Sashe 106
Zaujatu Jinnul Ashiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A hargitse Raihan ta ɗago tana jin maganar Daddy har sai da ta ji wani irin dum! A kunnenta kamar an buga mata guduma, hawaye ne bibbiyu yake bin fusakar Raihan ta ce, "Daddy ɗazun nan fa ya fita ka ce min ya mutu an ya kuwa ba wani mai kama da shi ba ne." Daddy cikin lallashin ya ce, "Raihan mutuwa ɗaya ce Alhaji Shatima ya tafi sai dai mu yi masa addu'ar Allah ya gafarta masa." Kuka Raihan take sosai zuciyarta na ƙuna jikinta har rawa yake, Mommy ce ta riƙa lallashinta tare da yi mata nasiha har ta daina kukan fili ya zamana sai hawaye da ke bin idanunta. A ranar Daddy da sauran Abokan Alhaji Shatima suka tsaya kai da fata aka bada gawarsa, bayan an sanarwa ƴaƴansa da ƴan uwansa aka yi masa sallah aka kai shi makwancinsa. Mutuwar Alhaji Shatima ba ƙaramin taɓa su Daddy ta yi ba, Raihan har bayan sadakar bakwai gani take kamar Alhaji Shatima zai dawo don har lokacin gani take kamar wani ne ya mutu ba shi ba, saboda a ƴan kwanakin da ta yi da shi ya nuna mata kulawa babu wata magana da za ta faɗa ta ɓatanci akansa, irin kulawar da ta samu ta ƴan awanni ko a gidan Al'amin ba ta same ta ba. Daga haka rayuwa ta ci gaba da tafiya, Raihan ta ci gaba da zawarci a gidansu tana takaba. Wannan mutuwar ta Alhaji Shatima ita ta sake sarewa Raihan rai ta fidda maganar aure da soyayyarsa a zuciyarta, ta saka wa zuciyarta daga kansa ba za ta sake yin aure ba balle wani abu ya ƙara faruwa da ita ba. Malam da Al'amin da su aka gama zaman makokin Alhaji Shatima, sai dai Malam bai kawo komai ba dangane da zaman makokin da Al'amin yake zuwa a yi da shi sai a ranar da Raihan ta fita daga takaba sannan ya je ya samu Malam a gida. Bayan ya gama sauraronsa Malam ya furta, "A wannan karon ba zan jagoranci neman aurenka a wurin yarinyar nan ba domin a baya ka watsa min ƙasa a ido a wurin mutumin da nake ganin mutumcinsa yake ganin nawa. Ka je ka nemi soyayyar yarinya idan ta ga za ta saurareka shi kenan, idan bata yi da kai kuma Allah ya fito mata da wanda ya fika." Al'amin kamar zai yi kuka ya dubi Daddy ya ce, "Wallahi Daddy kunyarta nake ji." Malam ya riƙe baki sannan ya ce, "Amma dai baka da kunya Al'amin, wato ni ne ba na jin kunya da zan shige maka neman aurenta a kato na biyu ko? Fice ka ba ni wuri kafin ranka ya ɓaci." A sanyaye Al'amin ya miƙe ya fita, ya fi minti talatin a mota yana saƙa da warwara daga ƙarshe ya wuce gida. Tun da Sumayya ta ji rasuwar mijin Raihan hankalinta ya yi matsanancin tashi, don tana tsoron Al'amin ya ce zai dawo da ita ga shi har lokacin ba zaman daɗi suke yo ba balle ta nuna bata amince ba don a wannan lokacin ta san bata da wannan power.Tana zaune ya shiga tana yi masa sannu da zuwa da yauwa kawai ya amsa mata sannan ya wuce ɗaki, jiki a saluɓe Sumayya ta bishi don ya fito ya ci abinci amma ya ce mata baya ci. Duk yadda ta kai ga lallashinsa ya ƙi ƙarshe ma sai cewa ya yi ta fita ta bashi wuri baya son hayaniya, haka Sumayya ta fito fuska ɗauke da hawaye don ta lura yanzu ko kaɗan Al'amin baya gudun gaya mata magana ko ya ɓata mata rai.
Tsananin soyayyar Raihan ce ta hana shi sukuni har ya yanke shawarar zuwa gidansu don ya nemi soyayyarta, sai dai cike da ƙwarin gwiwa ya tafi saboda ya san a baya Raihan na mutuwar son sa. Lokacin da ya ce a yi sallama da ita fir ta ƙi fita don tuni ta daɗe da shafe shafin aure daga ranta. Al'amin babu yadda bai yi ba amma ta ƙi fitowa daga ƙarshe ma cewa Auwalu ta yi idan ya kuma zuwa wurinta sai ransa ya ɓaci, Al'amin haka ya juya ya tafi ba tare da ya samu abin da yake so ba. Lokaci ɗaya ya kaɗe ya lalace kamar ba shi ba, Malam na lura da yanyinsa duk da yana jin tausayin halin da yake ciki amma ya ji daɗin rashin haɗin kan da Raihan bata bashi ba, Ammi kuwa da har ta ce za ta je gidan su Raihan domin ta nemi alfarmarta akan a mayar da aurensu, Malam ya ce mata matuƙar ta fita ita ma sai ranta ya yi mummunan ɓaci. Wannan lamarin shi ya sake ɗaga hankalin Al'amin ga shi bai san wurin da zai sami lambarta ba, tun da ya yi zuwa ya fi biyar amma duk lokacin da ya je sai dai ace masa bata nan. Watarana Kabiru yana gidan da ya ji abin da Auwalu ya faɗa kishi ya turniƙe zuciyarsa, a fusace ya fito ya samu Al'amin ya gaya masa magananganu marasa daɗi. Al'amin ransa ba ƙaramin ɓaci ya yi ba ya dubi Kabiru ya ce, "Akan matata kake gaya min magana saboda baka da mutumci ko?" Kabiru ya yi dariyar rainin hankali sannan ya ce, "Amma dai kai baka da hankali, idan matarka ce me ya sa baka shiga ka ɗauki abarka ka tafi da ita ba. Indai Raihan ce ka rasata kenan har abada lusari mai ƙaramin tunani." A zafafe Al'amin ya yi kan Kabiru a daidai lokacin Daddy ya dawo daga masallaci, da sauri ya shiga tsakaninsu yana ƙoƙarin jin ba asi." Al'amin cikin ɓacin rai ya ce, "Daddy wai akan Raihan wannan banzan yake gaya min magana saboda na aika ayi sallama da ita." Kabiru ya karɓe maganar da cewa, "Daddy ana dole ne Raihan ta ce ba za ta fito ba, wai don na ce ya haƙura zai ce min matarsa ce a ina ta zama matarsa?" Daddy ya tura Kabiru cikin gida ya ce, "Wuce ciki bana son maganar." Sannan ya juya wurin Al'amin ya furta, "Don Allah ka yi haƙuri Al'amin." A kunyace Al'amin ya furta, "Ba komai Daddy ammm... Dama..." Sai kuma kunya ta kama shi ya kasa magana ya furta, "Shi kenan sai da safe Daddy."
Littafin kuɗi ne 300 idan kina buƙata ki min mgn 0706 206 2624
52
🔚🔚🔚🔚🔚🔚
Al'amin na tafe a mota lokaci-lokaci yake sakin tsaki don ya fahimci wani abu a tattare da Kabiru, ya hango kishi ƙarara a ƙwayar idonsa. Babban tashin hankalinsa da ya rasa ta yaya zai samu lambar Raihan balle ya sake bata haƙuri ya nemi soyayyarta. Gashi ya yi juyin duniya akan Malam ya yi wa Daddy magana fir ya ƙi yadda, ya kawo ido ya zura masa don ya ce sai dai ya nemi soyayyarta.
Daddy na shiga cikin gida ya samu Raihan a falo tana lissafin wasu kaya da ta yi order su. Zama ya yi a kujera ta kalle shi da murmushi ta ce, "Daddy barka da shigowa." Daddy ya amsa cikin sakin fuska sannan ya ce, "Raihan ashe Al'amin ya zo." Nan take ta haɗe fuska ta ce, "Ya zo Daddy amma ban fita saboda a yanzu ba na son abin da zai sake dagula lissafin rayuwata." Daddy ya yi murmushin irin nasu na manya ya ce, "Amma da kin saurare shi ki ji abin da yake tafe da shi." Raihan ta tura baki gaba ta ce, "Ai duk abin da yake tafe da shi na yafe masa ya riƙe kayansa Daddy." Dariya Daddy ya yi ya ce, "Shi kenan Raihan ɗin Daddy ba zan yi miki dole ba duk abin da kike so haka za a yi, amma fa kar ki manta aure sunnar Annabi ne." Raihan ta yi murmushi tana cewa, "Daddy ni fa ba komai nace ba amma gaskiya ni da aure kam sai nan da wasu shekaru." Daddy ya nufi hanyar part ɗin sa yana faɗin, "Shi kenan Allah ya nuna mana lokaci." Raihan ta amsa da Amin sannan ta ci gaba da abin da take yi.
Tsananin soyayyar Raihan ce ta hana shi sukuni har ya yanke shawarar zuwa gidansu don ya nemi soyayyarta, sai dai cike da ƙwarin gwiwa ya tafi saboda ya san a baya Raihan na mutuwar son sa. Lokacin da ya ce a yi sallama da ita fir ta ƙi fita don tuni ta daɗe da shafe shafin aure daga ranta. Al'amin babu yadda bai yi ba amma ta ƙi fitowa daga ƙarshe ma cewa Auwalu ta yi idan ya kuma zuwa wurinta sai ransa ya ɓaci, Al'amin haka ya juya ya tafi ba tare da ya samu abin da yake so ba. Lokaci ɗaya ya kaɗe ya lalace kamar ba shi ba, Malam na lura da yanyinsa duk da yana jin tausayin halin da yake ciki amma ya ji daɗin rashin haɗin kan da Raihan bata bashi ba, Ammi kuwa da har ta ce za ta je gidan su Raihan domin ta nemi alfarmarta akan a mayar da aurensu, Malam ya ce mata matuƙar ta fita ita ma sai ranta ya yi mummunan ɓaci. Wannan lamarin shi ya sake ɗaga hankalin Al'amin ga shi bai san wurin da zai sami lambarta ba, tun da ya yi zuwa ya fi biyar amma duk lokacin da ya je sai dai ace masa bata nan. Watarana Kabiru yana gidan da ya ji abin da Auwalu ya faɗa kishi ya turniƙe zuciyarsa, a fusace ya fito ya samu Al'amin ya gaya masa magananganu marasa daɗi. Al'amin ransa ba ƙaramin ɓaci ya yi ba ya dubi Kabiru ya ce, "Akan matata kake gaya min magana saboda baka da mutumci ko?" Kabiru ya yi dariyar rainin hankali sannan ya ce, "Amma dai kai baka da hankali, idan matarka ce me ya sa baka shiga ka ɗauki abarka ka tafi da ita ba. Indai Raihan ce ka rasata kenan har abada lusari mai ƙaramin tunani." A zafafe Al'amin ya yi kan Kabiru a daidai lokacin Daddy ya dawo daga masallaci, da sauri ya shiga tsakaninsu yana ƙoƙarin jin ba asi." Al'amin cikin ɓacin rai ya ce, "Daddy wai akan Raihan wannan banzan yake gaya min magana saboda na aika ayi sallama da ita." Kabiru ya karɓe maganar da cewa, "Daddy ana dole ne Raihan ta ce ba za ta fito ba, wai don na ce ya haƙura zai ce min matarsa ce a ina ta zama matarsa?" Daddy ya tura Kabiru cikin gida ya ce, "Wuce ciki bana son maganar." Sannan ya juya wurin Al'amin ya furta, "Don Allah ka yi haƙuri Al'amin." A kunyace Al'amin ya furta, "Ba komai Daddy ammm... Dama..." Sai kuma kunya ta kama shi ya kasa magana ya furta, "Shi kenan sai da safe Daddy."
Littafin kuɗi ne 300 idan kina buƙata ki min mgn 0706 206 2624
52
🔚🔚🔚🔚🔚🔚
Al'amin na tafe a mota lokaci-lokaci yake sakin tsaki don ya fahimci wani abu a tattare da Kabiru, ya hango kishi ƙarara a ƙwayar idonsa. Babban tashin hankalinsa da ya rasa ta yaya zai samu lambar Raihan balle ya sake bata haƙuri ya nemi soyayyarta. Gashi ya yi juyin duniya akan Malam ya yi wa Daddy magana fir ya ƙi yadda, ya kawo ido ya zura masa don ya ce sai dai ya nemi soyayyarta.
Daddy na shiga cikin gida ya samu Raihan a falo tana lissafin wasu kaya da ta yi order su. Zama ya yi a kujera ta kalle shi da murmushi ta ce, "Daddy barka da shigowa." Daddy ya amsa cikin sakin fuska sannan ya ce, "Raihan ashe Al'amin ya zo." Nan take ta haɗe fuska ta ce, "Ya zo Daddy amma ban fita saboda a yanzu ba na son abin da zai sake dagula lissafin rayuwata." Daddy ya yi murmushin irin nasu na manya ya ce, "Amma da kin saurare shi ki ji abin da yake tafe da shi." Raihan ta tura baki gaba ta ce, "Ai duk abin da yake tafe da shi na yafe masa ya riƙe kayansa Daddy." Dariya Daddy ya yi ya ce, "Shi kenan Raihan ɗin Daddy ba zan yi miki dole ba duk abin da kike so haka za a yi, amma fa kar ki manta aure sunnar Annabi ne." Raihan ta yi murmushi tana cewa, "Daddy ni fa ba komai nace ba amma gaskiya ni da aure kam sai nan da wasu shekaru." Daddy ya nufi hanyar part ɗin sa yana faɗin, "Shi kenan Allah ya nuna mana lokaci." Raihan ta amsa da Amin sannan ta ci gaba da abin da take yi.