amsa sunan Hatsabibiya saboda kin wuce tunanin mai tunani. Wai Abar bauta Mugaza har yanzu babu amo baby labari ne?" Abar bauta ta wage ɗaya daga cikin bakunan jikinta ta hau ɓaɓɓaka dariya sannan ta ce, "Mugaza tana can tana jinyar Huzaifa saboda kaɗan ya rage bai mutu ba, kin ga ta yuwu lokaci da za mu mallaki gangar jiki da ruhin Raihan har lokacin Huzaifa bai maro daga jinyar da yake ciki ba." Hatsabibiya ta sake bushewa da dariya sannan ta suka faɗa cikin taohuwar rijayar nan take ta shafe daga kamar ba a taɓa ƙirƙirar rami a wurin ba.
Wata ƙawar Mommy Hajiya Safiya ita take zuwa har gida tana yi wa Raihan gyaran jiki, sana'arta ce har wasu garuruwan take zuwa gyaran amare. Hajiya Safiya gyara take yi wa Raihan ciki da waje don har magungunan gyaren jiki take haɗawa, Daddy ban da shige da ficen shirin biki babu abin da yake yi. Bikin Raihan saura sati guda tuni Daddy ya gama tanadar komai na hidimar biki, an sanarwa da ƴan uwa da abokan arziƙi tuni shirye-shirye ya yi nisa daga gidansu Raihan zuwa gidansu Salim lokacin biki kawai suk jira. Ƙawayen Raihan ba ƙaramin mamakin jin bikin Raihan suka yi ba, haka suka yi ta tsegungumi kowa yana son sanin waye mijin da ya yi shahada zai auri Raihan, saboda Daddy bai ɓoyewa Salim da iyayensa komai ba game da ciwon Raihan, duk da ƙawayenta sun san warkewarta amma mafi yawan ƙawayenta ba su yarda ba.
MUN KUSA SHAN AMARCI🤸ðŸ»â€â™€ï¸ ALLAH YA SA DAI KAR SALIM YA HAÆŠU DA AMAYAR KAZA😂
Littafin kuɗi ne 300 idan kina buƙata ki min mgn ta wannan number 0706 206 2624
27
Raihan ba ƙaramin kyau ta yi ba fatar jikinta ban da sheƙi babu abin da take yi, ta yi wani irin fresh kallo ɗaya za ka yi mata ka ji kamar ka sace ta. Tun ranar Laraba aka fara bikin Raihan, a ranar ne ta yi bridal shower da ita da wasu tsirarin ƙawayenta. Doguwar riga baƙa ta saka mai ratsin fararen duwatsu, kasancewarta mai hasken fata ba ƙaramin kyau kayan suka yi mata ba. Ƙawayenta su Shida suka yi ankon Ash ɗin material, a cikin gidansu Raihan aka yi komai. Suka kira masu decorations suka tsara musu komai gwanin birgewa. Ranar alhamis aka yi kamun amarya da ango, a ranar Raihan ta saka blue ɗin atamfa shi kuma Salim ya saka blue ɗin shadda. Ba ƙaramin burge mutane suka yi ba, kasancewar Salim mai matuƙar barkwanci ya sa ban da fara'a babu abin da yake yi. Abokansa ba ƙaramin ƙoƙari suka yi ba don sun yi masa kara matuƙa, da su aka yi komai aka watse daga taro. Ranar juma'a aka ɗaura aure da kimanin ƙarfe biyu na rana lokacin an sauko daga sallar juma'a, an ɗaura auren Salim da Raihan a masallacin Marigayi Sheik Jafar da ke unguwar ɗorayi.
Ƙarfe goman dare aka fara dinner su Raihan a Lailan Event center, wani rantsattsen leshi Raihan ta saka wanda Daddy ya siyo mata daga Dubai. Su Inno an kame a kan kujeru sai kallon mutane suke ɗaiɗai bakin nan ya ƙi rufuwa. A yadda aka tsara Dinner babu mutane da yawa amma su Inno suka kafe kai da fata akan duk mutanen da suka zo daga Albasu da waɗanda suka zo daga Daura sai an shiga da su. Sai da Mommy ta yi musu dabara sannan ta samu suka bar maganar. Farar Shadda Salim ya sa daga shi har Raihan sai dai mutum ya ce sam barka, sai mai hassada shi zai kushe irin kwalliyar da suka yi. Anci an sha taro ba ƙaramin kyau ya yi ba mommy sai hada-hada take yi da mutane, ita kanta ba ƙaramin kyau ta yi ba. Kimanin ƙarfe sha biyun dare aka tashi daga dinner, Salim da Raihan a motar abokinsa Muhsin suka zo. Da za su koma gida ma motarsa suka shiga, Salim riƙo hannun Raihan ya yi lokaci ɗaya gabanta ya faɗi sakamakon haka bata taɓa kasancewa tsakaninta da shi ba. Ɗagowa ta yi suna haɗa ido ta sunkuyar da kai ƙasa saboda wata irin kunyarsa da ta ji. Janyota ya yi jikinsa a lokacin Muhsin ya buɗe ƙofar zai shiga, yana ganin haka ya koma da baya. Raihan ta zaro ido waje ta ce, "Habibi Muhsin fa ya ganmu." Salim ya sumbaci gefen wuyanta cikin kasalalliyar murya ya ce, "Shi ma yana komawa gida wurin matarsa za shi, laifi ne don na zo wurin tawa matar?" Kunya ta kama Raihan ta yi shiru tana murza ƴan yatsunta, Salim ya sake kwantar da murya ya ce, "Ni dai gaskiya ki cewa su Daddy a kai ki yau Allah gobe fa ta yi nisa." Raihan ta buɗe baki tana zaro ido ta ce, "A'a wallahi rufa min asiri inmutu maza su kaini." Muhsin ne ya kira shi a waya yana ɗauka Salim ya fita daga motar zai yi magana Muhsin ya ce, "Kai fa ɗan iska ne ai ka bari idan Allah ya kaimu gobe ka fara ɗana amarcin." Salim ya yi dariya ce, "Ɗan sa ido me ye naka a ciki." Dariya suka yi gabaɗaya sannan suka shiga motar suka wuce gida.
Washegari.
Bayan sallar Magriba aka shirya Raihan cikin wata tsadaddiyar alkyabba, ba ƙaramin kyau ta yi ba sai dai tun da gari ya waye ban da kuka babu abin da Rainan take yi. Lokacin da za a tafi kaita su Inno ne suka yi mata nasiha sosai da sauran tsofaffin da suke wurin, ana cewa Raihan ta fito ta rungume Mommy ta sa kuka. Ita kanta Mommy tun tana dakewa har ta gagara ta fashe da kuka, da ƙyar aka cireta daga jikin Mommy kai tsaye ta falon Daddy aka wuce da ita tana ganin Daddy ta rungume shi ta fashe da wani irin kuka. Murmushi Daddy ya yi don jin kukanta yake har cikin ransa. Nasiha ya yi mata mai ratsa jiki daga nan aka wuce da ita ɗaya daga cikin motar da Salim ya aiko don ɗaukan amarya.
Tsayawa tsara gidan Raihan ɓata lokaci ne saboda Daddy ba ƙaramin kuɗi ya kashe mata ba, kai tsaye gidansu Salim aka fara kai Raihan Mahaifiyarsa ta yi mata nasiha sannan ta ɗauko turarrika da kuɗi ta bawa Hafsa ƙanwar mommy da take riƙe da ita daga nan suka wuce da ita katafaran gidanta da ke Tudun yola.
"Ya ke abar bauta wannan shirin da muka yi gani nake kamar ya yi yawa, kina ganin Raihan gadan-gadan aure ta yi yanzu haka za mu saka ido nasarorin ƙungiya suna dakushe wa." Hatsabibiya ta yi maganar hankali a matuƙar ɓace. Abar bauta ta saki wata shu'umar dariyar sannan ta ce, "Auren Raihan ba zai hana mu gudanar da abin da muka yi niyya ba, ba na ganin auren Raihan zai kawo mana cikas domin yin aurenta shi zai ba mu damar aiwatar da duk abin da muke so, saboda idan ta yi aure duk wanu zarge-zarge da ake yi mata na jinnu zai kau za mu biyar da ita yadda muke so." Hatsabibiya ta lalubo hannun Mijinta ta saƙale shi sai da suka je bakin wata baƙar rijiya sannan ta ce, "Tabbas abar bauta ke ya cancanci ki amsa sunan Hatsabibiya saboda kin wuce tunanin mai tunani. Wai Abar bauta Mugaza har yanzu babu amo baby labari ne?" Abar bauta ta wage ɗaya daga cikin bakunan jikinta ta hau ɓaɓɓaka dariya sannan ta ce, "Mugaza tana can tana jinyar Huzaifa saboda kaɗan ya rage bai mutu ba, kin ga ta yuwu lokaci da za mu mallaki gangar jiki da ruhin Raihan har lokacin Huzaifa bai maro daga jinyar da yake ciki ba." Hatsabibiya ta sake bushewa da dariya sannan ta suka faɗa cikin taohuwar rijayar nan take ta shafe daga kamar ba a taɓa ƙirƙirar rami a wurin ba.
Wata ƙawar Mommy Hajiya Safiya ita take zuwa har gida tana yi wa Raihan gyaran jiki, sana'arta ce har wasu garuruwan take zuwa gyaran amare. Hajiya Safiya gyara take yi wa Raihan ciki da waje don har magungunan gyaren jiki take haɗawa, Daddy ban da shige da ficen shirin biki babu abin da yake yi. Bikin Raihan saura sati guda tuni Daddy ya gama tanadar komai na hidimar biki, an sanarwa da ƴan uwa da abokan arziƙi tuni shirye-shirye ya yi nisa daga gidansu Raihan zuwa gidansu Salim lokacin biki kawai suk jira. Ƙawayen Raihan ba ƙaramin mamakin jin bikin Raihan suka yi ba, haka suka yi ta tsegungumi kowa yana son sanin waye mijin da ya yi shahada zai auri Raihan, saboda Daddy bai ɓoyewa Salim da iyayensa komai ba game da ciwon Raihan, duk da ƙawayenta sun san warkewarta amma mafi yawan ƙawayenta ba su yarda ba.
MUN KUSA SHAN AMARCI🤸ðŸ»â€â™€ï¸ ALLAH YA SA DAI KAR SALIM YA HAÆŠU DA AMAYAR KAZA😂
Littafin kuɗi ne 300 idan kina buƙata ki min mgn ta wannan number 0706 206 2624
27
Raihan ba ƙaramin kyau ta yi ba fatar jikinta ban da sheƙi babu abin da take yi, ta yi wani irin fresh kallo ɗaya za ka yi mata ka ji kamar ka sace ta. Tun ranar Laraba aka fara bikin Raihan, a ranar ne ta yi bridal shower da ita da wasu tsirarin ƙawayenta. Doguwar riga baƙa ta saka mai ratsin fararen duwatsu, kasancewarta mai hasken fata ba ƙaramin kyau kayan suka yi mata ba. Ƙawayenta su Shida suka yi ankon Ash ɗin material, a cikin gidansu Raihan aka yi komai. Suka kira masu decorations suka tsara musu komai gwanin birgewa. Ranar alhamis aka yi kamun amarya da ango, a ranar Raihan ta saka blue ɗin atamfa shi kuma Salim ya saka blue ɗin shadda. Ba ƙaramin burge mutane suka yi ba, kasancewar Salim mai matuƙar barkwanci ya sa ban da fara'a babu abin da yake yi. Abokansa ba ƙaramin ƙoƙari suka yi ba don sun yi masa kara matuƙa, da su aka yi komai aka watse daga taro. Ranar juma'a aka ɗaura aure da kimanin ƙarfe biyu na rana lokacin an sauko daga sallar juma'a, an ɗaura auren Salim da Raihan a masallacin Marigayi Sheik Jafar da ke unguwar ɗorayi.
Ƙarfe goman dare aka fara dinner su Raihan a Lailan Event center, wani rantsattsen leshi Raihan ta saka wanda Daddy ya siyo mata daga Dubai. Su Inno an kame a kan kujeru sai kallon mutane suke ɗaiɗai bakin nan ya ƙi rufuwa. A yadda aka tsara Dinner babu mutane da yawa amma su Inno suka kafe kai da fata akan duk mutanen da suka zo daga Albasu da waɗanda suka zo daga Daura sai an shiga da su. Sai da Mommy ta yi musu dabara sannan ta samu suka bar maganar. Farar Shadda Salim ya sa daga shi har Raihan sai dai mutum ya ce sam barka, sai mai hassada shi zai kushe irin kwalliyar da suka yi. Anci an sha taro ba ƙaramin kyau ya yi ba mommy sai hada-hada take yi da mutane, ita kanta ba ƙaramin kyau ta yi ba. Kimanin ƙarfe sha biyun dare aka tashi daga dinner, Salim da Raihan a motar abokinsa Muhsin suka zo. Da za su koma gida ma motarsa suka shiga, Salim riƙo hannun Raihan ya yi lokaci ɗaya gabanta ya faɗi sakamakon haka bata taɓa kasancewa tsakaninta da shi ba. Ɗagowa ta yi suna haɗa ido ta sunkuyar da kai ƙasa saboda wata irin kunyarsa da ta ji. Janyota ya yi jikinsa a lokacin Muhsin ya buɗe ƙofar zai shiga, yana ganin haka ya koma da baya. Raihan ta zaro ido waje ta ce, "Habibi Muhsin fa ya ganmu." Salim ya sumbaci gefen wuyanta cikin kasalalliyar murya ya ce, "Shi ma yana komawa gida wurin matarsa za shi, laifi ne don na zo wurin tawa matar?" Kunya ta kama Raihan ta yi shiru tana murza ƴan yatsunta, Salim ya sake kwantar da murya ya ce, "Ni dai gaskiya ki cewa su Daddy a kai ki yau Allah gobe fa ta yi nisa." Raihan ta buɗe baki tana zaro ido ta ce, "A'a wallahi rufa min asiri inmutu maza su kaini." Muhsin ne ya kira shi a waya yana ɗauka Salim ya fita daga motar zai yi magana Muhsin ya ce, "Kai fa ɗan iska ne ai ka bari idan Allah ya kaimu gobe ka fara ɗana amarcin." Salim ya yi dariya ce, "Ɗan sa ido me ye naka a ciki." Dariya suka yi gabaɗaya sannan suka shiga motar suka wuce gida.
Washegari.
Bayan sallar Magriba aka shirya Raihan cikin wata tsadaddiyar alkyabba, ba ƙaramin kyau ta yi ba sai dai tun da gari ya waye ban da kuka babu abin da Rainan take yi. Lokacin da za a tafi kaita su Inno ne suka yi mata nasiha sosai da sauran tsofaffin da suke wurin, ana cewa Raihan ta fito ta rungume Mommy ta sa kuka. Ita kanta Mommy tun tana dakewa har ta gagara ta fashe da kuka, da ƙyar aka cireta daga jikin Mommy kai tsaye ta falon Daddy aka wuce da ita tana ganin Daddy ta rungume shi ta fashe da wani irin kuka. Murmushi Daddy ya yi don jin kukanta yake har cikin ransa. Nasiha ya yi mata mai ratsa jiki daga nan aka wuce da ita ɗaya daga cikin motar da Salim ya aiko don ɗaukan amarya.
Tsayawa tsara gidan Raihan ɓata lokaci ne saboda Daddy ba ƙaramin kuɗi ya kashe mata ba, kai tsaye gidansu Salim aka fara kai Raihan Mahaifiyarsa ta yi mata nasiha sannan ta ɗauko turarrika da kuɗi ta bawa Hafsa ƙanwar mommy da take riƙe da ita daga nan suka wuce da ita katafaran gidanta da ke Tudun yola.