Sashe 69
Zaujatu Jinnul Ashiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Idanunsa ne suka kaɗa jawur rai a matuƙar ɓace ta dubi Mama Hafsa ya ce, "Ba ni key." A sanyaye ta miƙa masa ya karɓa ya shiga motar ganin haka ya sa sauran matan suka fito daga cikin motar suka yi carko-carko, cikin matsanancin gudu Daddy ya fita da gudun gaske. Mama Hafsa ce ta dubi su Hajiya Lawisa ta ce, "Tsaiwa a wurin nan ba za ta kaimu ba, mu ƙarasa gida mu sanar da Aunty Zainab don wannan ba maganar da za a yi shiru ba ce." Cike da gamsu wa da bayanin Mama Hafsa suka fara takawa da ƙafa don ƙarasawa, su Hajiya Shafa da suke cikin ɗayar motar suma suka rufa musu baya. Suna shiga cikin gidan mommy ta tare su fuskarta ɗauke da fara'a tana faɗin, "Wallahi ke dai Hafsa wayarki bata da amfani sam. Na kiraki ya fina a irga amma baki ɗauka ba." Mama Hafsa bata amsa mata ba a ƙoƙarinta na danne hawayen da yake son ziraro mata, ganin yanayinsu babu walawala ya sa Mommy ta ruƙo hannun Mama Hafsa tana faɗin, "Lafiya Hafsa me yake faruwa? Me ya faru da Raihan don Allah ki gaya min." Jin haka ya karya zuciyar Mama Hafsa ta faɗa jikin mommy tana fashe wa da kuka, a madadin Mommy ta sake tambayar abin da ya faru jikinta rawa ya fara yi nan take hawaye ya fara zubo mata, ta faɗa kan kujera daɓass ta zauna sannan ta iya furta, "Idan wani abu ne ya faru don Allah ku sanar da ni." Inno da shigowarta ɗakin kenan ta dafe ƙirji da hannuwa biyu ta ce, "Kuka wane iri nake ji da kunnuwana? Me ye kuma ake kuka kamar gidan mutuwa? Huzaifan shi ma mutuwa ya yi ne?" Shiru suka yi ba tare da wani ya iya furta komai ba, Mama Hafsa ta yi ƙarfin halin zama kusa da mommy sannan ta zayyane musu duk abin da yake faruwa. Salati mutanen ɗakin suka ɗauka Inno da Goggo kuwa tuni suka fashe da kuka, Mommy na zaune a wurin da take kasa motsa wa ta yi lokaci ɗaya ta ji kanta ya sara, wata irin juya na ɗaukanta ƙirjinta na wani irin buga wa da ƙarfi, ba su yi aune ba sai gani suka yi luuuuuu ta faɗa jikin Mama Hafsa a sume. Hankali a tashe Goggo ta faɗa kan Mommy tana kuka da sauri mutane suka janye ta aka shiga yayyafa wa Mommy ruwa amma ko kaɗan bata motsa ba, da sauri Mama Hafsa da sauran mutanen wurin suka taimaka aka fita da Mommy aka saka ta a mota, ganin wannan lamarin ya ƙara tsinka zuciyar Kabiru, duk da bai san abin da ya faru ba amma jikinsa yana ba shi wani abu ne ya faru da Raihan don ko a daren da aka kaita kwana ya yi bai yi bacci ba sai gabannin asuba, kuma ko da bacci ya ɗauke shi wani irin mummunan mafarki ya yi da ita. Jikinsa har rawa yake ya ƙarasa bakin falon bayan fitar da mommy daga gidan, jin kukan su Inno ya ƙara dagula lissafinsa har ya manta da matsayinsa na mai gadi ya faɗa cikin falon hankali a tashe yana tambaya. Inno sai da ta sharce majina ta ce, "Kabiru yanzu dama yaron nan Huzaifa azzalumi ne ba mu sani ba? Wai an nemi gidan Raihane an rasa ya ɓace da ƴar mutane ɓat kamar masu layar ɓata." Ƙirjinsa ne ya buga jikinsa ya fara karkarawa a firgice ya kuma tambayar halin da ake ciki, su Inno suka yi masa bayani dalla-dalla kamar yadda Mama Hafsa ta yi musu. Kamar wanda aka zare wa laka a jiki haka ya fice daga falon ya koma ɗakinsa ya zauna, shiru ya yi ransa ba ƙaramin ɓaci ya yi ba nan take kansa ya fara juyawa lokaci-lokaci ya fara furzar da iska mai zafi.
Daddy ko da ya je ya shafe minti talatin a tsaye wayarsa ya ciro ya kira lambar Dr Hussain ko sallama bai yi masa ba ya ce, "Wallahi duk wurin da abokinka ya kai min ƴata sai ya fito min da ita, na rantse da Allah sai ya fito min da ƴata tun wuri ka gaya." Daddy bai jira cewar Dr ba ya katse wayar sannan ya kira D.P.O abokinsa ya sanar masa halin da ake ciki. Suna gama waya wayar Daddy ta fara ƙara Mama Hafsa ce a nan take sanar da shi halin da Mommy take ciki, da asibitin da suke ake bawa Mommy agajin gaggawa don har lokacin bata farfaɗo ba. Daddy bai gama jin abin da Mama Hafsa take faɗa ba ya katse wayar tare da shiga mota ya fita a guje, kafin Daddy ya ƙarasa asibitin saboda irin gudun da yake yi har sai da ya bige wani ɗan makaranta don ma Allah ya taƙaita yaron bai ji ciwo sosai ba. Yana shiga asibitin likitoci suna shiga yi masa bayanin zuciyar Mommy na gabda buga wa saboda matsananciyar damuwar da ta faɗa lokaci guda.
Raihan ba ita ta farka ba sai bayan da gari ya fara yin haske, kukan waɗansu tsuntsaye ne ya fara tashinta. A hargitse ta miƙe lokaci ɗaya ƙwaƙwalwarta ta fara hakaito mata da abin da ya faru, da sauri da fara dube-dube tana neman ta wurin da Huzaifa zai ɓullo mata sai dai babu shi babu alamarsa. Banɗakin ɗakin ta fara nema amma abin da ya bata mamaki ƙofarsa ta shafe tamkar ba a taɓa yin sa a wurin ba. Zarya ta fara yi a ɗakin tana neman ruwan da za ta yi alwala da shi, sai dai hatta ruwan jarkokin da Huzaifa ya kawo mata a daren ranar babu su ta neme su ta rasa. A hankali ta buɗe ƙofar ta fita zuwa falo, cikin sanɗanta ta fara dube-dube a cikin gidan amma sama da ƙasa da ta duba babu ruwa, kogin da ta gani a daren ranar ne ya faɗo mata da sauri ta ƙarasa wurin tana son buɗe ƙofar tsoro fal zuciyarta, ta jikin ƙofar ta leƙa amma sai gani ta yi kogin ya koma wawaken ƙaton rami. Dawowa cikin gida Raihan ta yi ta fashe da wani irin matsanancin kuka, ganin kuka ba zai kaita ba ya sa sake miƙe wa ta fita wurin ramin nan, da niyyar zura hannunta ta fara yin taimam. A ɗarare ta zura hannunta ta fara taimama tana shirin gamawa ta ji wani abu ya riƙe hannunta gam, a gefe ɗaya ga wani irin gurnani da yake tashi. Ƙara Raihan ta ƙwalla haɗe ta fisgar hannunta da ƙarfi, jini ne ya fara zuba sakamakon gefen ɗan yatsanta da wannan ƙanƙanuwar hallita ta kaiwa cizo. Jiki na rawa Raihan ta rufe ƙofa ta koma ciki, ganin jinin na zuba ya sa ta yaga ɗankwalinta ta ɗaure wurin. Zuciyarta na rawa ta gabatar da sallar asuba a lokacin tuni gari ya waye, wani abin mamaki har ta fara jin hayaniyar mutanen unguwar da yaransu. Tana nan zaune tunanin su Mommy ya faɗo mata da sauri ta ɗauki wayarta ta shiga kira amma fir ta ƙi shiga, hawaye ne yake bin kuncinta ɗaya bayan ɗaya, ga wata irin addababbiyar yunwa da take cinta kasancewar ranar ɗaurin aurenta ban da ruwan tea babu abin da ta iya sha saboda fargaba. Tana nan zaune ta ji turowar ƙofa da sauri ta matsa ta takure wuri ɗaya, Huzaifa ta ga ya shigo cikin ƙananan kaya ba ƙaramin kyau ya yi mata ba duk da tsoronsa ya riga da ya cika zuciyarta, amma da ta ƙare masa kallo sai take ganin kamar ba shi ne Huzaifan da yake son hallaka a daren jiya ba. Ƙirjinta ne ya buga da ya fara tunkarota, hannu ta ɗaga masa tana faɗin, "Don Allah ka mayar da ni gida." Murmushi ya sakar mata sannan ya tsugunna a ɗan nesa da ita ya ce, "Raihan!" Ɗagowa ta yi tana kallonsa ba tare da furta komai ba. "Kin san irin ƙaunar da nake yi miki kuwa? Ina yi miki soyayyar da ko iyayenki ba sa yi miki ita. Ni Huzaifa na rabu da kowa nawa akanki me ya sa ba za ki haƙura da su mu yi rayuwa mai ɗore wa cikin farinciki ba?" Huzaifa yana rufe baki Raihan ta fara jin alamar tsayawar motoci, waigawa Huzaifa ya yi ya saki wani shu'umin murmushi, karaf Raihan ta ji muryar su Mama Hafsa. A zabure ta miƙe ta fice falo haɗe da bankaɗe labulen window ta tura ƙofar windon da ƙarfi tana ƙwala mata kira.
Littafin kuɗi ne 300 idan kina buƙata ki min mgn 0706 206 2624
38
Daddy ko da ya je ya shafe minti talatin a tsaye wayarsa ya ciro ya kira lambar Dr Hussain ko sallama bai yi masa ba ya ce, "Wallahi duk wurin da abokinka ya kai min ƴata sai ya fito min da ita, na rantse da Allah sai ya fito min da ƴata tun wuri ka gaya." Daddy bai jira cewar Dr ba ya katse wayar sannan ya kira D.P.O abokinsa ya sanar masa halin da ake ciki. Suna gama waya wayar Daddy ta fara ƙara Mama Hafsa ce a nan take sanar da shi halin da Mommy take ciki, da asibitin da suke ake bawa Mommy agajin gaggawa don har lokacin bata farfaɗo ba. Daddy bai gama jin abin da Mama Hafsa take faɗa ba ya katse wayar tare da shiga mota ya fita a guje, kafin Daddy ya ƙarasa asibitin saboda irin gudun da yake yi har sai da ya bige wani ɗan makaranta don ma Allah ya taƙaita yaron bai ji ciwo sosai ba. Yana shiga asibitin likitoci suna shiga yi masa bayanin zuciyar Mommy na gabda buga wa saboda matsananciyar damuwar da ta faɗa lokaci guda.
Raihan ba ita ta farka ba sai bayan da gari ya fara yin haske, kukan waɗansu tsuntsaye ne ya fara tashinta. A hargitse ta miƙe lokaci ɗaya ƙwaƙwalwarta ta fara hakaito mata da abin da ya faru, da sauri da fara dube-dube tana neman ta wurin da Huzaifa zai ɓullo mata sai dai babu shi babu alamarsa. Banɗakin ɗakin ta fara nema amma abin da ya bata mamaki ƙofarsa ta shafe tamkar ba a taɓa yin sa a wurin ba. Zarya ta fara yi a ɗakin tana neman ruwan da za ta yi alwala da shi, sai dai hatta ruwan jarkokin da Huzaifa ya kawo mata a daren ranar babu su ta neme su ta rasa. A hankali ta buɗe ƙofar ta fita zuwa falo, cikin sanɗanta ta fara dube-dube a cikin gidan amma sama da ƙasa da ta duba babu ruwa, kogin da ta gani a daren ranar ne ya faɗo mata da sauri ta ƙarasa wurin tana son buɗe ƙofar tsoro fal zuciyarta, ta jikin ƙofar ta leƙa amma sai gani ta yi kogin ya koma wawaken ƙaton rami. Dawowa cikin gida Raihan ta yi ta fashe da wani irin matsanancin kuka, ganin kuka ba zai kaita ba ya sa sake miƙe wa ta fita wurin ramin nan, da niyyar zura hannunta ta fara yin taimam. A ɗarare ta zura hannunta ta fara taimama tana shirin gamawa ta ji wani abu ya riƙe hannunta gam, a gefe ɗaya ga wani irin gurnani da yake tashi. Ƙara Raihan ta ƙwalla haɗe ta fisgar hannunta da ƙarfi, jini ne ya fara zuba sakamakon gefen ɗan yatsanta da wannan ƙanƙanuwar hallita ta kaiwa cizo. Jiki na rawa Raihan ta rufe ƙofa ta koma ciki, ganin jinin na zuba ya sa ta yaga ɗankwalinta ta ɗaure wurin. Zuciyarta na rawa ta gabatar da sallar asuba a lokacin tuni gari ya waye, wani abin mamaki har ta fara jin hayaniyar mutanen unguwar da yaransu. Tana nan zaune tunanin su Mommy ya faɗo mata da sauri ta ɗauki wayarta ta shiga kira amma fir ta ƙi shiga, hawaye ne yake bin kuncinta ɗaya bayan ɗaya, ga wata irin addababbiyar yunwa da take cinta kasancewar ranar ɗaurin aurenta ban da ruwan tea babu abin da ta iya sha saboda fargaba. Tana nan zaune ta ji turowar ƙofa da sauri ta matsa ta takure wuri ɗaya, Huzaifa ta ga ya shigo cikin ƙananan kaya ba ƙaramin kyau ya yi mata ba duk da tsoronsa ya riga da ya cika zuciyarta, amma da ta ƙare masa kallo sai take ganin kamar ba shi ne Huzaifan da yake son hallaka a daren jiya ba. Ƙirjinta ne ya buga da ya fara tunkarota, hannu ta ɗaga masa tana faɗin, "Don Allah ka mayar da ni gida." Murmushi ya sakar mata sannan ya tsugunna a ɗan nesa da ita ya ce, "Raihan!" Ɗagowa ta yi tana kallonsa ba tare da furta komai ba. "Kin san irin ƙaunar da nake yi miki kuwa? Ina yi miki soyayyar da ko iyayenki ba sa yi miki ita. Ni Huzaifa na rabu da kowa nawa akanki me ya sa ba za ki haƙura da su mu yi rayuwa mai ɗore wa cikin farinciki ba?" Huzaifa yana rufe baki Raihan ta fara jin alamar tsayawar motoci, waigawa Huzaifa ya yi ya saki wani shu'umin murmushi, karaf Raihan ta ji muryar su Mama Hafsa. A zabure ta miƙe ta fice falo haɗe da bankaɗe labulen window ta tura ƙofar windon da ƙarfi tana ƙwala mata kira.
Littafin kuɗi ne 300 idan kina buƙata ki min mgn 0706 206 2624
38