← Book details Zaujatu Jinnul Ashiq Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 110

Sashe 35

Zaujatu Jinnul Ashiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Malam babu ruwanka da ni, karka shiga hurumin da ba naka na, wallahi ba zan rabu da ita ba saboda matata ce na aureta halak-malak na biya sadakinta me ya yi saura." Malam Usman ya matsa gaban Raihan yana faɗin, "A ina ka taɓa jin aljani ya auri bil'adam? Nan ba wurin zamanka ba ne tun wuri ka kama gabanka." Raihan ta fara takowa cikin isa da ƙasaita ta ce, "Malam Ina ganin mutumcinka tun wuri ka kama gabanka don ko sama da ƙasa za ta haɗe ba zan fita daga jikinta ba. Ni Huzafa na auri Raihan sama da shekara goma sha ta haifa min ƴaƴa, na santa farin sani na yi mu'amala da ita har ta fi matata ta jinsina gamsar da ni. Na shafe tsahon shekaru ina rainon abata, yanzu haka ina hanyata ta zuwa neman warakarta Mar'usa ta sanar da ni halin da ake ciki, kana ganin duk wannan wahalar da na yi za ta tashi a banza ne? Mahaifinta shi ya damƙamin ita shi da kansa ya bani aurenta akan me rana tsaka za ka zo ka nemi raba ni da matata." Lokaci ɗaya jikin Daddy ya hau tsuma baki na rawa ya furta, "Ni...Kuma? Yaushe na sanka da har na baka auren Raihan?" A zabure Raihan ta nuno Daddy tana cewa, "Ƙarya kake munafuki ni za ka ƙaryata a gaban jama'a? Na fi ƙarfin ka ƙaryata ni kuma ina ɗaga maka ƙafa ne saboda kana nunawa matata kulawa, baka cika saka mata ido ba kamar mahaifiyarta. Kun ga wannan." Raihan ta nuna Mommy sannan ta ci gaba da cewa, "Ta yi bala'in saka min ido kuma ba tun yau na so halakata ba don dai tana da yawan ibada, ta matsawa Matata Raihan kuma ga shi ita ce sanadiyyar bankaɗo sirrina." Malam Usman ya jinjina kai ya kallai Raihan ya ce, "Ba na son ƙarya don na san akwai maƙaryata da yawa a cikinku, ya aka yi Mahaifinta ya baka aurenta kana tunanin akwai uban da zai damƙa auren ƴarsa a hannun aljani ne?" Tuno idanun Mommy suka kawo ruwa ta kalli Daddy cikin kuka ta ce, "Dama ashe soyayyar da kake yi wa Raihan bata kai zuci ba, wanne abu kake aikawata a ɓoye da har za ka damƙawa aljani auren ƴata?" Daddy zai yi magana Malam Usman ya dakatar da shi da cewar, "Huzaifa kake ko wa? Na ji sunanka da alama kai musulmi ne to da farko zan haɗa ka da girman Allah ka fice daga jikin yarinyar nan ko za ka samu salama a wurina, matuƙar ka nuna min taurin kai sai na ƙoneka ƙurmus." Raihan ta koma jikin bango ta zauna sannan ta ce, "Malam ka bar haɗa ni da musulunci don ni ba Musulmi ba ne, ba don kar in watsawa Mahaifiyata ƙasa a ido ba da sai na ce hanyar da musulunci take ban biyota ba. Mahaifiyata da danginta Musulmai ne, mahaifina da danginsa duka kafirai ne. Zan yi maka magana ta ƙarshe, ba zan taɓa fita daga jikin Raihan ba, duk abin da za ka min sai dai ka yi amma zama a jikinta yanzu na fara domin yanzu ta zama cikakkiyar budurwa, na raineta tun bata zama wani abu ba sai da na fara ɗanɗana zumarta za ka ce na fita? Ɗan da muka haifa waye zai ci gaba da shayar da shi?" Malam Usman ya jinjina kai a fili ya ce, "Tabbas za mu kai ruwa rana da shi domin wannan yana cikin masu taurin kai." Nan take Malam Usman ya yi A'uziyya ya fara karanta surartul Baƙara, Malam Ya jima yana karatu amma Huzaifa ya yi shiru sai da ya ji azaba ta ishe shi ya ƙwalla wata irin razananniyar ƙara.

Inno na daga ƙofar ɗakin Kabiru ya saki dariyar farinciki ta ce, "Allah mai mutane da yawa, kai jama'a Allah na dawo Zinaru kin ji yadda Malam yake fata-fata da aljanin nan da ayar Allah?" Goggo ta sake baza kunne sannan ta ce, "Wuya mai sa Waziri shiga wandon Sarki ki ce da na tafi Albasu da na bar kallo."

Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ki min mgn 0706 206 2624

18

Kabiru yana daga ɗaki yana jin su Inno da har ya yi niyyar ya yi musu shiru sai ya ziro da kai yana faɗin, "Inno kar dai ku manta da ambaton Allah, don idan kuka yi sake ana cirewa daga jikinta za su iya faɗowa kanku." Inno tuni ta yi wuri-wuri ta ɗebi salati tana watsa wa Kabiru daƙuwa haɗe da cewa, "Gidanku ka ji ɗan nan, yoo ni me aljani zai yi da ni fata ta saki gijibgi duk ya sauko, kwarankwatsa ko da ina budurwa sai dai ya ganni ya ƙyale?" Goggo ta kalli Inno ta ce, "A'a bar faɗin haka wallahi tsaf za ki yi kyau da su ke dai mu roƙi Allah ya raba mu da su amma Aljanu suka haye mu na san Audullahi tarkata mu zai yi ya wuce Albasu da mu." Inno kamar mai nazari haka ta yi jigum cikin tsiro don har lokacin bata daina hango kammanin kofaton Mama Uwani a ƙafarta ba.

Malam Usman karatu ya ci gaba da yi babu ƙyaƙƙyautawa don ya san dama sai ya ɓullo masa ta haka za a samu mafita, sai da ya lura da Huzaifa ya yi lugub sannan ya sarara da karatun yana tambayarsa, "Za ka fita daga jikinta ko ba za ka fita ba?" A wahalce Raihan ta ɗago da kai dana sauke ajiyar zuciya ta ce, "Malam ka dakata mu yi magana da kai ta fahimta don Allah ka daina ƙonani." Malam Usman ya zauna a kan kujerar ɗakin Raihan ya ce, "Babu wata magana ta masala da za mu yi da kai da ta wuce ka amince da abin da na umarceka." Raihan ta gyara zamanta sannan ta ƙurawa Malam Usman ido cikin rashin tsoro ta ce, "Malam ka faɗi wata buƙatar taka amma ba wannan ba, don ba zan taɓa rabuwa da ita ba saboda ita ɗin mallakina ce ban taɓa ƙaunar wata hallita kamar yadda nake ƙaunarta ba. Zan iya fansar da dangina tas akan ta, amma ka daina furta kalmar rabuwa a tsakaninmu." Malam Usman kalli Malama Nafisa ya ce, "Ba ni ruwan Addu'ar nan da garin maganin nan mai haɗe da habbatais sauda." Nan take Malama Nafisa ta ciro abubuwan da Malam ya buƙata a cikin wata jaka mai ɗauke da tambarin Waraka Islamic Chemist. Malam Usman yana karɓa ya ƙarasa gaban Raihan ya yi bismillah ya fara yayyafa mata, ya miƙawa Malama Nafisa garin maganin ya ce, "Ki tabbatar da ta shaƙi wannan garin maganin." Malama Nafisa ta tunkari Raihan tana tafe tana addua, ganin ta tunkarota ya sa Raihan ta yo kanta suka fara kokawa da ƙyar ta samu ta shaƙa mata maganin. Raihan na shaƙa ta fara sakin atishawa cikin fitar hayyaci, Malam Usman ya ƙarasa kanta ya fara yayyafa mata ruwa yana ci gaba da karatu, azaba goma da ashirin ce ta sa Huzaifa a gaba. Ban da ihunsa babu abin da yake tashi a cikin ɗakin, Daddy da Mommy suna gefe suna kallon ikon Allah. Lokaci-lokaci Mommy take wurgawa Daddy mugun kallo don har lokacin maganar Huzaifa ta tsaye mata a rai da yace Daddy ne ya bashi auren Raihan. Daddy duk jikinsa ya yi sanyi duk ya yi zuru-zuru kamar wanda yake bakin bindiga, suna cikin wannan halin suka riski muryar Huzaifa yana cewa, "Dakata! Dataka Malam zan fita." Malam Usman ya tsagaita da karatun ya ce, "Za ka fita ta ina?" Huzaifa ya sauke numfashi ya ce, "Zan fita amma sai ta gama shayar min da jaririn ɗana." Ran Malam Usman ya yi mummunan ɓaci ba ɓata lokaci ya ci gaba da karatu duk yadda Huzaifa ya kaiga roƙon Malam bai saurara masa. Yana cikin karatun ya ji wata murya ta canji ta Huzaifa da yin sallama, "Assalamu alaikum." Malam Usman ya koma ya zauna sannan ya amsa, "Wa'alaikas salam da wa nake magana." Cikin nutsuwa dattijuwar ta ci gaba da cewa, "Kana magana da Malama Fatima, ni ce mahaifiyar Huzaifa." Malam Usman ya ce, "Malama Fatima me ya sa za ki katse min aikina ina shirrin hallaka ɗanki Huzaifa."

Kafin mu ji amsar Mahaifiyar Huzaif mu koma waiwaye don jin Tarihin su waye Mommy da Daddy🥱

WAIWAYE...
Chapter 35 · 0% Book details