Sashe 75
Zaujatu Jinnul Ashiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Raihan ta warware raunukan jikinta duk sun warke, kuma tun da Kabiru ya samu labarin dawowar Raihan kusan kullin sai ya kira wayar mommy ya ce a bawa Raihan zai dubata. Mommy har mamakin wannan kulawar da Kabiru yake bawa Raihan yake yi amma da ta tuna irim ɗawainiyar da Daddy yake yi masa sai take ganin kamar saka alheri da alheri ne Kabiru yake yi kuma hakan ba ƙaramin faranta ransu yake yi ba. Su Baba faɗa suka yi wa Huzafa sosai game da abubuwam da yake aikawata, ya yi nadama sosai don haka ya ji aikinma gabaɗaya ya fice masa da kai. Sai da Abokan aikinsa suka ƙarfafi gwiwarsa sannan ya koma bakin aiki, kuma kafin tafiyarsa sai da aka ɗaura masa aure wara cousine sister ɗinsa da sakamakon dama ya jima yana son ya yi mata magana tun a lokacin gaya, amma sai a wannan lokacin Allah ya yi don haka ba a ɗauki lokaci ba dudu wata uku aka tsayar lokaci na cika aka ɗaura musu aure ya tafi da matarsa. A wannan lokacin tuni Kabiru ya dawo garin Kano sai dai a lokacin da zai baro garinsu Matarsa na ɗauke da cikin wata biyar don har ya fara fitowa, a da baya jin komai game da Maryama amma ɗan zaman da ya yi lokacin rasuwar Mahaifinsa ya ƙara musu shaƙuwa tsakaninsa da ita, sosai ya riƙa jin kewar matarsa lokacin da zai taho sannan ga wani irin ƙaunarta da yake ji ita da abin da yake cikinta. Tun bayan da komawar Raihan gida Daddy ya samu Malamai game da auren Raihan da aka ɗaura, nan take suka nusar da shi auren Raihan babu shi domin an yi shi ne a cikin rashin sani hasalima ba shi ne ainihin mai wannan siffar ba kuma ba jinsinta ba ne. Don haka babu wurin da aka halatta aure tsakanin jinsin mutum da aljani, da farko iyayen Huzaifa sun so a tambayi Raihan ko za ta amince ta auri wannan Huzaifan idan ya so sai a ɗaura musu aure. Daddy ne ya dakatar da maganar a take don cewa ya yi ko Raihan ɗin ba zai gaya mata ba, saboda ba za ta iya rayuwa da Huzaifa saboda a kodayaushe ta gan shi zai riƙa tuna mata da wancen. Tun da ko daga baya ita kaɗai idan ta dubi hotunan bikinsu sai ta riƙa ganin suna yi mata gizo, har ta kai ga hotunan kamar sun fara tsorata. Ba shiri ta ware rana ɗaya ta ƙone su gabaɗaya, waɗanda suke cikin wayarta da na Mommy suma duka aka gone. Rahan haka ta ci gana da kasuwancinta gwanin birgewa saboda da farko ne ta saka wa ranta damuwa amma daga baya duk ta watsar ta fauwala wa Allah lamuranta. Sai dai babbaj abin da ya fi nuƙurƙusar zuciyarta bai wuce tunanin Al'amin da take kwana take tashi da shi ba, tun tana iya danne wa har ta samu Mommy da maganar don a lokacin ba ta da aiki sai na mafarkinsa da tunanin suna gudanar da rayuwa cikin farinciki da annushuwa. Wannan tunane-tunane ne ya sake rura wutar da ke cikin zuciyar Raihan, ba a ɗauki lokaci ba ta zabge ta rame ita kaɗai ta rasa abin da yake damunta. Ga shi tana fargabar tarar Mommy ta gaya mata don bata san yadda za ta ɗauki maganar ba, watarana tana zaune da tunanin Al'amin ya addabi rayuwarta miƙe wa ta yi ta ɗauki key ɗin motarta. Tun bayan bikinta da Huzaifa ba ta sake fita ira kaɗai ba sai ranar, Inno na ganinta da mukullin mota ta ƙanƙance ido tana sannan ta ce, "Raihanu ni kam wannan makullin gidan abinci ne?" Raihan ta ɗago shi ta nuna wa Inno sannan ta ce, "Mukullin motata ce fita zan yi." Da sauri Inno ta zaro ido waje ta furta, "Fita ina ban gane ba." Tura baki gaba Raihan ta yi, ta yi ƙasa da murya ta ce, "Idan na je na dawo kya gane." Da sauri Inno ta ta shi ta tare bakin ƙofar tana kiran Mommy, nan take ta ƙaraso tana tambayar ko wani abu ne ya faru. Inno ta nuna Raihan ta ce, "Gata nan wai fita za ta yi, wallahi ki shaida Zainabu idan waccen hatsabibin ya sake ɗauke ta ko ƙyallin hawaye ba za ki gani a idona ba." Mommy na shirin yin magana Goggo ta ce, "Wallahi balle bikin ƴar gidan Safare gare ni ko ƙarƙashin kukar Bulukiya ya kai ki babu abin da zai hana ni tafiya Albasu biki." Mommy ta dubi Raihan ta ce, "Ina za ki je?" Idanun Raihan suka ciko da ƙwallah kafin mommy ta yi aune sai ga hawaye na zuba." Baki suka riƙe gabaɗaya suna kallonta, Goggo ta tafa hannuwa cike da takaici ta ce, "Raihane kin ji kunya gwandamemiya kamar ke kina wannan sakarcin daga tambaya." Raihan kukan da take yi fargabarta kar ta hana ta fita don haka ta tattaro jarumanta ta goge hawayen ta ce, "Mommy shop zani fa komai na maka up ɗina ya ƙare." Mommy jim ta yi sannan ta ce, "Ba na son ki riƙa fita ke ɗaya Raihan gaskiya ki kira Daddy idan ya ce ki fita shi kenan." A nan take Raihan ta kira Daddy ta sanar da shi da farko bai amince ba sai daga baya. Raiham kamar za ta yi tsalle ta tashi sama saboda sauri, don lokacin da ta fita mommy har kallonta ta yi tana mamakin saurin da take yi. Amma da yake ba fita take ba, sai ta yi tunanin ko ɗokin fita ne take yi.
Sai da ta fara zuwa store ta siyo kaya shafe-shafe sannan ta ɗauko hanyar Waraka Islamic store, tana parking ƙirjinta ya buga sakamakon hango shi da ta yi a barandar asibitin. Ajiyar ta sauke a hankali ta furta, "Allah ka cika mij burina wanda yake alkairi a gare ni." Cikin shauƙin so ta nufi wurin da yake zaune a kan kujera, tana ƙarasawa ta ɗan yi gyaran murya sannan ta yi sallama sakamakon ta same shi yana yin waya. Sai da ya ɗago ya kalleta sannan ya gyaɗa mata kai ya furta, "Ok Ur hightness i wll call you later..." Daga can ɓangaren aka katse shi da cewar, "Baby ba dai wata beb ɗin ka yi ba?" Lumshe ido ya yi sannan ya furta, "No wara patient ce da Daddy bawa magani." Amsa ta bashi sannan ya furta, "Na yi kewarki dear yaushe za ku kawo ne, gaskiya zan biyo ki garin Dutsen nan."
Afwan ban tace shi i ba.
Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 0706 206 2624
41
Sai da ta fara zuwa store ta siyo kaya shafe-shafe sannan ta ɗauko hanyar Waraka Islamic store, tana parking ƙirjinta ya buga sakamakon hango shi da ta yi a barandar asibitin. Ajiyar ta sauke a hankali ta furta, "Allah ka cika mij burina wanda yake alkairi a gare ni." Cikin shauƙin so ta nufi wurin da yake zaune a kan kujera, tana ƙarasawa ta ɗan yi gyaran murya sannan ta yi sallama sakamakon ta same shi yana yin waya. Sai da ya ɗago ya kalleta sannan ya gyaɗa mata kai ya furta, "Ok Ur hightness i wll call you later..." Daga can ɓangaren aka katse shi da cewar, "Baby ba dai wata beb ɗin ka yi ba?" Lumshe ido ya yi sannan ya furta, "No wara patient ce da Daddy bawa magani." Amsa ta bashi sannan ya furta, "Na yi kewarki dear yaushe za ku kawo ne, gaskiya zan biyo ki garin Dutsen nan."
Afwan ban tace shi i ba.
Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 0706 206 2624
41