Sashe 56
Zaujatu Jinnul Ashiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Satin su Raihan ɗaya suka ɗunguma zuwa ƙasa mai tsarki, kafin tafiyarsu Daddy sai da ya gama yi wa Raihan komai ya yi mata awon kayanta sannan suka wuce ƙasar Saudiya. Su Inno baki ya ƙi rufuwa dukda wannan zuwan nasu ba shi ne na farko ba amma farincikin kasancewarsu a ƙasar ya sa murna ta cika su. Mommy sosai ta duƙufa wurin yi wa Raihan addu'ar Allah ya cire mata damuwar da take ciki, ya kuma mantar da ita Salim daga zuciyarta. Ta yi mata addu'a sosai akan Allah ya fito mata da miji nagari. Ita kanta Raihan ta yi wa kanta addu'a sosai a harami, ta kuma yi wa Salim addu'a mai yawan da neman Allah ya zaɓa mata abin da ya fi alheri a rayuwarta. Ana gobe za su dawo Nigeria da daddare sun dawo daga sallar Tarawi za su tsallaka don zuwa hotel ɗin da suka sauka. Kamar a mafarki ta hango mutum a bakin titi zai tsallaka, wani ni'imtaccen murmushi ne ya suɓucewa Raihan ta dubi Mommy ta ce, "Mommy kin ga mutumin nan da nake baki labari." Gaban mommy ne ya faɗi don tana tsoron kar Raihan ta sake gano mata mai kama da Salim, kallon wurin ta yi ta hango wani matashin saurayi da yake tsaye da baƙar jallabiya a jikinta. Da ganin yanayinsa shi ma baƙar fata ne don haka cikin rashin fahimta Mommy ta ce, "Waye wancen ɗin?" Raihan ta ce, "Wanda na taɓa baki labari na bige shi yana mashin ina cikin mota. Don Allah mommy na je na yi masa magana." Haɗe fuska Mommy ta yi ta ce, "Ba na son sakarci me kike yi haka? Raihan ko kin manta ke mace ce ne? Idan kin yi masa magana ki ce masa me?" Raihan gabanta na ci gaba da faɗuwa ta ce, "Wallahi ba wani abu zan yi ba Mommy haƙuri kawai zan bashi." Tsaki Mommy ta yi ta ce, "Da can baki bashi haƙuri ba sai yanzu." Idon Raihan ya ciko da ƙwallah ta ce, "Don Allah mommy." Mommy ta sake ɗaure fuska ta ce, "Maza ki je yanzu ki dawo ina jiranki." Daɗi ne ya kama Raihan har a fili sai da ta murmusa. A hankali ta fara takawa tana gabda ƙarasawa wurinsa ya fara haramar tsallakawa, da sauri ta furta: "Bawan Allah ɗan tsaya!" A hankali Al'amin ya tsaya juyo jin muryar bahaushiya na yi masa magana, takawa ya fara yi wurinta sannan ya nuna ƙirjinsa ya ce, "Da ni kike?" Raihan kai ta gyaɗa masa ta ce, "Am dama haƙuri na zo in baka." Da mamaki ya ɗan zaro ido ya ce, "Haƙuri kuma me kika yi min?" Raihan ta ɗan sosa kai a kunyace ta ce, "A nigeria ne dama na taɓa yi maka laifi." Wannan karonma zaro ido ya sake yi don rabonsa da Nigeria ya haure shekara biyu. Raihan tana cikin nazari ta riski muryarsa ya ce, "Duk irin laifin da kika min na yafe miki." Murmushi ta yi masa tana son sake yi masa magana ta ji ya ce, "Idan babu damuwa zan tsallaka wani Bro ɗina yana jirana." Raihan na son karɓar lambar wayarsa amma sai ta rasa me za ta ce masa kunya ta kama shi, don haka ta yi masa godiya suka yi sallama Al'amin ya tsalla ita kuma ta koma wurin Mommy sannan ita ma suka tsallaka suka yi ɓangaren wurin da Hotel ɗin su yake.
Wani irin farinciki Raihan take ji har sai da mommy ta fahimci halin da take ciki, mommy murmushi ta yi don ta fahimci Raihan na matuƙar ƙaunar bawan Allahn tun kafin wannan ranar. Abin da ya sa bata ba ta goyon baya bata san ya halin yaron yake ba tun da a wannan lokacin da ake ciki namiji ya nuna shi yake sonka ma ya gari ya waya balle a ce mace ita ta kai kanta. Abin da Mommy ta ƙudurtawa kanta komai rubutacce ne a wurin Ubangiji Idan Allah ya yi mijinta ne babu makawa sai ta aure shi, idan kuma ba mijinta ba ne duk yadda ta ƙaunace shi ba za ta taɓa aurensa ba. Don haka take ci gaba da yi wa Raihan addu'a da fatan alheri akan dukkan lamuranta. Su Raihan sai da suka shafe sati biyu a ƙasa mai tsarki sannan suka dawo gida Nigeria, tun daga ranar da Raihan ta ga Al'amin kullin suka fita ta rinƙa baza idanu ko za ta ƙara ganinsa amma ko mai kama da shi ba ta gani ba, ta ciza yatsa sosai don ta yi dana-sanin rashin amsar lambarsa hasalima ko sunansa bata sani ba balle ta san wani abu game da shi. Har addu'a ta riƙa yi Allah ya sa ta gan shi ko a hanya ne kamar wancen karon amma ko walƙiyarsa bata gani ba, ranar da za su tafi ƙuncin duniya ya rufe ta don ko kaɗan ba haka ta so ba. Tun tana fushinta a ɓoye har ya fito fili, a nan Daddy yake tambayarta abin da yake damunta don ya san Raihan ba ma'abociyar fushi bace. Bata ɓoye masa komai ba tun daga lokacin da ta ga Al'amin har lokacin tafiyarsu, shi kansa ya ji babu daɗi amma sai ya ƙarfafeta ta hanyar yi mata nasiha akan abin da ya dace da wanda bai kamata ba. Tare da nusar da ita illar abin da take shirin aikatawa dukda ba haramin ba ne a musulunci mace ta furta soyayya ga namiji, har ya nuna mata da ace ya san yaron yana iya yi masa tayin auren Raihan ba wai don ta gaza ko bata da masoyi ba. Ko ba komai Raihan ta ji daɗi don haka ta ci gaba da harkokinta.
Suna Airport gabda za su shiga jirgi suna zaune su Inno sai kalle-kalle suke yi, idan suka hango wani abin da bai yi musu ba sai dai Mommy ta ji suna ƙusƙus abin su. Idan kuma wani abin ne ya ba su dariya sai dai su ji su Inno sun tuntsire da dariya, Raihan ce ta shiga yi musu hotuna da Videos ba tare da sun sani ba sai da ta gama yi musu sannan kuma suka ɗaɗɗauki hotuna gabaɗayansu. Daddy na daga zaune ya hango Malam Usman da wata mace a tare da shi, kallo ɗaya za ka yi musu ka tabbatar da iyalinsa ce. Fara ce matar mai ɗan jiki yanayinta zai tabbatar maka da babarbariya ce duba da yanayin shigarta da tsagun fuskarta, Malam Usman bai ga Daddy ba sai Daddy ne ya yi masa magana haɗe da ƙarasawa wurinsa. Cikin mutumci suka gaisa Daddy ya ce, "Malam Usman kar dai jirginku ne ya sauka." Matar Malam Usman suka gaisa da Daddy a daidai lokacin Mommy ta ƙaraso, Malam Usman na hango su Inno ya ƙarasa ya tsugunna har ƙasa ya gaishe su sanna ya dubi Daddy ya ce, "Wallahi zuwanmu kenan hala duk jirgi ɗaya muka hau?" Daddy ya yi murmushi ya ce, "A'a mu ai yau za my wuce." Raihan ce ta gaida Malam Usman ya amsa har yana tambayarta sauƙin jikinta ta amsa masa. Adaidai lokacin jirgin su Daddy ya fara shela, Malam Usman ya ce, "To Alhaji sai mun taho. Ni ma na jima a nan ɗan wurina nake jira Al'amin tun ɗazu bai ƙaraso ba." Daddy da suke haramar wuce wa ya ce, "Kasan yaran nan da shiririta ta yuwu wani abu ne ya tsayar da shi." Daga haka suka yi sallama suka wuce ɓangaren da za su shiga ya sada su da jirgin da za su hau. Barin wurinsu ke da wuya Al'amin ya ƙaraso cike da zolaya ya ce wa Mahaifinsa, "Ahlan wasahlam ya Abiey." Malam Usman ya ce, "Balaraben Sudan ka shanya mu da yawa, tun ba wannan tsohuwar taka ba yau ina jin sai ta yi wa ƙafafuwanta ruwan zafi." Murmushi ya yi sannan ya yi musu barka da zuwa babu jimawa suka wuce masaukinsa.
Littafin kuɗi ne 300 idan kina buƙata ki min mgn 0706 206 2624
31
Raihan har suka dawo gida Nigeria bata da tunani sama da na Al'amin, ita kaɗai take sakin murmushi lokaci-lokaci idan ta tuna lokacin da suke tattauna wa ita da shi. Saboda yanayin daɗewar da suka yi basa gida ya sa kafin komawarsa Mommy ta yi wa Mama Hafsa magana ta turo wasu maƙonta da byake ba su da ƙarfi kuma ana ɗan basu wankau da sirfau, sai ta haɗo su da su Safna suka zo suka gyara gidansu Raihan. Don tun daga kan Mama Uwani su Mommy suka ce sun yaye ɗaukan kowacce mai aiki, ana gobe su Raihan za su dawo tuni an gyaran gidan komai ya yi tsaf don haka suna dawo wa suka samu komai tsaf gwanin sha'awa. A gajiye Raihan ta faɗa ɗakinta sai da ta ajiye jakar hannunta sannan ta ta fara rage kayan jikinta, a gajiya ta shiga banɗaki ta watsa ruwa. Kan katifarta ta kwanta ta lumshe ido tana hakaito fuskar Al'amin a lokacin da yake yi mata murmushi. A hankali ta tashi zaune ta furta, "Sau biyu kaɗai na taɓa ganinsa amma soyayyarsa na neman malale birnin zuciyata. Allah ka bayyana min shi a matsayin masoyi idan da alheri a tarrayata da shi" Hannunta ta kai saitin ƙirjinta a daidai lokacin bugun zuciyarta ya ƙaru, ta janyo fulo ta rungume haɗe da ɗora kanta a kan fulon ta furta, "Bayan Salim ban taɓa jin mutumin da ya ƙawata birnin zuciyata ba sai wannan gwarzon mazajen." Tana zaune tana zancen zuci har ta ji bacci na neman lulluɓe idonta ta, a hankali ta ja blanket ta kwanta, babu jima wa bacci ya yi awon gaba da ita.
Wani irin farinciki Raihan take ji har sai da mommy ta fahimci halin da take ciki, mommy murmushi ta yi don ta fahimci Raihan na matuƙar ƙaunar bawan Allahn tun kafin wannan ranar. Abin da ya sa bata ba ta goyon baya bata san ya halin yaron yake ba tun da a wannan lokacin da ake ciki namiji ya nuna shi yake sonka ma ya gari ya waya balle a ce mace ita ta kai kanta. Abin da Mommy ta ƙudurtawa kanta komai rubutacce ne a wurin Ubangiji Idan Allah ya yi mijinta ne babu makawa sai ta aure shi, idan kuma ba mijinta ba ne duk yadda ta ƙaunace shi ba za ta taɓa aurensa ba. Don haka take ci gaba da yi wa Raihan addu'a da fatan alheri akan dukkan lamuranta. Su Raihan sai da suka shafe sati biyu a ƙasa mai tsarki sannan suka dawo gida Nigeria, tun daga ranar da Raihan ta ga Al'amin kullin suka fita ta rinƙa baza idanu ko za ta ƙara ganinsa amma ko mai kama da shi ba ta gani ba, ta ciza yatsa sosai don ta yi dana-sanin rashin amsar lambarsa hasalima ko sunansa bata sani ba balle ta san wani abu game da shi. Har addu'a ta riƙa yi Allah ya sa ta gan shi ko a hanya ne kamar wancen karon amma ko walƙiyarsa bata gani ba, ranar da za su tafi ƙuncin duniya ya rufe ta don ko kaɗan ba haka ta so ba. Tun tana fushinta a ɓoye har ya fito fili, a nan Daddy yake tambayarta abin da yake damunta don ya san Raihan ba ma'abociyar fushi bace. Bata ɓoye masa komai ba tun daga lokacin da ta ga Al'amin har lokacin tafiyarsu, shi kansa ya ji babu daɗi amma sai ya ƙarfafeta ta hanyar yi mata nasiha akan abin da ya dace da wanda bai kamata ba. Tare da nusar da ita illar abin da take shirin aikatawa dukda ba haramin ba ne a musulunci mace ta furta soyayya ga namiji, har ya nuna mata da ace ya san yaron yana iya yi masa tayin auren Raihan ba wai don ta gaza ko bata da masoyi ba. Ko ba komai Raihan ta ji daɗi don haka ta ci gaba da harkokinta.
Suna Airport gabda za su shiga jirgi suna zaune su Inno sai kalle-kalle suke yi, idan suka hango wani abin da bai yi musu ba sai dai Mommy ta ji suna ƙusƙus abin su. Idan kuma wani abin ne ya ba su dariya sai dai su ji su Inno sun tuntsire da dariya, Raihan ce ta shiga yi musu hotuna da Videos ba tare da sun sani ba sai da ta gama yi musu sannan kuma suka ɗaɗɗauki hotuna gabaɗayansu. Daddy na daga zaune ya hango Malam Usman da wata mace a tare da shi, kallo ɗaya za ka yi musu ka tabbatar da iyalinsa ce. Fara ce matar mai ɗan jiki yanayinta zai tabbatar maka da babarbariya ce duba da yanayin shigarta da tsagun fuskarta, Malam Usman bai ga Daddy ba sai Daddy ne ya yi masa magana haɗe da ƙarasawa wurinsa. Cikin mutumci suka gaisa Daddy ya ce, "Malam Usman kar dai jirginku ne ya sauka." Matar Malam Usman suka gaisa da Daddy a daidai lokacin Mommy ta ƙaraso, Malam Usman na hango su Inno ya ƙarasa ya tsugunna har ƙasa ya gaishe su sanna ya dubi Daddy ya ce, "Wallahi zuwanmu kenan hala duk jirgi ɗaya muka hau?" Daddy ya yi murmushi ya ce, "A'a mu ai yau za my wuce." Raihan ce ta gaida Malam Usman ya amsa har yana tambayarta sauƙin jikinta ta amsa masa. Adaidai lokacin jirgin su Daddy ya fara shela, Malam Usman ya ce, "To Alhaji sai mun taho. Ni ma na jima a nan ɗan wurina nake jira Al'amin tun ɗazu bai ƙaraso ba." Daddy da suke haramar wuce wa ya ce, "Kasan yaran nan da shiririta ta yuwu wani abu ne ya tsayar da shi." Daga haka suka yi sallama suka wuce ɓangaren da za su shiga ya sada su da jirgin da za su hau. Barin wurinsu ke da wuya Al'amin ya ƙaraso cike da zolaya ya ce wa Mahaifinsa, "Ahlan wasahlam ya Abiey." Malam Usman ya ce, "Balaraben Sudan ka shanya mu da yawa, tun ba wannan tsohuwar taka ba yau ina jin sai ta yi wa ƙafafuwanta ruwan zafi." Murmushi ya yi sannan ya yi musu barka da zuwa babu jimawa suka wuce masaukinsa.
Littafin kuɗi ne 300 idan kina buƙata ki min mgn 0706 206 2624
31
Raihan har suka dawo gida Nigeria bata da tunani sama da na Al'amin, ita kaɗai take sakin murmushi lokaci-lokaci idan ta tuna lokacin da suke tattauna wa ita da shi. Saboda yanayin daɗewar da suka yi basa gida ya sa kafin komawarsa Mommy ta yi wa Mama Hafsa magana ta turo wasu maƙonta da byake ba su da ƙarfi kuma ana ɗan basu wankau da sirfau, sai ta haɗo su da su Safna suka zo suka gyara gidansu Raihan. Don tun daga kan Mama Uwani su Mommy suka ce sun yaye ɗaukan kowacce mai aiki, ana gobe su Raihan za su dawo tuni an gyaran gidan komai ya yi tsaf don haka suna dawo wa suka samu komai tsaf gwanin sha'awa. A gajiye Raihan ta faɗa ɗakinta sai da ta ajiye jakar hannunta sannan ta ta fara rage kayan jikinta, a gajiya ta shiga banɗaki ta watsa ruwa. Kan katifarta ta kwanta ta lumshe ido tana hakaito fuskar Al'amin a lokacin da yake yi mata murmushi. A hankali ta tashi zaune ta furta, "Sau biyu kaɗai na taɓa ganinsa amma soyayyarsa na neman malale birnin zuciyata. Allah ka bayyana min shi a matsayin masoyi idan da alheri a tarrayata da shi" Hannunta ta kai saitin ƙirjinta a daidai lokacin bugun zuciyarta ya ƙaru, ta janyo fulo ta rungume haɗe da ɗora kanta a kan fulon ta furta, "Bayan Salim ban taɓa jin mutumin da ya ƙawata birnin zuciyata ba sai wannan gwarzon mazajen." Tana zaune tana zancen zuci har ta ji bacci na neman lulluɓe idonta ta, a hankali ta ja blanket ta kwanta, babu jima wa bacci ya yi awon gaba da ita.