← Book details Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 99

Sashe 44

Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Daga alk'amin
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
Don k'arin bayani
09065327995
Love you oll
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izinina ba.

Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi ga kowa,idan suna ki hali yaso d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi t,arashi ne mai kashe auren wawa.
*BISIMILLAHI RAHMANI RAHEEM*
Page4
Haka ta fita kamar kazar da k'wai ya fashewa a ciki,ta fita ya bita da kallon banza.

A haka ta da jik'akkun kayan ta dinga aiki da su a jikinta,har suka bushe a jikinta ga sanyin da take ji ba yadda ta iya ahaka ta gama ayyukan gidan.

Kasancewar ba ya cin abincinta ya sa bata yi wani girki ba ta ruwan shayi kawai ta dafa ta sha,ta koma d'akinta lokacin rana ta riga da ta yi, wanka ta yi ta Sanya soguwar riga na atamfa wayarta ta soma ringing dubawa ta yi Usman ne daon haka Bata d'aga kiran ba har ya tsinke,wani tunani ta yi kodai ta d'aga ne tunda wannan auren ba mai d'orewa bane shi da kansa ya fad'a mata idan Sumayya ta dawo zai rabu da ita,don ba sonta ya ke ba tunanin hakan ne ya sa ta cewa bari ta d'aga kafin matarsa ta dawo ya ce zai sallame ta,d'aga wayar ta yi ta Kara a kunnenta.

"Assalamu Alaikum"
Daga can 'bangaren Usman da ke zaune a office d'insa ya saki ajiyar zuciya tare da furta.

"Wa'alaiki salam, har naji sanyi a Raina Inteesar azabtar da ni da kike ya yi yawa,baki san rashin ganinki da rashin jin muryarka ya hanani sukuni ba kullun da tunaninki nake kwana nake tashi,tunda muka had'u a sau uku nazo gidanku amma kika hana wai Abba ya hanaki,hakan ya sa na yi tunanin zuwa neman izinin zuwa zance a wurinsa."
Da sauri ta katse shi da cewa
"Kadai bari zuwa nan gaba kad'an amma ko ka same shi yanzun zai ce ka bari zuwa gaba kad'an ba jimawa,saboda haka idan olkaci ya yi da kaina zan sanar dake."
Hira suka ta'ba sosai na kusan mintuna talatinl,sai da ya ji ana knocking sannan ya mata sallama ya ajiye wayar,sannan ya bada izinin shigowa.

Ita kuma sanin cewa jiya abokan mijinta suka ce yau zasuzo ne ya sa ta mi'ke ta nufi kitchen don d'aura masu girki.

Jallop d'in cuscus ta da white rice and stew da ta ji naman rago,sai pepper chicken da tayi masu da farfesun d'anyar kifi da ta yi masu ga lafiyayyan juice na kwakwa da madara,ta had'a masu girkuna masu gidan ya cika da k'amshin girkinta ya cika gidan.

Komawa d'akinta tayi ta fad'a toilet ta sake sabon wanka sake ta shirya cikin doguwar riga na less d'inki bubu ya kar'bi jikinta,dama ita bata damu da kwalliya ba,don haka bayan ta shafa man shafawarta na wajen Hajiya Bilkisu, powder kawai ta shafa sai man baki,ta saka sark'a da d'an kunne,gasjin kanta ta tufke shi a tsakiyar kanta,zama ta yi baki gadon tare da d'aukar wayarta tana buga game.

Gidansu Inteesar kuwa koda Abbanta ya dawo kasuwa yammaci ne lik'is hannunsa d'auke da leda mai layin yellow da bak'i, Dankalin hausa ne a cikin ledan da sallama ya shigo gidan , Umma da ke zaune gaban murhun itace tana tuk'a tuwo ne ta amsa masa sallamar,sakin muciyar ta yi da niyyar tashi ta kar'bo ledar,hannu ya d'aga mata alamar ta barshi .

"Zauna ki cigaba da aikinki Umman Inteesar"
Murmushi ta yi tare da cewa
"Sannu da zuwa ya kasuwar?"
"Alhamdulillah an godewa Allah."
Zama ya yi kan tabarman da ke shimfid'e a k'ofar d'akinsa.

Bayan Umman Inteesar ta gama tuk'a tuwon ne ta tashi ta d'auki kofin silver da murfinsa ta d'ebo masa ruwa,a cikin randar k'andar k'asa me sanyi gabnsa ta ajiye tare da k'ara masa sannu da zuwa,bayan yasha ruwan ne ya mi'ke tare da cewa
"Bari na tashi nayi wanka na tafi masallaci, lokacin salla ya k'arato.

Mi'kewa ya yi yayin da Umma dama ta ajiye masa ruwan wanka a cikin tukunyar da suke dafa ruwan zafi,juyewa ta yi a cikin bokinti ta surkar masa da ruwan sanyi ta kai masa bad'aki ya fito daga cikin d'akinsa ya shiga band'akin
Bayan sallar isha'i ne bayan ta dawo daga masallaci yana zaune a Kan tabarma Umma ta kawo masa tuwo,ya ci ya gama ta ce ,
"Mallam Inteesar sunzo da mijinta d'azun da rana kana kasuwa."
Zuba ma Umma ido yayi fuskarsa d'auke da murna duk da bai ganta ba amma ya ji dad'in zuwanta gidan.

"Masha Allah da nasan zata zo da na bari sai na ganta kafin na tafi,suna dai lafiya ba wata matsala ko?"
"Wannan ne kuma ban sani ba mallam"
"Kamar ya baki sani ba da tazo me yasa baki tambaye ta ba ko awai wata damuwa."
Shiru Umma ta yi tana tunanin yanayin da taga Inteesar,ita ta haifeta tafi kowa saninta a duniyarnan,amma ganin yanayin da ta ganta ko shakka babu akwai abunda ke damunta,dalilin da yasa bata d'aga hankali ba tasan cewa wasu lokutan auren had'i idan har basa son junansu sukan sawa kansu damuwa da tunani saboda ba wannan ne a zuciyarsa ba,wannan dalilin yasa Mummy kauda ido.

"Mallam ta ce mani suna zaune lafiya."
Jinjina kai yayi
"Masha Allah"
Umma ta mik'e ta shiga d'aki ta fito hannunta d'auke da kud'in da Muhdeen ya bata mik'a masa tare da cewa
"Mijinta ne ya kawo muna kayan abinci masu yawa tare da kud'in nan."
Kallon kud'in Abba ya yi sannan ya kalli Umma ya ce,
"Harda d'awainiya haka?da baki kar'bi kod'insa ba"
"Nima banso kar'ba ba ajiyewa ya yi"
Yana zaune akan kujera Yana jiran isowar abokansa,wayarsa ta fara ruri,dubawa ya yi yaga Dadynsa ne,d'aga wayar ya yi tare da cewa
"Assalamu Alaikum"
Daga d'aya 'bangaren
"Wa'alaika salam Muhammad kana gida ne?"
"Eh Dady ina gida ina jiran su Jabeer ne zasu zo."
"Okay to ga Gwaggo nan ta shirya kayanta ta ce lallai sai dai na kira ka kazo ka d'auke ta zuwa gidanka."
Gaba d'aya hankalin Muhdeen ya tashi,don yasan zuwa sa masa ido kawai Gwaggo zata yi ba wai don ziyara ba,yanzun ya zaiyi da wannan tsohuwar ba,ta zame masa matsala,yana cikin tunani ya jiyo muryar Dady na cewa
"Ya kayi shiru lafiya kuwa?"
Ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa
"Gani nan zuwa Dady"
Tsuki ya ja tare da d'aukar wayarsa kamar ya ba Direba ya d'auko ta,ya tuna kira Mahaifinsa ne don haka ya ta fi da kansa.

Yana driving akan hanyarsa ta zuwa d'aukota ne wayarsa ta soma ruri dubawa ya yi yaga Sumayya ce, ba shiri yayi parking a gefen titi ya amsa wayar cikin farin ciki.

"Hello Baby sai yau kika Kira ni tunda kika tafi sai ma kika sakani a blacklist ko?"
Jin sautin kukanta ya ke harda sheshshek'ar kukanta,rintse ido ya yi sakamakon jin sautin kukan nata.

Kinga kunga dan Allah ki daina kukan nan hakanan muyi magana.

"Ba dole nayi kuka ba tunda na tafi ba ka damu Dani ba ka mance dani saboda kana tare da wannan yarinyar da parents d'inka suka aura maka."
Kinga da kinsan irin zaman da nake yi da yarinyar nan a gidan nan ko?da baki fad'i haka ba,ni fa wannan auren ban d'auke shi aure ba tunda taso gidan nan wallahi ko kallo bata ishe ni ba zaman gidan nan dai-dai yake da zaman gidan wak'afi a wajenta."
Dakatar da kukanta ta yi tare da cewa
"Kana nufin ba abunda ya shiga tsakaninka da ita?'
"K'warai kuwa ko hannunta ba ta'ba rik'ewa ba ballantana wani abu ya shiga tsakaninka mu,kuma zaman da take a gidan nan ki d'auka 'yar aiki ce na kawo maki,zata kasance mai maki ko wani irin aiki da bin umarninki."
Dariyar mugunta ta yi tare da cewa to
"Gobe ma zan dawo"
Shiru ya ya yana nazari kafin ya ce,
"Dawowarki gobe akwai matsala ki bari sai bayan wata d'aya ki dawo?"
Sakin baki tayi cikin mamaki ta ce,
"Baby anya kuwa kana sona yanzun?"
"Ba abunda ya ragu cikin son da nake maki."
"To me zaisa ka ce na bari sai bayan wata d'aya na dawo alhalin ina nan na matsu na ganka kana cewa one month."
"Abunda ya sa kika ji na ce haka yau Gwaggo zata zo gidan nan kuma idan tazo sai ta yi one month kafin ta tafi,Kinga kuma zamanki da Gwaggo a gida d'aya akwai matsala,kuma kunga matuk'ar tana cikin gidan nan bazan ta'ba k'untatawa rayuwar Inteesar ba dole na d'aga mata k'afa bazan cutar da ita ba har sai bayan Gwaggo tabar gidan."
Shiru ta yi tana nazari kafin ta d'aura da cewa
"Bakomai amma gaskiya ka samu lokaci kazo na matsu na ganka kafin lokacin tafiyar Gwaggo ya zo."
Murmushi ya yi tare da cewa
"Karki damu zamuyi waya anjima."
Tana zaune a falonta tana tunanin yanayin rayuwar da take ciki,tana kuma tuna yanayin rayuwar da take ciki kafin aurenta.

Turo k'ofar aka yi taga Ishaq direba ne da akwati a hannunsa,tana kallon akwatin ne ta ji muryar Gwaggo na cewa
"Ina 'yar albarka take?"
A guje ta nufi k'ofar tana dariya,akan barandar shiga falon ne taga Gwaggo da Muhdeen, rungume Gwaggo ta yi da k'arfi kamar zata shige jikinta.

"Yar albarka bini a hankali k'afar ba lafiya"
Jin hakan yasa ta d'an sassauta tare da cewa
" Oyoyo Gwaggo"
"Okay wato ganin Gwaggo yasa kin mance da ni ko?oyoyon da ake mani ma yanzu ban samu ba saboda Gwaggo ko?"
Tsayawa ta yi tana kallonsa cikin mamamki,a zuciyarta ta ke cewa yanzun zai fara amfani da fuska biyu kenan.
Chapter 44 · 0% Book details