Sashe 29
Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Umma ta amsa da
"Ameen"
Gidan Muhdeen kuwa tunda Sumayya ta shige d'akinta ta murza key ta rufe sai suratai take kamar wata mahaukaciya.kayan kwallalliyar da suke jere a gaban dressing mirror ne ta Fara wargazawa tana d'aukar su d'aya bayan d'aya tan jifa dasu masu fashewa na fashewa kallon kanta tayi ta cikin mirror d'in hannu ta dunk'ule ta kaiwa mirror naushi take mirrorn ya tarwatse idonta takai ga T.v dake mak'ale a bango a guje ta k'arasa gaban T.v zaro shi tayi ta bugashi a Kan tiles d'in d'akin ya fashe haka komai dake d'akin ta shiga illata shi, hatta pillows da bedsheet sai da ta yi ta cilli dasu durowar kayanta ta bud'e ta dinga d'ebo kayan tana cillosu waje, a k'asa haka ta dingayi bayan ta gama zuar da kayan ta dinga binsu d'aya bayan d'aya ta yayyagasu ko wanne sai ta rabashi gida biyu sannan tayi cilli dashi gefe wad'anda taji sunyi Mata k'arfi a hannu sai ta saka hak'ori tayi masu hanya sannan ta k'arasa yagawa.bayan ta gama ne ta bud'e 'bangaren da akwatunan kayan lefenta suke,nan ma ta zuzzuge zif d'in akwatunan haka ta dinga wurgi da kayayyakin abubuwan fashewa na fashewa wad'anda ba na fashewa ba kuwa ta tattaka su.
'Bangaren Muhdeen kuwa tunda Sumayya ta fita daga d'akinsa ya zauna a bakin gadon gaba d'aya ya rasa mai ke damunsa.don yasan ko yabi Sumayya Dan ya rarrasheta ba sauraransa zatayi ba,hakan yasa ya d'an barta tukunna.Ya rasa me yasa Gwaggo zata yi masa haka zata sa ayi masa aure ba tare da amincewarsa ba,sannan ta rasa wacce zata say aura masa sai Inteesar yarinyar da ya tsana a rayuwar sa ita ce aka aura masa?lallai kuwa Inteesar ta tabka babban kuskure da ta yadda da wannan auren,Don wallahi sai ta d'and'ani kud'arta,daga ranar da ta shigo cikin gidan nan a matsayin matarsa daga ranar zata zatayi ban kwana da farin ciki.Yana cikin zancen zucin nasa ne yaji wani irin k'ara na tarwatsewar abu,cikin tashin hankali ya fito daga cikin d'akinsa ya nufi d'akin Sumayya.
Daga cikin d'akin Sumayya kuwa show glass d'in da aka jera Mata turararruka ne da su kwalaben humra da turararen wuta,lokacin da idonta ya sauka akan show glass d'inne ta nufesa tana k'arasawa ta d'auki k'arfen da da ke ajiye na rataya jakunkuna ,tana d'aukar k'arfen ne ta bugawa show glass ya tarwatse,k'arar show glass d'inne yaja hankalin Muhdeen ya nufo d'akin nata cikin tashin hankali.
Yana tura k'ofar yaji a datse ya shiga buga k'ofar Yana Kiran sunanta Amma Ina Bata ma San tanayi ba sai buge-buge da jefe-jefe takeyi tana Sam batu tayi nan tayi can duk abunda ya tari gabanta jifa dashi take,komai na d'akin ta gama hargiza wa ta fargasa duk abunda ya kasance na fashewa abu biyu ne a d'akin Wanda suke zaune a muhallinsu, durowar zuba kayanta sai gado suma don ba zata iya d'aukarsu bane hatta katifa tayi jifa dashi gefe.
Muhdeen ne koma d'akinsa ya d'auko key yazo ya bud'e k'ofar,ganinta ya yi kamar mahaukaciya duk ta fita hayyacinta ga hannayenta da taji ciwo.Suna had'a ido dashi ta d'aga masa hannu ta ce,
"out of my side"
Cikin tashin hankali ya ce,
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un"
k'awa tayi ta d'auki wani dogon fasasshen gilashi ta d'aga ta saita shi dai-dai saitin cikinta cikin d'aga murya ta ce,
"Kafita!"
Had'a hannayensa yayi alamar rok'o ya Fara magana
"Dan Allah ki tsaya ki saurareni,wallahi bada amincewa ta aka d'aura Mani aure da Inteesar ba."
Zaro ido tayi cikin cikin mamaki ta ce,
"Inteesar ka aura?"
Girgiza Kai tayi tana fad'in
"I said out, wallahi idan baka fita ba zan kashe kaina!"
Ta fad'i maganar tana saita tsinin kwalbar a cikinta.
Daga alk'alamin
Maman Ihsan
09065327995
Love u oll
*MAULUD MUBARAK*Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga.
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi ga kowa ba,idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba.Arashi ne Mai kashe auren wawa.
Page3
"I said out,wallahi idan baka fita ba zan kashe kaina!"
Ta fad'i maganar tana saita tsinin kwalbar a cikinta.
Ganin kamar da gaske take yasa ya fita falo gaba d'aya ya rasa me zaiyi.
Wauarsa ya ciro daga cikin aljihu, number Jabeer ya lalubo ya danna masa Kira,bayan Jabeer ya d'aga wayar ne muhdeen ya fara magana yana cewa
"Jabeer don Allah duk abunda kake ka ajiye shi kazo gidana yanzun nan."
bai jira cewarsa ba ya kashe kiran.Safa da marwa yake yana zaman jiran Jabeer.
Jin sallamar Jabeer ne yasa shi sakin ajiyar zuciya,k'arasowa yayi ya rik'e hannun Jabeer ya ce,
"Jabir ina cikin tashin"
Kallonsa Jabeer yayi cikin rashin fahimtar inda zancensa ya dosa ya fara magat
"Wai meke faruwa ne ne?"
"Ai komai ma ya faru"
"Kayi mani bayanin da zan gane inda zancenka ya dosa,ka kirani a waya kana cewa wai da sanina akayi maka aure wani irin aure kuma? dan Allah ka fitar dani haske domin kwata-kwata ban gane inda zancenka ya dosa ba."
Cikin 'bacin ran yanayin da ya ke ciki ya fara magana
"Jabeer aure suka k'ara yi mani,sati biyu da auren mu da my Sumy suka k'ara mani aure,jiya ana idar da sallar juma'a ne aka d'aura aure ba tare da sun nemi izini na ba kawai umarni suka bani inaji Ina gani aka d'aura auren.Jabeer wallahi bana son auren nan ba yadda zanyi ne."
Shiru Jabeer yayi yana nazarin maganar shikam baiji takaicin wannan auren da aka d'aurawa Muhdeen ba,don yasan cewa iyayen nasau sun lura da rashin tarbiyar Sumayya ce shiyasa aka nema masa masa wata matar.A cikin zuciyarsa yaji dad'in zancen don dama ba yadda baiyi dashi ba akan kada ya auri Sumayya amma soyayyarta ta riga da ta rufe masa ido ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa
"Wace ce matar da aka aura maka?"
Cikin takaici ya fad'i sunanta
"INTEESAR"
Gaban Jabeer ya fad'i Jin sunan Inteesar,take yaji wani Abu zuciyarsa har sai da wayar hannunsa ta su'buce masa ta fad'i k'asa.Sunanta ya ambata da k'arfi
"INTEESAR?"
Kai Muhdeen ya jinjina masa alamar eh
Shiru yayi na d'an lokaci kafin ya saki murmushi ya ce,
"Indai Inteesar ce na Taya ka murna samunta a matsayin mata,duk da na fahimci baka son aurenta amma Ina da yak'inin cewa zuwa gaba zakayi alfahari da ita."
Tsuki Muhdeen yayi
"Allah ya kiyaye kaima fa na lura da cewa a 'bangaren su Gwaggo kake."
Gajeren murmushi Jabeer yayi tare da cewa
"Ba zaka gane gata akayi maka ba sai nan gaba."
"Ba wani gata ni ba wannan yasa na kiraka ba,tunda my Sumy taji Ina fad'a maka zancen auren Inteesar har suma tayi Kai a rak'aice dai gata can a d'aki dai fashe-fashe takeyi."
Da mamaki Jabeer ya saki baki yana kallonsa
"Yanzu tana ina Wai?"
Tana d'akinta Kai tsaye suka nufi d'akin,k'wank'wasawa suka dingayi suna bata baki amma ina bata saurare su ba.Haka suka hak'ura inda Jabeer ya nuna masa cewa ya barta zuwa anjima idan ta d'an sauko sai suyi magana.
Daga haka ne Muhdeen yaja Jabeer zuwa d'akinsa inda Muhdeen ya shiga bathroom room don yin wanka inda yabar Jabeer zaune saman sofa yana jiransa.
Daga can d'akin Sumayyay kuwa tunda ta gaji taga bazata iya cigaba da yayyaga kayan ba.Hakan yasa sauran akwatunan kayan lefen auren ta dinga jansu tana kaiwa harabar gidan tana jibgesu,a haka har ta gama jidar kayan lefen auren bayan ta gama jibgasu waje guda ne ta d'aga kai ta hango Mai gadin gidan tare da Zayyanu Direban gidan suna kallonta,harara ta watsa masu tare da yi wa Zayyanu Direban alamun yazo manuniya,gabasa ne ya fad'i ganin ta kirasa don kallon mahaukaciya sukayi mata ganin yadda takeyi tsoro da fargaba ya hana Zayyanu k'arasawa wajenta sai da mai gadin yayi masa da alamar yaje,cikin tsoro ya k'arasa wajenta.magana tayi masa a kausashe ta ce,
"Kaje ka kawo mani fetur yanzun nan."
Da mamaki ya tsaya yana kallonta,
Tsawar da ta daka masa ne yasa yaba r wajen cikin rawar jiki,ba jimawa sai gashi ya dawo da fetur a cikin galan,amsa tayi tare da ce masa ya kawo mata ashana.k'arasawa yayi wajen mai gadin gidan ya amso mata ashana ya kawo mata.
Ga mamakinsu gani sukayi ta bud'e robar fetur d'in ta tsiyaya shi duka a jikin akwatunan kayan lefenta,sanan ta kyasta ashana ta jefa kai tsaye cikin gidan ta koma.
Jabeer dake zaune saman sofa ne ya hango bak'i ta jikin gilashin windows, mi'kewa yayi tare da d'an zuge gilashin window d'in,ganin hayak'in da ya turnik'e gidan ne yasa shi sakin salati dai-dai lokacin da Muhdeen ya fito daga wanka ganin hakan yasa cikin sauri ya saka Jallabiya suka nufi hanyar fita,don sun d'auka gobara ce.
Suna nufar inda suka ga hayak'in na tasowa turus suka tsaya ganin akwatuna da da kaya suna ci da wuta.
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un"
Kalmar da Muhdeen ya furta kenan.Jabir ya kalleshi tare da cewa
" ta yaya kuma me hakan yake nufi?"
Ajiyar zuciya Muhdeen ya sauke tare da cewa
"Sumayya ce ta k'ona kayan lefenta "
Cikin mamaki Jabeer ya ce,
"Kana nufin kayan lefen da kuka je Dubai kuka siyo da akwatunan sune ta bankawa wuta?"
Kai Muhdeen ya jinjina masa alamun eh.
"Tirk'ashi
Shine kalmar da Jabeer ya fad'a,sannan ya d'ora da cewa
"Gaskiya duk yadda nake tunananin Sumayya lamarinta ya wuce haka,ta wuce sanin tunanina.wannan ai hauka ne da rashin sanin darajar dukiya.kayan miliyoyin kud'in ne zata bankawa wuta?saboda mahaukacin kishi?
"Ameen"
Gidan Muhdeen kuwa tunda Sumayya ta shige d'akinta ta murza key ta rufe sai suratai take kamar wata mahaukaciya.kayan kwallalliyar da suke jere a gaban dressing mirror ne ta Fara wargazawa tana d'aukar su d'aya bayan d'aya tan jifa dasu masu fashewa na fashewa kallon kanta tayi ta cikin mirror d'in hannu ta dunk'ule ta kaiwa mirror naushi take mirrorn ya tarwatse idonta takai ga T.v dake mak'ale a bango a guje ta k'arasa gaban T.v zaro shi tayi ta bugashi a Kan tiles d'in d'akin ya fashe haka komai dake d'akin ta shiga illata shi, hatta pillows da bedsheet sai da ta yi ta cilli dasu durowar kayanta ta bud'e ta dinga d'ebo kayan tana cillosu waje, a k'asa haka ta dingayi bayan ta gama zuar da kayan ta dinga binsu d'aya bayan d'aya ta yayyagasu ko wanne sai ta rabashi gida biyu sannan tayi cilli dashi gefe wad'anda taji sunyi Mata k'arfi a hannu sai ta saka hak'ori tayi masu hanya sannan ta k'arasa yagawa.bayan ta gama ne ta bud'e 'bangaren da akwatunan kayan lefenta suke,nan ma ta zuzzuge zif d'in akwatunan haka ta dinga wurgi da kayayyakin abubuwan fashewa na fashewa wad'anda ba na fashewa ba kuwa ta tattaka su.
'Bangaren Muhdeen kuwa tunda Sumayya ta fita daga d'akinsa ya zauna a bakin gadon gaba d'aya ya rasa mai ke damunsa.don yasan ko yabi Sumayya Dan ya rarrasheta ba sauraransa zatayi ba,hakan yasa ya d'an barta tukunna.Ya rasa me yasa Gwaggo zata yi masa haka zata sa ayi masa aure ba tare da amincewarsa ba,sannan ta rasa wacce zata say aura masa sai Inteesar yarinyar da ya tsana a rayuwar sa ita ce aka aura masa?lallai kuwa Inteesar ta tabka babban kuskure da ta yadda da wannan auren,Don wallahi sai ta d'and'ani kud'arta,daga ranar da ta shigo cikin gidan nan a matsayin matarsa daga ranar zata zatayi ban kwana da farin ciki.Yana cikin zancen zucin nasa ne yaji wani irin k'ara na tarwatsewar abu,cikin tashin hankali ya fito daga cikin d'akinsa ya nufi d'akin Sumayya.
Daga cikin d'akin Sumayya kuwa show glass d'in da aka jera Mata turararruka ne da su kwalaben humra da turararen wuta,lokacin da idonta ya sauka akan show glass d'inne ta nufesa tana k'arasawa ta d'auki k'arfen da da ke ajiye na rataya jakunkuna ,tana d'aukar k'arfen ne ta bugawa show glass ya tarwatse,k'arar show glass d'inne yaja hankalin Muhdeen ya nufo d'akin nata cikin tashin hankali.
Yana tura k'ofar yaji a datse ya shiga buga k'ofar Yana Kiran sunanta Amma Ina Bata ma San tanayi ba sai buge-buge da jefe-jefe takeyi tana Sam batu tayi nan tayi can duk abunda ya tari gabanta jifa dashi take,komai na d'akin ta gama hargiza wa ta fargasa duk abunda ya kasance na fashewa abu biyu ne a d'akin Wanda suke zaune a muhallinsu, durowar zuba kayanta sai gado suma don ba zata iya d'aukarsu bane hatta katifa tayi jifa dashi gefe.
Muhdeen ne koma d'akinsa ya d'auko key yazo ya bud'e k'ofar,ganinta ya yi kamar mahaukaciya duk ta fita hayyacinta ga hannayenta da taji ciwo.Suna had'a ido dashi ta d'aga masa hannu ta ce,
"out of my side"
Cikin tashin hankali ya ce,
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un"
k'awa tayi ta d'auki wani dogon fasasshen gilashi ta d'aga ta saita shi dai-dai saitin cikinta cikin d'aga murya ta ce,
"Kafita!"
Had'a hannayensa yayi alamar rok'o ya Fara magana
"Dan Allah ki tsaya ki saurareni,wallahi bada amincewa ta aka d'aura Mani aure da Inteesar ba."
Zaro ido tayi cikin cikin mamaki ta ce,
"Inteesar ka aura?"
Girgiza Kai tayi tana fad'in
"I said out, wallahi idan baka fita ba zan kashe kaina!"
Ta fad'i maganar tana saita tsinin kwalbar a cikinta.
Daga alk'alamin
Maman Ihsan
09065327995
Love u oll
*MAULUD MUBARAK*Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga.
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi ga kowa ba,idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba.Arashi ne Mai kashe auren wawa.
Page3
"I said out,wallahi idan baka fita ba zan kashe kaina!"
Ta fad'i maganar tana saita tsinin kwalbar a cikinta.
Ganin kamar da gaske take yasa ya fita falo gaba d'aya ya rasa me zaiyi.
Wauarsa ya ciro daga cikin aljihu, number Jabeer ya lalubo ya danna masa Kira,bayan Jabeer ya d'aga wayar ne muhdeen ya fara magana yana cewa
"Jabeer don Allah duk abunda kake ka ajiye shi kazo gidana yanzun nan."
bai jira cewarsa ba ya kashe kiran.Safa da marwa yake yana zaman jiran Jabeer.
Jin sallamar Jabeer ne yasa shi sakin ajiyar zuciya,k'arasowa yayi ya rik'e hannun Jabeer ya ce,
"Jabir ina cikin tashin"
Kallonsa Jabeer yayi cikin rashin fahimtar inda zancensa ya dosa ya fara magat
"Wai meke faruwa ne ne?"
"Ai komai ma ya faru"
"Kayi mani bayanin da zan gane inda zancenka ya dosa,ka kirani a waya kana cewa wai da sanina akayi maka aure wani irin aure kuma? dan Allah ka fitar dani haske domin kwata-kwata ban gane inda zancenka ya dosa ba."
Cikin 'bacin ran yanayin da ya ke ciki ya fara magana
"Jabeer aure suka k'ara yi mani,sati biyu da auren mu da my Sumy suka k'ara mani aure,jiya ana idar da sallar juma'a ne aka d'aura aure ba tare da sun nemi izini na ba kawai umarni suka bani inaji Ina gani aka d'aura auren.Jabeer wallahi bana son auren nan ba yadda zanyi ne."
Shiru Jabeer yayi yana nazarin maganar shikam baiji takaicin wannan auren da aka d'aurawa Muhdeen ba,don yasan cewa iyayen nasau sun lura da rashin tarbiyar Sumayya ce shiyasa aka nema masa masa wata matar.A cikin zuciyarsa yaji dad'in zancen don dama ba yadda baiyi dashi ba akan kada ya auri Sumayya amma soyayyarta ta riga da ta rufe masa ido ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa
"Wace ce matar da aka aura maka?"
Cikin takaici ya fad'i sunanta
"INTEESAR"
Gaban Jabeer ya fad'i Jin sunan Inteesar,take yaji wani Abu zuciyarsa har sai da wayar hannunsa ta su'buce masa ta fad'i k'asa.Sunanta ya ambata da k'arfi
"INTEESAR?"
Kai Muhdeen ya jinjina masa alamar eh
Shiru yayi na d'an lokaci kafin ya saki murmushi ya ce,
"Indai Inteesar ce na Taya ka murna samunta a matsayin mata,duk da na fahimci baka son aurenta amma Ina da yak'inin cewa zuwa gaba zakayi alfahari da ita."
Tsuki Muhdeen yayi
"Allah ya kiyaye kaima fa na lura da cewa a 'bangaren su Gwaggo kake."
Gajeren murmushi Jabeer yayi tare da cewa
"Ba zaka gane gata akayi maka ba sai nan gaba."
"Ba wani gata ni ba wannan yasa na kiraka ba,tunda my Sumy taji Ina fad'a maka zancen auren Inteesar har suma tayi Kai a rak'aice dai gata can a d'aki dai fashe-fashe takeyi."
Da mamaki Jabeer ya saki baki yana kallonsa
"Yanzu tana ina Wai?"
Tana d'akinta Kai tsaye suka nufi d'akin,k'wank'wasawa suka dingayi suna bata baki amma ina bata saurare su ba.Haka suka hak'ura inda Jabeer ya nuna masa cewa ya barta zuwa anjima idan ta d'an sauko sai suyi magana.
Daga haka ne Muhdeen yaja Jabeer zuwa d'akinsa inda Muhdeen ya shiga bathroom room don yin wanka inda yabar Jabeer zaune saman sofa yana jiransa.
Daga can d'akin Sumayyay kuwa tunda ta gaji taga bazata iya cigaba da yayyaga kayan ba.Hakan yasa sauran akwatunan kayan lefen auren ta dinga jansu tana kaiwa harabar gidan tana jibgesu,a haka har ta gama jidar kayan lefen auren bayan ta gama jibgasu waje guda ne ta d'aga kai ta hango Mai gadin gidan tare da Zayyanu Direban gidan suna kallonta,harara ta watsa masu tare da yi wa Zayyanu Direban alamun yazo manuniya,gabasa ne ya fad'i ganin ta kirasa don kallon mahaukaciya sukayi mata ganin yadda takeyi tsoro da fargaba ya hana Zayyanu k'arasawa wajenta sai da mai gadin yayi masa da alamar yaje,cikin tsoro ya k'arasa wajenta.magana tayi masa a kausashe ta ce,
"Kaje ka kawo mani fetur yanzun nan."
Da mamaki ya tsaya yana kallonta,
Tsawar da ta daka masa ne yasa yaba r wajen cikin rawar jiki,ba jimawa sai gashi ya dawo da fetur a cikin galan,amsa tayi tare da ce masa ya kawo mata ashana.k'arasawa yayi wajen mai gadin gidan ya amso mata ashana ya kawo mata.
Ga mamakinsu gani sukayi ta bud'e robar fetur d'in ta tsiyaya shi duka a jikin akwatunan kayan lefenta,sanan ta kyasta ashana ta jefa kai tsaye cikin gidan ta koma.
Jabeer dake zaune saman sofa ne ya hango bak'i ta jikin gilashin windows, mi'kewa yayi tare da d'an zuge gilashin window d'in,ganin hayak'in da ya turnik'e gidan ne yasa shi sakin salati dai-dai lokacin da Muhdeen ya fito daga wanka ganin hakan yasa cikin sauri ya saka Jallabiya suka nufi hanyar fita,don sun d'auka gobara ce.
Suna nufar inda suka ga hayak'in na tasowa turus suka tsaya ganin akwatuna da da kaya suna ci da wuta.
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un"
Kalmar da Muhdeen ya furta kenan.Jabir ya kalleshi tare da cewa
" ta yaya kuma me hakan yake nufi?"
Ajiyar zuciya Muhdeen ya sauke tare da cewa
"Sumayya ce ta k'ona kayan lefenta "
Cikin mamaki Jabeer ya ce,
"Kana nufin kayan lefen da kuka je Dubai kuka siyo da akwatunan sune ta bankawa wuta?"
Kai Muhdeen ya jinjina masa alamun eh.
"Tirk'ashi
Shine kalmar da Jabeer ya fad'a,sannan ya d'ora da cewa
"Gaskiya duk yadda nake tunananin Sumayya lamarinta ya wuce haka,ta wuce sanin tunanina.wannan ai hauka ne da rashin sanin darajar dukiya.kayan miliyoyin kud'in ne zata bankawa wuta?saboda mahaukacin kishi?