Sashe 85
Zaujatu Jinnul Ashiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Tana shiga kitchen É—inta babu abin da babu don haka kai tsaye ruwan tea ta fara dafa musu ta zuba a flask, sannan ta fere dankali ta soya musu sai kuma ta soya Æ™wai daban don ta so soya kayan miya ko miyar jajjage ta yi musu, bayan ta haÉ—a komai tunani ta fara yi a wurin da za ta ajiye musu abinci. Nata ta haÉ—a daban sannan ta haÉ—a musu na su a tire ta saka komai ta É—auka ta nufi É—akin Sumayya. Da sallama ta shiga a lokacin tuni Sumayya ta shirya cikin Æ™ananan kaya riga da wando, kanta a Æ™asa ta shiga da shi ta jiye musu sannan ta koma ta É—auki nata ta wuce Main falonsu ta zauna tana karyawa. Ƙarar turo Æ™afa ta ji tana kai idonta ta ga Al'amin É—auke da tiren ya fito da shi ya kawo falon da take zaune, da ido ta bishi har ya koma ya riÆ™o hannun Sumayya suka dawo cikin falon. Tana zaune ta ci gaba da cin abincinta kamar ma bata gansu ba haka ta É—auke kanta sai dai gabaÉ—aya ta daina jin daÉ—in abincin, turawa kawai take yi don kar su fahimci halin da take ciki. Akan idonta suka riÆ™a ciyar da juna cikin shauÆ™in so da Æ™auna, suna gamawa Al'amin ya kwashe kayan ya kai su kitchen. Dawo wa ya yi ya zauna Sumayya ta kwantar da kanta a jikinsa cikin shagwaÉ“a ta furta, "Darling don Allah ka roÆ™i alfarmar Aunty Raihan ta taimaka t gyara mana É—aki wallahi zan ji kunya idan baÆ™in gidanmu suka zo, ka ga a gabanka Mami ta kira ni wai baÆ™i za su zo ganin É—aki." Jim Al'amin ya yi yana ganin kamar saka Raihan gyran É—akin baccinsu bai dace ba, kamar ta san abin da yake nazari ta tashi zaune tana marairaice murya ta ce, "Wallahi ko yatsana da Æ™yar nake iya É—agawa, ka ga ita ma lokacin da za ka koma É—akinta duk abin da ya dace na gida ai ni zan yi. Amma ka yi haÆ™uri idan baka so haka ba." Ta Æ™arasa maganar tana kwanciya a jikin kujera. MiÆ™e wa ya yi cike da jin daÉ—i don gani yake kamar Sumayya ta sauko don su haÉ—a kansu da Raihan ne ya nufi É—akin Raihan yana faÉ—in, "Menene amfanin zaman tare My baby? Bari na yi mata magana." Tura Æ™ofar É—akin ya yi a lokacij Raihan na waya da Inno don ta yi kewarsu, tsaye ya yi yana kallonta babu laifi tana da kyau daidai gwargwado gata da gashi irin na fulani har baya. Yana son mace mai tsayin gashi duk da Raihan ba fara ba ce kuma bata da wani jiki amma bata da muni a fuska, tana gama waya ta juyo tana kallonsa. ÆŠauke kai ya yi kamar bai ganta ba sannan ya ce, "Am dama cewa na yi ki É—an gyarawa Sumayya É—aki ba za ta iya ba." Æata fuska ta yi har bata san lokacin da ra furta, "Gyaran É—aki?" GyaÉ—a mata kai ya yi ya ce, "Eh saboda baÆ™i za su zo ita kuma kin ga yadda jikin nata yake." Raihan bata tanka masa ba zuciyarta na suya ta wuce ta nufi É—akin Sumayya don ta manta ko É—ankwalinta bata saka balle hijabi. Daga iya sai doguwar rigar leshi, kayan ba Æ™aramin kyau suka yi mata ba. Sumayya na ganin Raihan sai da gabanta ya faÉ—i, saboda koda ta san Raihan bata fita kyau ba amma babu wanda zai kalli Raihan bai ce ta yi masa kyau ba. Kai tsaye É—akin ta shiga ta fara kaÉ—e gadon cikin takaici, kayan Raihan duk a warwatse har da Æ™ananan kayanta na ciki. Sai da ta kwashe su da cusa mata a drower sannan ta gyara gadon ta mayar da komai yadda yake ta wuce É—akinta. Hankalin Sumayya bai kwanta ba sai da ta ga Raihan ta shiga É—aki, amma abin da ya É“ata ranta yadda ta lura da irin satar kallon da Al'amin yake yi wa kan Raihan. Idan ka kalli Sumayya tashin farko za ka fahimci ta fi Raihan kyau sai dai Raihan ta nuna mata dirin jiki da tsayin gashi domin Sumayya fara ce kyakkyawa, ita ma doguwa ce amma tafi faÉ—i daga sama. Shigar Raihan É—aki babu wuya suka ji bugun gida, ta window Raihan take kallon hanya Al'amin na buÉ—e wa ta hango su Mama Hafsa da sauran baÆ™in da ba su gano É—aki ba. Mamaki ne ya kama ta ganin yadda Al'amin yake gaida su cikin mutumci fa girmamawa yana sunne kai Æ™asa, suna shigo wa da sauri ta É—ane Mama Hafsa tana murna. Ita ma rungumeta ta yi cikin farinciki don ta ji daÉ—in ganin Ƴar Æ´ar'uwarta cikin Æ™oshin lafiya, sai a lokacin ta baje musu kajin da Al'amin ya kawo mata, kaÉ—an suka yi suka saka mata sauran a firji. Babu Æ™ofa É—aya da Raihan ta buÉ—e musu da take nuna tana cikin damuwa don haka sai santin É—akinta suke yi, sai da suka leÆ™a sashen Sumayya suka gaisa ta amsa musu cikin mutumci sai yabon sauÆ™in kanta suke Raihan ban da murmushi babu abin da take yi, daga Æ™arshe suka koma É—akin Raihan suka yi mata nasiha mai ratsa jiki, akan ladabi da biyayya sai juriya da haÆ™uri. Sun yi mata nasiha sosai akan yadda za ta kula da mijinta ta É“angaren kissa da tarairaya Mama Hafsa na gaya mata har kunya take ji, ba su wani daÉ—e a gidan ba suka yi mata sallama suka tafi. Lokacin da za su tafi har da Æ™wallarta ta raka su bakin gate tana É—aga musu hannu, É—akinta ta koma ta É—auki waya ta kira wayar mommy. Sun jima suna hira da mommy duk a game da baÆ™i ne da sauran Æ´an biki, bayan sun gama ta kira Daddy cikin farinciki ya amsa mata bayan sun gaisa suka taÉ“a hira sannan suka yi sallama.