Sashe 73
Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Cikin sanyin muryarta ta ce,
"Lafiya lau da sauki' naji muryarsa ya zo gidan nan Gwaggo dan Allah ka da ku maidani gidansa"
Ta k'arasa maganar cikin rawar murya kamar wacce zata saka kuka, dafa kafad'arta Gwaggo tayi tare da cewa
"Ki kwantar da hankalinki ba mai maida ke gidansa kinji."
Jinjina kai tayi alamun gamsuwa ta ce
"To nagode"
Daga nan ta nufi hanyar kitchen.
Jin muryar Gwaggo tayi tana cewa
"Ina kuma zaki je?"
"Zanje na gaishe da Mummy ne"
Daga nan ta nufi kitchen d'in inda ta samu Mummy na fere dankalin turawa, Mummy na ganinta ta sakar mata murmushi ta ce,
"Daughter kin tashi"
Itama murmushi ta sakar mata zata durk'usa Mummy tayi saurin cewa
"A'a Daughter tashi dan Allah"
"Ina kwana Mummy"
"Lafiya lau Daughter ya jikinki"
"Naji sauk'i Mummy"
"Ina ke maki ciwo yanzun?"
"Bakomai Mummy, ba wurin da ke mani ciwo?"
"Kin tabbata"
"Eh Mummy"
"To alhamdulillah haka nake son ki"
K'ok'arin karb'ar wuk'ar take ne sai Mummy ta hana ta tace
"Daughter kije ki kwanta ki huta"
"Mummy kinsan ban saba kwanciya da safe ba idan ba aiki mayi ba, dan Allah ki kawo zan iya."
Mik'ewa Inteesar tayi ta nufi wajen gas don duba ruwan shayin da ta d'ora, Gwaggo ce ta shigo kitchen d'in ganin Inteesar na aiki yasa ta saki salati.
"Fatima saboda rashin tausayi yarinyar da d'anki ya gama azabtar da ita daga fardad'owarta kuma sai ki sakar mata aiki? wannan ai rashin tausayi ne muraran."
"Gwaggo ba laifinta bane ta hanani nice na matsa mata dole ta barni."
"Saboda baki tausayin kanki da kanki ko?"
"Gwaggo wallahi zan iya kibarni nayi."
"Sai kiyi tayi ai"
Daga nan ta saka kai ta fice, Mummy dai uffan bata ce ba don inda sabo ta saba da halin Gwaggo.
Muhdeen kuwa da ya d'auki motarsa ya bar gidan, kai tsaye gidansu Inteesar ya tafi, koda ya shiga a zaure ya samu Abba yana karatun al'qur'ani mai girma, bayan ya kai k'arshen ayar da yake karantawa ne ya rufe tare da ajiye shi gefen tabarmar da yake zaune, durk'usawa yayi bayan yayi sallama
"Ina kwana Abba"
"Muhammad kai ne da safen nan? ka tashi lafiya?
"Lafiya lau Abba"
"Masha Allah, ya kwanan iyali?"
"Lafiya lau"
"Masha Allah"
Shiru yayi ya kada magana, har abba yayi magana ya ce,
"Bari na shiga na duba ko Umman ta tashi sai ku gaisa."
"To Abba"
Daga nan Abba ya mik'e ya nufi cikin gidan, ya tarar da Umma ta fito daga d'akinta kenan zata hura huta,kallonsa tayi tace,
"Mallam ka shigo ne"
"Eh ga Muhammad nan zai gaishe ki."
"Wani Muhammad d'in"
"Surukinki mana"
"Murmushi tayi tare da cewa
"Tare da Inteesar suka?"
"A'a shi kad'ai na gani"
Daga nan ya koma zaure inda suka shigo tare Muhdeen na bunsa a baya, suka tarar har Umma ta shimfid'a masu tabarma, durk'usawa yayi ya ce,
"Ina kwana Umma?"
"Lafiya lau Muhammad"
"Ya k'arfin jiki?"
"Jiki Alhamdulillah naji sauk'i"
"Masha Allah Allah ya k'ara lafiya"
"Ameen ka zauna mana"
Zama yayi gefen tabarmar kansa a k'asa, muryar Abba ya ji yana cewa
"Sannu da k'ok'ari fa mungode da d'awainiyar Asibiti, Allah ya saka da alkahiri."
"Bakomai Abba addu'a da sanya albarka kawai nake nema daga gare ku"
Murmushi kawai Abba yayi tare da cewa
"Ai kullun cikin yi maku addu'a muke Allah ya albarkaci rayuwarku ya kare ku daga sharrin abun k'i yasa ku gama da duniya lafiya."
Murmushi yayi tare da jin dad'in addu'a da Abba yayi masu Umma ce ta amsa da Ameen, shiru ne ya biyo baya, inda muryar Umma ta katse shirun da cewa
"Halan Inteesar bata san zaka zo nan ba?"
Zuciyarsa ce ta tsinke ya rasa me zai ce, amma tuna zancen Mummy da tayi masa da gudun kada hankalin iyayenta su tashi yasa ya k'ak'alo murmushi ya ce
"Bata sani ba Umma"
"Ayyah nasan da ta sani zata dame ka, ka kawo ta."
Fira suka d'an ta'ba daga nan yayi masu sallama ya tafi.
Yana driving gaba d'aya hankalinsa a tashe yake ya rasa inda zai saka kansa yanzun ya gama tabbatar wa da kansa cewa bata gidan Ummanta, kai tsaye gidansu ya koma.
Suna kitchen sun kammala aikinsu dai-dai lokacin da Inteesar ta fito daga cikin kitchen d'in d'auke da faranti da aka jera foodflask a ciki tana fitowa daga kitchen d'in ta nufo falo, dai-dai lokacin da Muhdeen ke shigowa ya juya falon ya maida k'ofar ya rufe.
*Daga alk'alamin*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
*DON K'ARIN BAYANI*
09065327995
Love you oll
Comments & shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izinina ba.
*SANARWA*
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubuta shi dan cin zarafi ga kowa ba, idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarce ni bada niyar yin hakan nayi ba arashi ne mai kashe auren wawa.
*BISIMILLAHI RAHAMANI RAHEEM*
Page6
Suna kitchen sun kammala aikinsu dai-dai lokacin da Inteesar ta fito daga cikin kitchen d'in, d'auke da faranti da aka jera foodflask a ciki, tana fitowa daga kitchen d'in ta nufo falo dai-dai lokacin da Muhdeen ke shigowa ya juya falon ya maida k'ofar ya rufe, tana ganinsa tayi saurin komawa cikin kitchen d'in da sauri ba tare da ya ganta ba, jin motsi hanyar kitchen yasa ya kalli wajen amma baiga kowa ba.
Mummy dake cikin kitchen ganin Inteesar ta dawo da sauri yasa ta ce,
"Lafiya kuwa me ya faru?"
A hankali tayi magana ta ce
"Yaya ne ya dawo"
Da sauri Mummy ta nufi hanyar fita kitchen d'in, tana fita kenan sai gashi yana k'ok'arin shigowa kitchen din, tsayawa tayi ta kalle shi fuska a tamke ta ce,
"Lafiya?"
Cikin karaya yayi magana yana cewa
"Mummy na shiga uku wallahi Inteesar bata gidan iyayenta, ku taimaka mani na samota ta ina zan fara, nemanta ban san mutanen da take mu'amala da su ba, ban san k'awayensu ba, suk da cewar jiya nasa Mufida ta Kira duk wasu k'awayensu amma sunce bata nan, Mummy yanzun ba wanda ya kamata ya taimkaa mani a cikin wannan halin sai Mufida tasan mutanen da Inteesar ta sani k'awaye da dangi da 'yan uwa, dan haka tazo mu tafi..."
Tun kafin takai k'arshen maganar da zaiyi yaji Mummy na cewa
"Kuje ina? kuma tare da wace ce? badai Mufida ta ba kamar yadda bata san mai ya had'a ku har Inteesar ta bar gida ba haka zalika ba zaka saka ta cikin zancen nemanta ba, kaje can ka k'arata duk inda 'yarsu ta shiga ka je ka nemo masu ita."
Da mamaki ya ke binta da kallo don kwata-kwata baiyi tunanin jin makamancin wannan zancen daga gareta ba cikin kwantar da muryar ya fara magana
"Mummy yanzun ke da bakinki kike fad'in haka? idan da wani ne ya fad'a mani abunda kika fad'a zan k'aryata shi, amma ni naji da kunne na."
"Ka ji ka k'ara ji duk inda 'yar mutane ta shiga ka je ka nemo masu 'yarsu, duk yadda akayi akwai wani abunda kayi mata Wanda yasa dole ta fita ta bar maka gidanka, amma ba banza ba haka nan kawai ba zata fita ba an d'auki amanar 'yar mutane an baka kana ta gallaza mata har ya kai ga ta bar maka gidanka, Dan haka zama bai ganka ba ka tafi duk inda take a fad'in garin nan ka nemo masu 'yarsu."
"Mummy ba gallazawa ne yasa ta bar gidan ba, domin da gallazawa ne da tuni ta bar gidan a lokacin da nake gallaza mata, amma ba yanzun ba da bana gallaza mata ta bar gidan duk yadda akayi akwai wani 'boyayyen al'marin wanda bansan da shi ba."
Ta'be baki Mummy tayi tare da cewa
"Sai ka tafi ka nemo ta koma mene ne Kaine sanadi."
Zuba mata Ido yayi yana kallonta ya kasa gane dalilin da yasa suka yi biris da lmaarin nan shiru yayi na d'an lokaci kafin ya nufi k'ofara fita ya fice.
Yana driving ne ya ciro wayarsa tare da lalunar wayar Salisu, bugu biyu ya d'aga bai jira yayi magana na ya ce,
"Kana ina ne Salisu?"
Salisu ya bashi amsa da cewa
"Yanzun gani k'ofar gida ina shirin fita."
"Dan Allah ka jira ni a k'ofar gidan naku, gani nan zuwa yanzun nan insha Allah."
Daga nan ya katse wayar tare da maida hankalinsa ga driving din da yake yi.
"Lafiya lau da sauki' naji muryarsa ya zo gidan nan Gwaggo dan Allah ka da ku maidani gidansa"
Ta k'arasa maganar cikin rawar murya kamar wacce zata saka kuka, dafa kafad'arta Gwaggo tayi tare da cewa
"Ki kwantar da hankalinki ba mai maida ke gidansa kinji."
Jinjina kai tayi alamun gamsuwa ta ce
"To nagode"
Daga nan ta nufi hanyar kitchen.
Jin muryar Gwaggo tayi tana cewa
"Ina kuma zaki je?"
"Zanje na gaishe da Mummy ne"
Daga nan ta nufi kitchen d'in inda ta samu Mummy na fere dankalin turawa, Mummy na ganinta ta sakar mata murmushi ta ce,
"Daughter kin tashi"
Itama murmushi ta sakar mata zata durk'usa Mummy tayi saurin cewa
"A'a Daughter tashi dan Allah"
"Ina kwana Mummy"
"Lafiya lau Daughter ya jikinki"
"Naji sauk'i Mummy"
"Ina ke maki ciwo yanzun?"
"Bakomai Mummy, ba wurin da ke mani ciwo?"
"Kin tabbata"
"Eh Mummy"
"To alhamdulillah haka nake son ki"
K'ok'arin karb'ar wuk'ar take ne sai Mummy ta hana ta tace
"Daughter kije ki kwanta ki huta"
"Mummy kinsan ban saba kwanciya da safe ba idan ba aiki mayi ba, dan Allah ki kawo zan iya."
Mik'ewa Inteesar tayi ta nufi wajen gas don duba ruwan shayin da ta d'ora, Gwaggo ce ta shigo kitchen d'in ganin Inteesar na aiki yasa ta saki salati.
"Fatima saboda rashin tausayi yarinyar da d'anki ya gama azabtar da ita daga fardad'owarta kuma sai ki sakar mata aiki? wannan ai rashin tausayi ne muraran."
"Gwaggo ba laifinta bane ta hanani nice na matsa mata dole ta barni."
"Saboda baki tausayin kanki da kanki ko?"
"Gwaggo wallahi zan iya kibarni nayi."
"Sai kiyi tayi ai"
Daga nan ta saka kai ta fice, Mummy dai uffan bata ce ba don inda sabo ta saba da halin Gwaggo.
Muhdeen kuwa da ya d'auki motarsa ya bar gidan, kai tsaye gidansu Inteesar ya tafi, koda ya shiga a zaure ya samu Abba yana karatun al'qur'ani mai girma, bayan ya kai k'arshen ayar da yake karantawa ne ya rufe tare da ajiye shi gefen tabarmar da yake zaune, durk'usawa yayi bayan yayi sallama
"Ina kwana Abba"
"Muhammad kai ne da safen nan? ka tashi lafiya?
"Lafiya lau Abba"
"Masha Allah, ya kwanan iyali?"
"Lafiya lau"
"Masha Allah"
Shiru yayi ya kada magana, har abba yayi magana ya ce,
"Bari na shiga na duba ko Umman ta tashi sai ku gaisa."
"To Abba"
Daga nan Abba ya mik'e ya nufi cikin gidan, ya tarar da Umma ta fito daga d'akinta kenan zata hura huta,kallonsa tayi tace,
"Mallam ka shigo ne"
"Eh ga Muhammad nan zai gaishe ki."
"Wani Muhammad d'in"
"Surukinki mana"
"Murmushi tayi tare da cewa
"Tare da Inteesar suka?"
"A'a shi kad'ai na gani"
Daga nan ya koma zaure inda suka shigo tare Muhdeen na bunsa a baya, suka tarar har Umma ta shimfid'a masu tabarma, durk'usawa yayi ya ce,
"Ina kwana Umma?"
"Lafiya lau Muhammad"
"Ya k'arfin jiki?"
"Jiki Alhamdulillah naji sauk'i"
"Masha Allah Allah ya k'ara lafiya"
"Ameen ka zauna mana"
Zama yayi gefen tabarmar kansa a k'asa, muryar Abba ya ji yana cewa
"Sannu da k'ok'ari fa mungode da d'awainiyar Asibiti, Allah ya saka da alkahiri."
"Bakomai Abba addu'a da sanya albarka kawai nake nema daga gare ku"
Murmushi kawai Abba yayi tare da cewa
"Ai kullun cikin yi maku addu'a muke Allah ya albarkaci rayuwarku ya kare ku daga sharrin abun k'i yasa ku gama da duniya lafiya."
Murmushi yayi tare da jin dad'in addu'a da Abba yayi masu Umma ce ta amsa da Ameen, shiru ne ya biyo baya, inda muryar Umma ta katse shirun da cewa
"Halan Inteesar bata san zaka zo nan ba?"
Zuciyarsa ce ta tsinke ya rasa me zai ce, amma tuna zancen Mummy da tayi masa da gudun kada hankalin iyayenta su tashi yasa ya k'ak'alo murmushi ya ce
"Bata sani ba Umma"
"Ayyah nasan da ta sani zata dame ka, ka kawo ta."
Fira suka d'an ta'ba daga nan yayi masu sallama ya tafi.
Yana driving gaba d'aya hankalinsa a tashe yake ya rasa inda zai saka kansa yanzun ya gama tabbatar wa da kansa cewa bata gidan Ummanta, kai tsaye gidansu ya koma.
Suna kitchen sun kammala aikinsu dai-dai lokacin da Inteesar ta fito daga cikin kitchen d'in d'auke da faranti da aka jera foodflask a ciki tana fitowa daga kitchen d'in ta nufo falo, dai-dai lokacin da Muhdeen ke shigowa ya juya falon ya maida k'ofar ya rufe.
*Daga alk'alamin*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
*DON K'ARIN BAYANI*
09065327995
Love you oll
Comments & shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izinina ba.
*SANARWA*
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubuta shi dan cin zarafi ga kowa ba, idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarce ni bada niyar yin hakan nayi ba arashi ne mai kashe auren wawa.
*BISIMILLAHI RAHAMANI RAHEEM*
Page6
Suna kitchen sun kammala aikinsu dai-dai lokacin da Inteesar ta fito daga cikin kitchen d'in, d'auke da faranti da aka jera foodflask a ciki, tana fitowa daga kitchen d'in ta nufo falo dai-dai lokacin da Muhdeen ke shigowa ya juya falon ya maida k'ofar ya rufe, tana ganinsa tayi saurin komawa cikin kitchen d'in da sauri ba tare da ya ganta ba, jin motsi hanyar kitchen yasa ya kalli wajen amma baiga kowa ba.
Mummy dake cikin kitchen ganin Inteesar ta dawo da sauri yasa ta ce,
"Lafiya kuwa me ya faru?"
A hankali tayi magana ta ce
"Yaya ne ya dawo"
Da sauri Mummy ta nufi hanyar fita kitchen d'in, tana fita kenan sai gashi yana k'ok'arin shigowa kitchen din, tsayawa tayi ta kalle shi fuska a tamke ta ce,
"Lafiya?"
Cikin karaya yayi magana yana cewa
"Mummy na shiga uku wallahi Inteesar bata gidan iyayenta, ku taimaka mani na samota ta ina zan fara, nemanta ban san mutanen da take mu'amala da su ba, ban san k'awayensu ba, suk da cewar jiya nasa Mufida ta Kira duk wasu k'awayensu amma sunce bata nan, Mummy yanzun ba wanda ya kamata ya taimkaa mani a cikin wannan halin sai Mufida tasan mutanen da Inteesar ta sani k'awaye da dangi da 'yan uwa, dan haka tazo mu tafi..."
Tun kafin takai k'arshen maganar da zaiyi yaji Mummy na cewa
"Kuje ina? kuma tare da wace ce? badai Mufida ta ba kamar yadda bata san mai ya had'a ku har Inteesar ta bar gida ba haka zalika ba zaka saka ta cikin zancen nemanta ba, kaje can ka k'arata duk inda 'yarsu ta shiga ka je ka nemo masu ita."
Da mamaki ya ke binta da kallo don kwata-kwata baiyi tunanin jin makamancin wannan zancen daga gareta ba cikin kwantar da muryar ya fara magana
"Mummy yanzun ke da bakinki kike fad'in haka? idan da wani ne ya fad'a mani abunda kika fad'a zan k'aryata shi, amma ni naji da kunne na."
"Ka ji ka k'ara ji duk inda 'yar mutane ta shiga ka je ka nemo masu 'yarsu, duk yadda akayi akwai wani abunda kayi mata Wanda yasa dole ta fita ta bar maka gidanka, amma ba banza ba haka nan kawai ba zata fita ba an d'auki amanar 'yar mutane an baka kana ta gallaza mata har ya kai ga ta bar maka gidanka, Dan haka zama bai ganka ba ka tafi duk inda take a fad'in garin nan ka nemo masu 'yarsu."
"Mummy ba gallazawa ne yasa ta bar gidan ba, domin da gallazawa ne da tuni ta bar gidan a lokacin da nake gallaza mata, amma ba yanzun ba da bana gallaza mata ta bar gidan duk yadda akayi akwai wani 'boyayyen al'marin wanda bansan da shi ba."
Ta'be baki Mummy tayi tare da cewa
"Sai ka tafi ka nemo ta koma mene ne Kaine sanadi."
Zuba mata Ido yayi yana kallonta ya kasa gane dalilin da yasa suka yi biris da lmaarin nan shiru yayi na d'an lokaci kafin ya nufi k'ofara fita ya fice.
Yana driving ne ya ciro wayarsa tare da lalunar wayar Salisu, bugu biyu ya d'aga bai jira yayi magana na ya ce,
"Kana ina ne Salisu?"
Salisu ya bashi amsa da cewa
"Yanzun gani k'ofar gida ina shirin fita."
"Dan Allah ka jira ni a k'ofar gidan naku, gani nan zuwa yanzun nan insha Allah."
Daga nan ya katse wayar tare da maida hankalinsa ga driving din da yake yi.