Sashe 21
Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Koda suka k'araso harabar gidan duka motocin gidan ba ko d'aya duk an tafi dasu tundaga Kan motar Mummy har Motocin Muhdeen ba ko d'aya .Domin duk an tafi wajen reception motar Jabeer kawai suka gani sai motar Asiya wacce fitowarta kenan daga cikin gidan ita da k'awayenta guda biyu,tana k'arasowa ta kallesu tace,
"Au kuma baku tafi ba?"
Mufida ce ta kalleta tace,
"Wallahi bamu tafi ba tunda gaki sai mu biki"
girgiza Kai tayi tare da cewa,
"Sai dai dukkanku motar ba zata d'uke mu duka ba,don ga friends d'ina guda biyu sannan ga ku hud'u kinga sai dai mutum d'aya ta hak'ura ta hau keke napep"
Mufida ta kallesu ta ce,
"Badamuwa ni zan hau napep ku ku shiga motar."
Kai Asiya ta girgiza
"A'a sai dai Inteesar ta hau napep don bazaiyuwu ba kibar su Azeeza baku tare."
"Gaskiya Inteesar ba zata hau napep ba."
'Daga kafada Asiya tayi alamun I don't care d'innan sannan ta kalli Mufida ta ce,
"Shikenan sai ku tafi daga ke har ita kuhau napep d'in."
Dai -dai lokacin Muhdeen ya fito tare da Jabeer,Jin abunda suke fad'a yasa Jabeer tambayarsu.
"Wace ce zata shiga napep?"
Mufida ta ce
"Motar ce bazata d'auke mu duka ba saura mutum d'aya."
Idanun Jabeer ne suka akan Inteesar ya zuba Mata idanu ba ko k'yaftawa,gaba d'aya ta tafi da hankalin sa ya kasa d'auke idanunsa akan kyakkywan surar jikinta.Muhdeen ya lura da kallon da Jabeer ke mata hakan yasa ya buge masa hannu Wanda yasa shi dawowa hayyacinsa.Muhdeen ya baibi ta kansa ba ya wuce ya shige bayan motar ya zauna.
Jabeer ya kalli Inteesar ya ce,
"Inteesar kizo mu tafi a motata"
Kallon Mufida tayi,sai Mufida tayi mata alamun taje ta shiga.Hakan yasa tabi baynsa inda ya bud'e Mata marfin gabar motar ta shiga ta zauna.Mufida kuwa suka shiga na Asiya.Cikin sanyi murya ta ce,
"Nagode"
Murmushi Jabeer ya sakar mata tare da cewa
"Bakomai Inteesar."
Muhdeen ne ya had'e fusaka ya ce,
"Motar da zaka d'auki Amarya da Ango ne zaka d'auki wannan kucakar yarinyar to aiko sai dai ta fita."
Jabeer ne yayi masa irin kallon nan na kayi kad'an sannan yace,
"Wallahi bazata fita daga motar Nan ba sai dai Kai ka fita."
09065327995Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi
( Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*BISMILLAHIR RAHMANI RAHIM*
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin Rubuta ta Shi Dan cinzarafi ga kowa ba.idan suna ko hali yazo daya to KU gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba, arashi ne mai kashe auren Wawa.
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce,don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga.
Page2
"Wallahi ba zata fita daga motar nan ba sai dai Kai ka fita."
Kallon mamaki Muhdeen yayiwa Jabeer don Bai ta'ba tunananin jin wannan maganar daga bakin Jabeer ba.
"Yanzun akan wannan yarinyar kake fad'a Mani magana?don kaga friends d'ina sau d'auki motacina zasuyi amfani dashi basoda nace zanbi naka kai ka isa ka fad'a mani mota?kaima kasan motocin da nake hawa sunfi naka, ballantana ka fad'a Mani magana"
Murmushi Jabeer ya ce
"Bakomai ai zakaranka rak'uminka,kardai ka 'bata ranka a banza a wofi don yanzun zamuje mu d'auko maka amaryarka tana zaune gefenka yayin da ni kuma Inteesar tana zaune a gefe na."
Banza dashi Muhdeen yayi bai tanka masa ba, yayinda Jabeer kan d'an ja Inteesar da fira,duk da ba wani biyeshi yakeyi ba idan daga eh sai A'a, a hakan har suka k'araso k'ofar gidan su Sumayya amarya nan suka tarar da d'aya daga cikin motocin Muhdeen a k'ofar Get d'in gidan,wanda abokin ango Bilyaminu ne ya tukota don d'aukar 'kawayen amarya.Bayan ansaka amarya cikin motar da ango ke ciki ne sauran k'awayenta suka shiga motar da Bilyaminu ya tuk'o,daya nan suka d'au hanya.Amarya kuma ta shiga Motar Jabir inda ta zauna kusa da angonta.K'amshin turarenta ne ya gauraye cikin motar murmushi suka sakarwa junansu .Jabir ne ya kalleta ta cikin mirror d'in dake cikin motar ya ce,
"Amarya bakya laifi"
Murmushi tayi tana fad'in
"Koda na kashe d'an masu gida"
Amsa ya maida Mata da cewa,
" A'a sai dai idan baki kashe ba,"
Share shi tayi kamar bataji abunda yake fad'a ba,ta mayar da idanunta wajen duban angon nata cikin tsananin k'unarsa ta sakar masa murmushi cike da son sa ta ce,
"Kayi kyau my heart"
Murmushi ya mayar mata
"Ai ban kaiki kyawu ba"
Inteesar ce ta bud'e baki ta gaishe ta
"Anty sumayya ina wuni"
Dai -dai lokacin da Jabeer yaja mota suka bar wajen,sumayya cike da mamaki da takaici ta ce,
"Wannan ba yarinyar nan bace, Inteesar?"
Jabeer ne ya bata yayinda idanunsa ke kan hanya yana cigaba da tuk'i ya ce,
"Itace mana dama kinsanta ne?"
Ba tare da ta bashi amsa ba ta cigaba da magana
"To me yasa ta biyo ku batabi sauran jama'ar sun wuce ba?dole sai motar da ango da amarya zasu tafi shi zata bi a matsayinta na wa?"
"A matsayinta na mutum 'yar mutuwa,jikar rasuwa,kakar jana'iza.kamar yadda babu Wanda yafi wani a wurin Allah sai wanda yafi tsoron sa."
Shiru tayi ta cika tayi fam cike da takaici.
Kalaman Jabeer d'in kamar yana jirace da ita.Dama ta dad'e da zargin cewa Jabeer baya k'aunarta a tare da Muhdeen,kuma taci alwashin sai ta raba tsakanin su,bata gama tunanin da takeyi a cikin zuciyarta ba taji maganar Muhdeen yana cewa Jabeer
"Wai kai Jabeer me yake damunka ne? so kake sai ka gusar mana da farin cikin da ke cikin zuciyarmu ne? ya kake neman ka dinga gayawa mutane magana san ranka ne?ko ko don kaga an shiga motar ka ne zaka nemi gaya mana maganar banza?dama kace da abokaina su d'auki motocina suyi zurga-zarga dasu ne dan kaci mana mutunci?
To yanzun kayi parking nan mu sauka mubar maka motarka,zansa yanzun a kawo muna mota,kana ta faman gayawa mutane magana akan wannan kucakar yarinyar."
Murmushi Jabeer yayi tare da cewa,
"Idan ko zaka kira Inteesar kucaka ashe ko duka 'yan matan duniyar nan kucakai ne.don idan za'a tara mata d'ari to dakyar za'a samu biyar biyar kamarta."
Ganin ransu yayi matuk'ar 'baci ne yasashi cewa
"Kuyi hak'uri wallahi banida niyyar'bata muku rai,ku gafarceni."
Ba Wanda ya sakeyiwa kowa magana magana har suka k'arasa wajen reception d'in inda aka gudanar da komai cikin tsari,inda amarya da ango suka zauna wajen zaman su aka rera masu wak'a aka rak'ashe aka lik'a nairori.bayan antashi ne, Muhdeen ya ce,shi bazai shiga motar Jabeer ba inda Salisu ya d'auke su a d'aya daga cikin motocin Muhdeen d'in.Inteesar kuwa dole ta sake bin Jabeer Don komawa gida.
Akan hanyarsu ta komawa gida ne, Maryam matar Jabeer ta kirashi a waya Wai tana son shan agwaluma dan Allah ya siyo mata.bayan ya gama amsa wayar ya juya ya kalli Inteesar sannan ya maida dubansa ga driving d'in da yake yi ya ce,
"Don Allah kid'anyi hak'uri zamu d'an biya wani waje na siyawa mata ta agwaluma sai mu biya nakai mata."
Da sauri Inteesar ta kalle shi tare da cewa,
"To amma da ka ajiyeni anan sai na samu napep na k'arasa gida don bazan iya binka gidanka ba."
"Saboda me kina tsoron kada na cutar dake ko?"
Shiru tayi ta sunkuyar da kanta k'asa tana wasa da zara-zaran yatsun hannunta da suka sha jan lalle.Batare da ya kalleta ba ya sake jefa mata wata tambayar.
"Zaki yarda ki rakani ko?"
Nanma shiru tayi tana tunani, ita dai yau ta fara ganinsa lokacin da ya k'wace ta a hannun Muhdeen.Sai dai taji Mufida ta kira shi da Yaya Jabeer,kuma tana yawan jin sunan sa a bakin Mufida ko ranar da tayi rashin lafiya da su Mummy suka zo gaisheta taji Mufida na cewa daga gidan Yaya Jabeer suke wai d'an wan Mahaifinsu ne.sai dai duk da haka baikamta tabishi gidansa ba to amma kuma yana da mata kuma taji sanda matar take fad'a masa ya siyo Mata agwaluma Amma ya dace ta bishi kuwa?dama tare da Mufida suke ba zata damu ba.
"Au kuma baku tafi ba?"
Mufida ce ta kalleta tace,
"Wallahi bamu tafi ba tunda gaki sai mu biki"
girgiza Kai tayi tare da cewa,
"Sai dai dukkanku motar ba zata d'uke mu duka ba,don ga friends d'ina guda biyu sannan ga ku hud'u kinga sai dai mutum d'aya ta hak'ura ta hau keke napep"
Mufida ta kallesu ta ce,
"Badamuwa ni zan hau napep ku ku shiga motar."
Kai Asiya ta girgiza
"A'a sai dai Inteesar ta hau napep don bazaiyuwu ba kibar su Azeeza baku tare."
"Gaskiya Inteesar ba zata hau napep ba."
'Daga kafada Asiya tayi alamun I don't care d'innan sannan ta kalli Mufida ta ce,
"Shikenan sai ku tafi daga ke har ita kuhau napep d'in."
Dai -dai lokacin Muhdeen ya fito tare da Jabeer,Jin abunda suke fad'a yasa Jabeer tambayarsu.
"Wace ce zata shiga napep?"
Mufida ta ce
"Motar ce bazata d'auke mu duka ba saura mutum d'aya."
Idanun Jabeer ne suka akan Inteesar ya zuba Mata idanu ba ko k'yaftawa,gaba d'aya ta tafi da hankalin sa ya kasa d'auke idanunsa akan kyakkywan surar jikinta.Muhdeen ya lura da kallon da Jabeer ke mata hakan yasa ya buge masa hannu Wanda yasa shi dawowa hayyacinsa.Muhdeen ya baibi ta kansa ba ya wuce ya shige bayan motar ya zauna.
Jabeer ya kalli Inteesar ya ce,
"Inteesar kizo mu tafi a motata"
Kallon Mufida tayi,sai Mufida tayi mata alamun taje ta shiga.Hakan yasa tabi baynsa inda ya bud'e Mata marfin gabar motar ta shiga ta zauna.Mufida kuwa suka shiga na Asiya.Cikin sanyi murya ta ce,
"Nagode"
Murmushi Jabeer ya sakar mata tare da cewa
"Bakomai Inteesar."
Muhdeen ne ya had'e fusaka ya ce,
"Motar da zaka d'auki Amarya da Ango ne zaka d'auki wannan kucakar yarinyar to aiko sai dai ta fita."
Jabeer ne yayi masa irin kallon nan na kayi kad'an sannan yace,
"Wallahi bazata fita daga motar Nan ba sai dai Kai ka fita."
09065327995Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi
( Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*BISMILLAHIR RAHMANI RAHIM*
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin Rubuta ta Shi Dan cinzarafi ga kowa ba.idan suna ko hali yazo daya to KU gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba, arashi ne mai kashe auren Wawa.
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce,don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga.
Page2
"Wallahi ba zata fita daga motar nan ba sai dai Kai ka fita."
Kallon mamaki Muhdeen yayiwa Jabeer don Bai ta'ba tunananin jin wannan maganar daga bakin Jabeer ba.
"Yanzun akan wannan yarinyar kake fad'a Mani magana?don kaga friends d'ina sau d'auki motacina zasuyi amfani dashi basoda nace zanbi naka kai ka isa ka fad'a mani mota?kaima kasan motocin da nake hawa sunfi naka, ballantana ka fad'a Mani magana"
Murmushi Jabeer ya ce
"Bakomai ai zakaranka rak'uminka,kardai ka 'bata ranka a banza a wofi don yanzun zamuje mu d'auko maka amaryarka tana zaune gefenka yayin da ni kuma Inteesar tana zaune a gefe na."
Banza dashi Muhdeen yayi bai tanka masa ba, yayinda Jabeer kan d'an ja Inteesar da fira,duk da ba wani biyeshi yakeyi ba idan daga eh sai A'a, a hakan har suka k'araso k'ofar gidan su Sumayya amarya nan suka tarar da d'aya daga cikin motocin Muhdeen a k'ofar Get d'in gidan,wanda abokin ango Bilyaminu ne ya tukota don d'aukar 'kawayen amarya.Bayan ansaka amarya cikin motar da ango ke ciki ne sauran k'awayenta suka shiga motar da Bilyaminu ya tuk'o,daya nan suka d'au hanya.Amarya kuma ta shiga Motar Jabir inda ta zauna kusa da angonta.K'amshin turarenta ne ya gauraye cikin motar murmushi suka sakarwa junansu .Jabir ne ya kalleta ta cikin mirror d'in dake cikin motar ya ce,
"Amarya bakya laifi"
Murmushi tayi tana fad'in
"Koda na kashe d'an masu gida"
Amsa ya maida Mata da cewa,
" A'a sai dai idan baki kashe ba,"
Share shi tayi kamar bataji abunda yake fad'a ba,ta mayar da idanunta wajen duban angon nata cikin tsananin k'unarsa ta sakar masa murmushi cike da son sa ta ce,
"Kayi kyau my heart"
Murmushi ya mayar mata
"Ai ban kaiki kyawu ba"
Inteesar ce ta bud'e baki ta gaishe ta
"Anty sumayya ina wuni"
Dai -dai lokacin da Jabeer yaja mota suka bar wajen,sumayya cike da mamaki da takaici ta ce,
"Wannan ba yarinyar nan bace, Inteesar?"
Jabeer ne ya bata yayinda idanunsa ke kan hanya yana cigaba da tuk'i ya ce,
"Itace mana dama kinsanta ne?"
Ba tare da ta bashi amsa ba ta cigaba da magana
"To me yasa ta biyo ku batabi sauran jama'ar sun wuce ba?dole sai motar da ango da amarya zasu tafi shi zata bi a matsayinta na wa?"
"A matsayinta na mutum 'yar mutuwa,jikar rasuwa,kakar jana'iza.kamar yadda babu Wanda yafi wani a wurin Allah sai wanda yafi tsoron sa."
Shiru tayi ta cika tayi fam cike da takaici.
Kalaman Jabeer d'in kamar yana jirace da ita.Dama ta dad'e da zargin cewa Jabeer baya k'aunarta a tare da Muhdeen,kuma taci alwashin sai ta raba tsakanin su,bata gama tunanin da takeyi a cikin zuciyarta ba taji maganar Muhdeen yana cewa Jabeer
"Wai kai Jabeer me yake damunka ne? so kake sai ka gusar mana da farin cikin da ke cikin zuciyarmu ne? ya kake neman ka dinga gayawa mutane magana san ranka ne?ko ko don kaga an shiga motar ka ne zaka nemi gaya mana maganar banza?dama kace da abokaina su d'auki motocina suyi zurga-zarga dasu ne dan kaci mana mutunci?
To yanzun kayi parking nan mu sauka mubar maka motarka,zansa yanzun a kawo muna mota,kana ta faman gayawa mutane magana akan wannan kucakar yarinyar."
Murmushi Jabeer yayi tare da cewa,
"Idan ko zaka kira Inteesar kucaka ashe ko duka 'yan matan duniyar nan kucakai ne.don idan za'a tara mata d'ari to dakyar za'a samu biyar biyar kamarta."
Ganin ransu yayi matuk'ar 'baci ne yasashi cewa
"Kuyi hak'uri wallahi banida niyyar'bata muku rai,ku gafarceni."
Ba Wanda ya sakeyiwa kowa magana magana har suka k'arasa wajen reception d'in inda aka gudanar da komai cikin tsari,inda amarya da ango suka zauna wajen zaman su aka rera masu wak'a aka rak'ashe aka lik'a nairori.bayan antashi ne, Muhdeen ya ce,shi bazai shiga motar Jabeer ba inda Salisu ya d'auke su a d'aya daga cikin motocin Muhdeen d'in.Inteesar kuwa dole ta sake bin Jabeer Don komawa gida.
Akan hanyarsu ta komawa gida ne, Maryam matar Jabeer ta kirashi a waya Wai tana son shan agwaluma dan Allah ya siyo mata.bayan ya gama amsa wayar ya juya ya kalli Inteesar sannan ya maida dubansa ga driving d'in da yake yi ya ce,
"Don Allah kid'anyi hak'uri zamu d'an biya wani waje na siyawa mata ta agwaluma sai mu biya nakai mata."
Da sauri Inteesar ta kalle shi tare da cewa,
"To amma da ka ajiyeni anan sai na samu napep na k'arasa gida don bazan iya binka gidanka ba."
"Saboda me kina tsoron kada na cutar dake ko?"
Shiru tayi ta sunkuyar da kanta k'asa tana wasa da zara-zaran yatsun hannunta da suka sha jan lalle.Batare da ya kalleta ba ya sake jefa mata wata tambayar.
"Zaki yarda ki rakani ko?"
Nanma shiru tayi tana tunani, ita dai yau ta fara ganinsa lokacin da ya k'wace ta a hannun Muhdeen.Sai dai taji Mufida ta kira shi da Yaya Jabeer,kuma tana yawan jin sunan sa a bakin Mufida ko ranar da tayi rashin lafiya da su Mummy suka zo gaisheta taji Mufida na cewa daga gidan Yaya Jabeer suke wai d'an wan Mahaifinsu ne.sai dai duk da haka baikamta tabishi gidansa ba to amma kuma yana da mata kuma taji sanda matar take fad'a masa ya siyo Mata agwaluma Amma ya dace ta bishi kuwa?dama tare da Mufida suke ba zata damu ba.