Sashe 81
Zaujatu Jinnul Ashiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk yadda Likitoci suka kai ga ƙoƙarinsu abin ya ci tura, suna nan kan Raihan Mommy da Daddy na daga gefe suna yi mata tofi cikin ikon Allah aka samu jijiya aka saka mata jini, haka aman da yake fita ta hancinta shi ma ya tsagaita. Malam da kansa ya ƙarasa bakin gadon ya yi bismillah ya fara karanta addu'o'i yana tofa mata, sai da ya jima akanta sannan ya miƙa wa Mommy jarkar hannunsa ya ce ta yi bismillah ta shafa mata a jiki kuma ta samu ko yaya ne ta ɗiga mata a bakinta. Kabiru yana daga gefe bayan ya kammala tofin ya ciro wata ƙaramar kwalbar man zaitun da habbatussauda ya tsiyaya a ciki sannan ya ƙarasa bakin gadon Raihan, ganin haka ya sa likitocin suka fara faɗa don a cewarsu ana ɓata musu aiki tun da sun fara kamo bakin zaren. Kabiru bai bi ta kansu ba sai da ya gama yi mata addu'a sannan shi ma ya miƙa wa Mommy ya ce ta shafa mata a hafin ƙafarta da tafin hannunta sai fuskarta, a zuba ɗan kaɗan a tsiyaya a kunnenta da tsakiyar kanta. Da ƙyar likitoci suka bari Mommy ta shafawa Raihan waɗannan tofin, tana gama shafa mata jikinta ya fara fitar da gumi sai kuma ta fara rawar ɗari kamar mai jin sanyi. A hankali ta buɗe idanunta da suka shanye tana bin mutanen wurin da kallon, A fili su Mommy suka furta Alhamdulillah Kabiru ya ɗaga hannu sama yana gode wa Allah. Da taimakon Allah da taimakon litocin suka samu Raihan ta dawo hayyacinta, nan take suka yi mata allurar bacci Nurses ɗin da suke da duty a lokacin suka zo suka fara gyara wurin. Tun daga ranar wani abu bai sake faruwa da Raihan ba saboda kullin akwai tofin da Malam yake yi mata ana bata, haka shi ma Kabiru duk dare sai ya biyo daga Kamfani ya yi mata tofi da addu'o'i sannan ya wuce gida. Malam da Al'amin kusan kullin sai sun je asibiti duba Raihan saboda har lokacin Malam bai sanar masa da komai ba, haka Mai ɗakin Malam ita ma zuwanta uku daga haka suka yi sabo da Mommy sosai saboda Mahaifiyar Al'amin macece mai kirkin gaske, idan za ta zo har girki take yi wa su Mommy wannan karamcin ya ƙara wa Malam da iyalansa matsayi a wurin su Mommy. Raihan ta warke sosai tana cin abincinta kuma duk wani abu da yake damunta ya yi sauƙi, don haka likitoci suka sallame su. A ranar da aka sallami su Raihan da dare Kabiru bayan ya gabatar da sallar Isha'i yana shirin kwanciya ya ji kamar ana bubbuga ƙofar ɗakinsa, mamaki ne ya kama shi don bai taɓa samun haka daga masu gidan ba saboda ko abu Daddy zai saka shi sai asuba yake yi masa maganar idan ya fito sallar asuba. A hankali ya ƙarasa ya buɗe ƙofar amma babu kowa a wurin, komawa ya yi ya kwanta har bacci ya fara ɗaukansa. Ta jikin windonsa ya ji haushin kare ya ƙi ci ya ƙi cinye wa. Haska fitila ya yi a hankali yana kallon windon daga kwance, guntun tsaki ya yi ya koma ya kwanta yana nan kwance yana saƙa da warwara bacci ya yi awon gaba da shi. Cikin baccinsa yake jiyo kukan mage kamar a saitin kansa, firgigit ya motsa saboda ko kaɗan baya ƙaunar mage. A guje ya ga ta ɗare kan windon ɗakinsa tana zaro masa idanu, baƙa ce wuluk sai hasken idanunta da yake gani. Rigarsa da ya cire ya ɗauka yana korarsa don ya lura Muzuru ne amma ko gezau, kamar almara ya ji ya furta: "Saƙo na kawo maka kafin na cika aiki." Wata farar takarda ce ta faɗo, sai kuma ya nemi magen ya rasa. Wata zuciyar har ta hana shi ɗauka sai kuma ya yi bismillah ya ɗauka ya fara karanta rubutun da aka yi da ajami kamar haka: "Ina ƙara jan kunnenka akan ka fita hanyar Raihan ka ƙi, ka tsaya matsayinka amma sai cusa kanka kake wallahi sai na nuna maka iyakarka, idan har Raihan kake so sai na damalmala rayuwarka ta yadda ko wata macen ka gani ba za ka yi sha'awar kallonta ba balle ka ji ɗigon santa a zuciyarka. Ba dai matarka ciki gare ta ba, wallahi ka saurari saƙona yana tafe nan ba da jimawa ba. Mai HUZAIFA mijin Raihan har abada." Kabiru na gama karanta wa ya fahimci wanda ya aiko da saƙon, ƙirjinsa ne ya buga musamman da ya ji ya ambato Maryama da ke ɗauke da tsohon ciki don yana tsoron kar ya cutar masa da ita, hannunsa har rawa yake ya lalubo wayarsa ya kira lambarta amma yana kira ya ji a kashe take. A hankali ya miƙe ya faɗa banɗaki ya ɗauro alwala ya shiga gabatar da sallah yana kai wa Allah kukansa akan ya shiga tsakaninsu da sharrin Huzaifa da dukkan wani abin ƙi, baccin da bai koma kenan ba a ɓangare ɗaya kuma ya shiga tunanin wanda Raihan take yi wa tsananin soyayyar da har ciwon zuciya yake barzanar kamata. Tausayin kansa ne ya kama shi don ya san zuciyarsa bata yi masa hallaci ba da ta faɗa ƙaunar Raihan, don ya san dama ba tsararsa ba ce domin ya kwana da sanin hanyar jirgi daban da ta mota. Ba shi ya koma bacci ba sai gabanin asuba har so ya yi ya makara, don ma ranar babu aiki kasancewar juma'a ce. Kuma tun daga juma'a Daddy yake bada hutun ƙarshen mako har zuwa ranar Lahadi.
A razane Al'amin ya ɗago ya dubi Mahaifinsa baki na rawa ya ce, "Daddy ban fahimci abin da kake nufi ba fa." Malam ya sake ɗaure fuska ya ce, "Abin da ka ji na faɗa da farko shi za ka sake tarayo wa ka saurara, yarinyar nan saboda kai har tana neman salwantar da rayuwarta. Yanzu Aminu aibu ne don an ɗaura maka aure da mata biyu a rana ɗaya, na ga kowacce da halinta za ta zauna kuma kowaccensu tana ƙaunarka. A da na ce sai bayan aurenka da sati guda amma ina ganin babu fa'idar ɗagawa gara a ɗaura rana ɗaya, idan ya so ko bayan sati ɗaya da bikin ne sai ita Raihan ta tare tun nasan ba lalle sun gama shiri ba." Al'amin ya ɓata fuska kamar zai yi kuka murya na rawa ya ce, "Kuma yanzu yaro da ji a riƙa cewa matana biyu, wannan wanne irin abu ne Daddy." Mama na daga gefe ta karɓe zancen da cewar, "Al'amin wanda ya ce ya sonka ya fi wanda baya sonka, menene aibun yarinyar nan ba sai ka gaya wa Sumayya halin da ake ciki ba ka yi mata bayani." Al'amin ya miƙe murya a ciki ya ce, "Shi kenan ba komai." Daɗi ne ya kama su Malam suka shiga saka masa albarka, saboda dama sun san Al'amin ba zai ƙi Aurenta ya bujire musu ba. Yana shiga ɗaki ya fara zarya don bai san ta inda zai fara gaya wa Sumayya ba saboda ya san kishinta, yana cikin wannan tunanin ya ji muryar Daddy yana waya da Mahaifinta. Kamar wanda ruwa ya cinye haka Al'amin ya yi sak jikinsa tamkar an zare masa lasa, kasa motsa wa ya yi yana jin abin kamar a mafarki, a hankali ya ja ƙafarsa ya hau kan katifarsa daga haka bai sake fahimtar abin da Daddy yake faɗa ba ya zurfafa cikin tunani. Mahaifin Sumayya bai ji komai ba hasalima shi da kansa ya ce zai sanar wa da Summaya halin da ake ciki don ta yi wa Al'amin kyakkyawar fahimta. Malam ya ji daɗi ƙwarai da fahimtarsa da Mahaifin Sumayya ya yi, hira suka taɓa dangane da harkar bikin sannan suka yi sallama.
Lokacin da Mahaifiyar Sumayya ta samu labarin tsalle ta yi ta dire ta ce sam bata lamun ce ba, sai da Mahaifin Sumayya ya yi mata ba daɗi sannan ta sauko. Ita kuwa Sumayya yana gaya mata ta fashe da kuka haɗe da shiga ɗaki da gudu, tana zuwa wayarta ta ɗauka ta kira lambar Al'amin sai da ta katse tana shirin kira ta ga ya kirata. Cikin kuka ta furta, "Hubby da gaske ne abin da Daddy ya gaya min wai mu biyu za ka aura? Shi kenan ka daina sona ko?" Al'amin shuru ya yi yana jin kukanta har cikin zuciyarsa, tattaro jarumta ya yi ya ce, "Don Allah ki fahimce ni Dear kin san ina ƙaunarki kuma na tabbata za ki yi min adalci, idan kika ce na daina son ki kamar ba ki yi min adalci ba. Ina son ki ina ƙaunar ki kuma ba zan taɓa haɗa ƙaunarki da kowa ba, don Allah ki kwantar da hankalinki kin san komai muƙƙaddari ne daga Ubangiji." Hawaye ta goge sannan ta furta, "Amma me ya sa ba za ta nemi mijinta ba sai mijina, Hubby har yanzu zuciyata rawa take yi akan yarinyar nan gani nake kamar kana ƙaunarta, idan ba haka ba ya za a yi maganar aure lokaci ɗaya ta kankama kai da ita." Al'amin dafe kansa ya yi don duk yadda ya so nusar da Sumayya sam taƙi fahimtarsa idonta ya riga ya rufe, daga ƙarshe ma katse wayar ta yi tana kuka ya yi kiran duniya ta ƙi ɗauka. Sai dai ko kaɗan bai ji haushinta ba saboda ya san zafin kishi irin na Sumayya kuma kowacce macce aka yi wa haka abin da za ta yi kenan, lokaci ɗaya ya ji haushin Raihan ya kama shi don ita yake ganin ta zame masa linzamin da ta ja dokin rayuwarsu faɗa wa cikin matsala tsamo-tsamo.
Tarihinsu Al'amin.
A razane Al'amin ya ɗago ya dubi Mahaifinsa baki na rawa ya ce, "Daddy ban fahimci abin da kake nufi ba fa." Malam ya sake ɗaure fuska ya ce, "Abin da ka ji na faɗa da farko shi za ka sake tarayo wa ka saurara, yarinyar nan saboda kai har tana neman salwantar da rayuwarta. Yanzu Aminu aibu ne don an ɗaura maka aure da mata biyu a rana ɗaya, na ga kowacce da halinta za ta zauna kuma kowaccensu tana ƙaunarka. A da na ce sai bayan aurenka da sati guda amma ina ganin babu fa'idar ɗagawa gara a ɗaura rana ɗaya, idan ya so ko bayan sati ɗaya da bikin ne sai ita Raihan ta tare tun nasan ba lalle sun gama shiri ba." Al'amin ya ɓata fuska kamar zai yi kuka murya na rawa ya ce, "Kuma yanzu yaro da ji a riƙa cewa matana biyu, wannan wanne irin abu ne Daddy." Mama na daga gefe ta karɓe zancen da cewar, "Al'amin wanda ya ce ya sonka ya fi wanda baya sonka, menene aibun yarinyar nan ba sai ka gaya wa Sumayya halin da ake ciki ba ka yi mata bayani." Al'amin ya miƙe murya a ciki ya ce, "Shi kenan ba komai." Daɗi ne ya kama su Malam suka shiga saka masa albarka, saboda dama sun san Al'amin ba zai ƙi Aurenta ya bujire musu ba. Yana shiga ɗaki ya fara zarya don bai san ta inda zai fara gaya wa Sumayya ba saboda ya san kishinta, yana cikin wannan tunanin ya ji muryar Daddy yana waya da Mahaifinta. Kamar wanda ruwa ya cinye haka Al'amin ya yi sak jikinsa tamkar an zare masa lasa, kasa motsa wa ya yi yana jin abin kamar a mafarki, a hankali ya ja ƙafarsa ya hau kan katifarsa daga haka bai sake fahimtar abin da Daddy yake faɗa ba ya zurfafa cikin tunani. Mahaifin Sumayya bai ji komai ba hasalima shi da kansa ya ce zai sanar wa da Summaya halin da ake ciki don ta yi wa Al'amin kyakkyawar fahimta. Malam ya ji daɗi ƙwarai da fahimtarsa da Mahaifin Sumayya ya yi, hira suka taɓa dangane da harkar bikin sannan suka yi sallama.
Lokacin da Mahaifiyar Sumayya ta samu labarin tsalle ta yi ta dire ta ce sam bata lamun ce ba, sai da Mahaifin Sumayya ya yi mata ba daɗi sannan ta sauko. Ita kuwa Sumayya yana gaya mata ta fashe da kuka haɗe da shiga ɗaki da gudu, tana zuwa wayarta ta ɗauka ta kira lambar Al'amin sai da ta katse tana shirin kira ta ga ya kirata. Cikin kuka ta furta, "Hubby da gaske ne abin da Daddy ya gaya min wai mu biyu za ka aura? Shi kenan ka daina sona ko?" Al'amin shuru ya yi yana jin kukanta har cikin zuciyarsa, tattaro jarumta ya yi ya ce, "Don Allah ki fahimce ni Dear kin san ina ƙaunarki kuma na tabbata za ki yi min adalci, idan kika ce na daina son ki kamar ba ki yi min adalci ba. Ina son ki ina ƙaunar ki kuma ba zan taɓa haɗa ƙaunarki da kowa ba, don Allah ki kwantar da hankalinki kin san komai muƙƙaddari ne daga Ubangiji." Hawaye ta goge sannan ta furta, "Amma me ya sa ba za ta nemi mijinta ba sai mijina, Hubby har yanzu zuciyata rawa take yi akan yarinyar nan gani nake kamar kana ƙaunarta, idan ba haka ba ya za a yi maganar aure lokaci ɗaya ta kankama kai da ita." Al'amin dafe kansa ya yi don duk yadda ya so nusar da Sumayya sam taƙi fahimtarsa idonta ya riga ya rufe, daga ƙarshe ma katse wayar ta yi tana kuka ya yi kiran duniya ta ƙi ɗauka. Sai dai ko kaɗan bai ji haushinta ba saboda ya san zafin kishi irin na Sumayya kuma kowacce macce aka yi wa haka abin da za ta yi kenan, lokaci ɗaya ya ji haushin Raihan ya kama shi don ita yake ganin ta zame masa linzamin da ta ja dokin rayuwarsu faɗa wa cikin matsala tsamo-tsamo.
Tarihinsu Al'amin.