← Book details Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 78 OF 99

Sashe 78

Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Koda suka k'arasa mai gadin ya sanar da su baya ciki, wayarsa ya ciro ya lalubo number Muhdeen ya danna masa kira, jin ya d'aga ne yasa ya ce,
"Kana ina ne?"
Muhdeen dake driving ya ce,
"Sai yau ka tuna da ni?"
"Dama mancewa da kai aka ce nayi?"
"To yanzun dai mene ne?"
"Ina gidanka ne yanzun"
"Ni kuma ina hanya zanje gidan Dady ne, kazo gidan sai mu had'u ko?"
"A'a kadai zo nan dan maganar ba ta can bane."
"Me ke faruwa."
"Idan kazo zaka ji koma mene ne"
"Daga nan ya katse kiran ya maida wayarsa cikin aljihu, ya kalli Sumayya ya ce,
"Yana zuwa mu k'arasa ciki kafin ya zo."
Tana gaba yana binta baya suka wace zuwa falo.
*KUYI HAK'URI DA WANNAN*
*DAGA ALK'ALAMIN*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
*DON K'ARIN BAYANI*
09965327995
Love you oll
Comments & share
Comments & shareCanFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CIdxYmFSO83KRgWbm5FJ2a
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
Idan har kinsan cewa kina cikin group na Inteesar to kada kiyi joining wannan, wancan ya cika ne yasa na bud'e wannan duk abu d'aya ne, sannan idan kinsan cewa ba zakiyi comments ba kada ki shigar mani group, don ko kinshiga idan baki comments zan fitar da ke ne.
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izinina ba.
*SANARWA*
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubuta shi dan cin zarafi ga kowa ba, idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarce ni bada niyar yin hakan nayi ba, arashi ne mai kashe auren wawa.
*BISIMILLAHI RAHAMANI RAHEEM*
Tana gaba yana binta a baya suka wuce zuwa falo.

Zama suka yi suna jiransa ba jimawa ya k'araso tara da sallama d'auke a bakinsa, yana ganin Sumayya ya tamke fusaka tare da cewa
"Ke me na fad'a maki?"
Jabeer ne yayi magana ya ce,
"Dan Allah ka saura..."
D'aga masa hannu yayi alamar dakatarwa ya ce,
"Please Jabeer kada ka shiga wannan maganar, ka barta kawai halinta sai ita."
"Nasan girman laifin da kayi mata kuma na nuna mata kuskurenta, ta nuna tayi nadama dan Allah ka kar'bi tubarta, ko Allah da ya halicce mu idan munyi masa laifi yana yafe mana, ballantana kai bawan Allah, ka bata dama ta gyara kuskurenta insha Allah ba zata maimaita ba, nasan irin son da take maka kuma ba zata iya rabuwa da kai ba, don tasan idan ta sake hukuncin da zai biyo baya, kayi hak'uri dan Allah ko wannan dukan da kayi mata ai yakamta ace ka hak'ura ka huce haushinka."
Murmushin takaici yayi tare da cewa,
"Bazan ta'ba hucewa ba har sai Inteesar ta dawo cikin gidan nan matuk'ar bata dawo ba wallahi bazan ta'ba hucewa ba."
Da sauri Sumayya ta kalli Muhdeen jin kalaman da suke fitowa daga bakinsa,wani bak'in ciki da takaici ya lullu'be ta, ta d'auka fushin da yayi da ita na yunk'urin kisan Kaine, wanda ko akan waye zai d'auki mataki dan babban laifi ta aikata, amma yanzun ta fahimci cewa akan Inteesar ne yayi hakan, take ta tsinci Kanta a wani yanayi na tsananin bak'in ciki, ji tayi kamar ta kurma ihu tayi hauka, amma tuna halin da take ciki yasa tayi k'ok'arin danne bak'in cikinta kada su fahimta, a zubiyarta tana ayyana irin abunda zata aikata, tana magana ita kad'ai a tunaninta a zuciyarta take magana bata san maganar zuciya ce ta fito fili ba, jin muryarta sukayi tana cewa
"Kwantar da Hankalinki Sumy komai zai dawo dai-dai, kada wannan ya d'aga maki hankali kece zakiyi nasara."
Jin muryar Jabeer na cewa
"Nasara?"
Yasa ta gane cewa a fili tayi maganar, dan haka ta wayance da cewa,
"Eh mana ai mai hak'uri shine mai nasara."
Muhdeen ne ya kalli Jabeer ya ce,
"Jabeer a zahirin gaskiya bazan..."
Jabeer yayi saurin cewa
"Kada ka ce haka, na fahimci matsalarka, insha Allah zata gyara ka tuna baya da darajar iyaye da kuma soyayyar da ta nuna maka kayi hak'uri komai ya wuce."
Murmushin takaici yayi
tare da cewa
"Ba zata ta'ba canzawa ba, na san wace ce ita duk da yanzun ta wuce sani na, kuma ka sani ba abunda zai wuce har sai Inteesar ta dawo."
Danne bak'in cikinta tayi tare da k'ak'alo murmushi ta ce,
"Bakomai duk da hakan nagode Allah ya dawo da ita lafiya, tana ina ne?"
"Bai shafe ki ba, salon na fad'a maki kije ki k'arasa ta?"
Murmushi tayi ta ce
"Yanzun na Sumayya da ka sani a baya bace, wannan ta daban ce na sauya, ina son ka d'auki abunda nayi a baya kayi jifa da shi kada ka sake waiwayawa gare shi, hakan zaisa mu samu zaman lafiya."
Durk'usawa tayi akan gwuiwarta biyu ta fara magana
"Mijina ka yafe mani kuskuren da na aikata na tuba, ka gafarce ni hakan ba zata sake faruwa ba insha Allah."
Bud'e baki yayi da niyyar magana, Jabeer ya ce,
"Kada ka ce komai ka yafe mata dan albarkacin nabiyyin rahmati ."
Murmushi yayi tare da cewa
"Wato Jabeer kasan cewa duk fushin da nayi idan aka kira annabin rahama sai na hak'ura, dan ba za'ace annabi ba banyi ba, amma bakoma zaka iya tafiya."
Sallama Jabeer yayi masa ya tafiyarsa, yana fita ta fad'a jikin Muhdeen ta fashe da kuka ta fara magana
"Nasan zaka d'auke ni mace mara aji, mai nacin soyayya kada kaga laifi na zuciyata ce take assasa ni, I'm crazy about yor I love you more than everything."
Kuka ta dingayi sosai shima kansa yasan tana masifar sonta, wanda had'uwarsu ta farko ita ce ta fara nuna masa so kafin shi ya nuna mata, kuma yasan zata iya 'batawa da kowa akansa, amma duk da haka d'abi'arta baya sonsu, kallon fuskarta yayi ganin yadda ya sauya mata kamanni kuma ya kore ta amma ta kasa tafiya ta dawo ta nemi yafiyarsa, wanda bai ta'ba tunanin hakan ba, yadda take ji da kanta amma wannan Karan ta aje ji da kan a gefe saboda sonsa da gudun rasa shi, tausayinta ne ya kama sa cikin tausayi ya ce,
"Am so sorry"
"Ka daina sona ko?"
Murmushi yayi tare da cewa
"Ban daina sonki ba, kuma bazan ta'badainawa ba, halinki ne bana so, idan kika sauya bani da wata matsala da ke."
Goge hawayen fuskarta tayi tare da cewa
"To naji zan gyara, ita fa kana sonta?"
Ya gane abunda take nufi amma ya ce,
"Wace ce nake so?"
"Inteesar"
"Dukanku mata na ne kuma dukanku ina sonku."
'Daga kanta tayi daga k'irjinsa ta kalle shi da sauri, k'walla ce take k'ok'ari zubo mata na kishinsa, amma sai tayi saurin maida hawayenta ta ce,
"Kai da kanka ka sanar dani cewa kai baka sonta ka tsane ta, kuma nasan auren doke akayi maku daga kai har ita baku son juna, to yaushe ka fara sonta haka? dama saboda ita ce kayi mani dukan da kayi mani? saboda ita ce nemi raba ni da rayuwata?"
"Ba saboda ita bane, ko da ma waye kika aikatawa abunda kika aikata mata hukuncin da zan maki kenen, yakamata ki gane kuskurenki."
Jinjina kai tayi cike da k'unar rai ta ce,
"Yanzun idan ta dawo gidan nan tare zamu dinga sharing d'inka ni da ita?"
Jinjina mata kai yayi alamar eh kasa danne bak'in cikinta tayi ta fashe masa da kuka tana cewa
"Ai ba haka mukayi da kai ba, cewa kayi ko an d'aura maka aure da ita ba ruwanka da ita, baka d'auke ta mata a gare ka ba, na d'auka 'yar aiki aka kawo mani, amma shine yanzun zaka canza magana?"
"To yanzun maganarki zanbi, ko maganar Aah da manzonsa zanbi?"
Kallonsa tayi da idanunta da sukayi jazir tabce,
"Nidai na fad'a maka"
Addinina ya halatta mani auren mata hud'u, koda kike ganin Inteesar auren had'i akyi muna amma ai tana da hakki akaina, kuma idan na fifita ki aknta ko kuma na fifita ta aknaki Allah zai tambaye ni, ko kina son ranar gobe kiyama na tashi 'barin jiki na a karkace?"
Ba zata iya cigaba da saurarensa ba, dan haka ta ruga a guje zuwa d'akinta tana kuka, a tunaninta zai biyo ta ne kamar yadda suka Saba idan tayi haka ya bita shima a guje, amm ayau kam sai taga ba haka ba, ko a jikinsa ya fice a binsa, lokacin da taji tashin motarsa kukanta ya k'aru sosai
Pillows dake kan gadon ta fara d'auka tana jifa da su zanin gadon ma ta yaur tayi jifa da shi, ta mik'e ta nufi dressing mirror kenan ta tuna da zancensa, na cewa halinta ne baya so, don haka ta dakata ta tsaya tana nazari fasawa tayi ta kwashe pillows din da bedsheet ta d'ora Kan gadon don bata ma san yadda zata gyara gadon ta shimfid'a sabon zanin gadon ba.

A can gidan kuwa Inteesar tana cikin d'akin Mufida ta rafka tagumi, tunanin Ummanta kawai take yi, don tunda suka je asibiti dau d'aya ta gaida Ummanta bata sake zuwa ba, don bata san ya jikin nata ba ya kasance ba, ta dai san ance an sallame su tana gida, dan haka ta mik'e ta nufi falo don neman izinin zuwa gaida Mahaifiyarta.

Zaune suke Gwaggo ce da Mummy suna fira, Inteesar ta k'araso wajen tare da sallama, durkuwa tayi tare da cewa
"Sannunku"
Gaba d'ayansu suka amsa da yauwa, Gwaggo ta ce,
"Yar albarka kin fito?
Chapter 78 · 0% Book details