Sashe 58
Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai ta d'aga mata alamar eh
Murmushi tayi tare da cewa
"Ki k'ara hak'uri akan wanda kikayi a baya, da zaran ya shigo hannunki sai yadda kikayi dashi, saboda Allah ya baki wata irin baiwa wanda mijinki bai san da shi ba, amma da zaran ya San da hakan to wallahi kinfi k'arfin wulak'anci a wajensa, domin samun mace irinki yana da matuk'ar wahala kuma duk namijin da ya same ki kingama mallake zuciyarsa sai yadda kikayi da shi."
Zuba mata ido Aunty Abla tayi kafin ta ce,
"K'awa ta ta k'ara hak'uri zuwa yaushe? sai ta cigaba da zama cikin bak'in ciki da k'unci wanda ba'asan ranar wucewarsa ba?"
"Kada ki damu nan bada dad'ewa komai zai zamo labari, idan kinyi nazari a cikin labarin da ta bayar ai zaki fahimci ya fara sha'awar kusantarta, tunda ya fara kuwa bai wuya zai shiga hannunta sai yadda tayi dashi."
Kallon inteesar tayi tare da cewa
"Duk ranar da ya nemi kusantarki kada ki k'ara guje masa kamar yadda kikayi a baya."
Da sauri ta kalle ta
"Eh hakan zakiyi ba ki da wani za'bi
Daga alk'alamin
Zainab Abdullah K.N T
(Maman Ihsan)
Don Karin bayani
09065327995
Love you oll
Comments and shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullah K.N.T
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izinina ba.
*SANARWA*
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubuta shi dan cin zarafi ga kowa ba, idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarce ni bada niyyar yin hakan nayi ba, arashi ne mai kashe auran wawa.
*BISIMILLAHI RAHMANI RAHEEM*
Page5
"Duk ranar da ya nemi kusantarki kada ki k'ara guje masa kamar yadda kikayi a baya."
Da sauri ta kalle ta
"Eh hakan za'ayi baki da wani za'bi"
Tura baki tayi tare da cewa
"Shifa ya ce baya sona kuma da zarar matarsa ta dawo gidan nan zai rabu da ni, to kuma mutumin da baya k'auna ta zan bawa kaina? ya raba ni da budurci na fa kenan sannan ya rabu dani."
Ta k'arasa maganar tana sunkuyar da kanta k'asa,
Dariya sukayi dukansu, Aunty Abla ta d'ora da cewa
"Wa ya fad'a maki zai rabu dake?"
"Shine da bakinsa ya fad'a mani fah."
"Ya dai fad'a ne amma bai isa ya rabu da ke ba, domin rabuwa da ke tamakar bijirewa iyayensa yayi, kuma nasan shi yana da biyayya bazai iya bijirewa maganarsu ba, don haka idan kina tunannin zai rabu dake be to ki daina, kisan yadda zakiyi ki mallaki zuciyarsa kawai."
"Nima fa ba sonsa nake ba, jira nake ya rabu dani kawai na koma gidanmu."
Murmushi kawai Aunty Abla tayi tare da cewa
"To kiyi ta addu'a duk abunda yafi zama alkhairi a gare ki Allah ya tabbatar maki da shi."
Daga nan Hajiya Bilkisu ta bud'e jakkarta ta fito da wasu goruna guda uku, ta mik'awa inteesar d'aya kar'bi ki shanye shi nan da kwana uku safe da yamma zaki dinga sha."
Ta d'auko wani goran ta mik'a mata ta ce,
"Wannan rubutun kuma ki shanye shi yanzun nan ki bani goran."
Ba musu ta kar'ba tare da yin Bisimillah ta shanye ta mik'a mata goran, sai ta mik'a mata cikon ta ukun tare da cewa
"Wannan zumar kuma zaki sha cokali d'aya a rana, sai kuma washe gari sau d'aya ake sha a rana saboda yana da k'arfi."
Jakarta ta bud'e ta fito da wani turare ta ce,
"Wannan dai kinsan irinsa na tsugunno ne, na maki amfani da shi lokacin kina gida na."
Ta ciro wasu ta ce
"Wad'annan turarurruka ne da sabulun wanka ki dinga amfani da su kowane lokaci."
Nasiha suka k'ara mata da shawarwari suka k'ara bata hak'uri, sannan sukayi suka tafi, har zata raka su suka ce ta yi zamanta komawa tayi ta kwanta.
A falo suka samu Muhdeen yana waya, ganinsu yasa ya katse kiran tare da cewa
"Aunty har kun fito?"
Hajiya Bilkisu ce tayi masa sallama ta fice, yayin da Aunty Abla ta zuba masa ido ba tare da ta ce komai ba, tunani ya shiga yi ko dai inteesar ta kai k'ararsa ne? bai gama tunani ba ya ji murayar Aunty Abla na cewa
"Son kaji tsoron Allah yarinyar nan inteesar amana ce a wajenka, kamar yadda ba'ayi shawara da kai ba aka d'aura maka aure da ita haka itama, ba'ayi shawara da ita ba aka aura mata kai, hak'uri zakayi da ita ko baka sonta ka kyautata mata ka sauke duk wani hakki nata da Allah ya d'ora maka, kada kaga cewa ita waccan soyayya ce ta had'aku ka fifita ta akan inteesar, Allah yana ji kuma yana ganinka kuma zai tambaye ka, kafa ka tashi a ranar tashin alk'iyama 'barin jikinka yana karkata, ka sani kake sani, bata kowa sai ta baro gidan iyayenta saboda kai kada ka wulak'anta ta."
Daga nan bata sake magana ba tayi ficewarta, don har ga Allah taji zafin abunda yakewa inteesar a baya, musamman da ta tuna cewa farkon aurensu ya dinga wahalar da ita ba tausayawan alhalin bata masa laifin komai ba.
Cikin sanyin jiki ya koma kan kujera ya zaun, yana tunanin maganganun da Aunty Abla ta sanar da shi kuma yasan tabbas bai kyautawa inteesar ba, a d'an zamansa da ita ba wani abu na kyautatawa ko adalci da ya mata, sai musguna mata da wahalar da ita da yayi, kuma yasan tabbas a halin yanzun idan ya ce zai kwatanta adalci a tsakaninsu to za'a samu matsala da Sumayya, domin sai da ya sanar da ita cewa inteesar kamar mai aiki ce aka kawo mata ba kishiya ba kuma ko kallo bata ishe sa ba sannan ta yadda ta dawo, tunda ba abunda ta iya inteesar ce zata dinga mata.
Mik'ewa yayi ya nufi d'akinta, tura k'ofar d'akin yayi ya shiga da sallama, d'agowa tayi da sauri ta kalle shi cike da fargabar me zai biyo baya, ta dai san arziki da alkhairi baya sa ya shigo d'akinta, idan ya shigo to wani muguntar be zai mata, a zuciyarta ta ce, na shiga uku me kuma nayi masa ya biyo ni d'aki na? ko dai aikin wahalar ne zan cigaba tunda Gwaggo ta tafi, sannan wannan ne karo na farko da ya shigo da sallama a d'akinta, cikin sanyin muryarta ta ce,
"Wa'alaika salam"
K'arasowa yayi gabanta ya ce,
"Wace magana kukayi da su Aunty Abla?"
Gabanta ne ya fad'i amma sai ta dake ta ce
"Bakomai"
Zuba mata Ido yayi yana karantarta kafin ya ce,
"Akwai yanayin maganarta ya tabbatar mani da cewa akwai maganar da kika fad'a mata, wato ke baki iya rik'e sirrin gidanki ko?"
"Ba abunda na fad'a mata ta ce,wai na rame ne "
Shiru yayi sannan ya d'ora da cewa
"Mata ta dai ta dawo yau, saboda haka kiyi mata biyayya a matsayinta na uwar gida wacce kika zo kika tarar, dole ki girmama ta,bayan haka kuma ko a shekaru ba tsaranki bace ta girme maki nesa ba kusa ba, sannan kuma ita ta taso daga gidan iyayenta bata aikin komai masu aiki ke mata gyaran d'aki da girki bata komai sai dai ayi mata bata iya ba, kuma ni bana son ace 'yar aiki zata girka abincin da zanci, kuma bana son ace 'yar aiki zata shiga ta gyara mani bedroom, shine nake neman alfarma a wajenki da ki dinga taimaka mata da ayyukan tunda bata iya komai ba, kinga matsayin ya take a gare ki shekarunta talatin ke kuma shekarunki goma Sha takwas kinga ai ta cancanci kiyi mata ko?"
Shiru tayi tana nazari ba tare da ta ce, komai ba, ganin shirun nata yayi yawa ne yasa shi cewa
"Kinsan cewa na tsani shariya ko?"
Ahiyar zuciya ta sauke ta d'ora da cewa
"Zan iya mata gurkin abincin da zata ci kuma na wanke kwanikan da ta ci, amma gaskiya bazan iya zuwa na gyara mata d'aki na wanke toilet ba."
Zuba mata ido yayi kafin ya ce,
"Saboda me? kinfi k'arfin haka ne?to ki kafin a aura mani ke ni nake wannan aikin ballantana ke."
Murmushi tayi ba tare da ta kalle shi ba ta ce,
"Ballantana ni 'yar talaka ko? nasan abunda zaka fad'a kenan, matarka ta gama zagin iyaye na kaima yanzun zaka d'ora daga inda ta tsaya."
Ta k'arasa maganar tana goge k'walla da suka taru mata a ido.
"Ki kika fad'i haka, kuma na gama yanke shawara dan haka umarni na baki dole kiyi."
Daga nan yasa kai ya bar d'akin, a falo ya tarar da Sumayya da alama shi take nema, tana ganinsa ya fito daga d'akin inteesar ta tamke fuska ranta a 'bace ta ce,
"Baby me kaje yi a d'akin wannan kucakar yarinyar?"
"Naje sanar da ita ayyukan da zata yi ne."
Hannunta yaja suka nufi bedroom d'insa.
Haka rayuwa tayi ta tafiya, kullun inteesar idan ta idar da sallar asuba bata kowa ta kwanta, zata fara gyaran gidan idan ta gama ta shiga kitchen da had'a masu breakfast, bayan ta kammala ne lokacin da suka tashi daga barci zata shiga bedroom d'insu ta gyara masu, su kuma su zauna suna breakfast, duk randa zata shiga ta gyarawa Sumayya d'aki zara tarar ko ina a hargitse da kaya hatta kayan jikinta idan ta cire anan zata barsu zube a k'asa, ko kuma a watsa su saman gado.
'Dakun Muhdeen ne dai idan ta shiga bata shan wahalar gyarawa, domin komai a tsari yake yinsa ko kayan datti ne zai zuba a basket dake cikin toilet suke zuba kayan datti, idan mai wanki da guga yazo a had'a masa.
Murmushi tayi tare da cewa
"Ki k'ara hak'uri akan wanda kikayi a baya, da zaran ya shigo hannunki sai yadda kikayi dashi, saboda Allah ya baki wata irin baiwa wanda mijinki bai san da shi ba, amma da zaran ya San da hakan to wallahi kinfi k'arfin wulak'anci a wajensa, domin samun mace irinki yana da matuk'ar wahala kuma duk namijin da ya same ki kingama mallake zuciyarsa sai yadda kikayi da shi."
Zuba mata ido Aunty Abla tayi kafin ta ce,
"K'awa ta ta k'ara hak'uri zuwa yaushe? sai ta cigaba da zama cikin bak'in ciki da k'unci wanda ba'asan ranar wucewarsa ba?"
"Kada ki damu nan bada dad'ewa komai zai zamo labari, idan kinyi nazari a cikin labarin da ta bayar ai zaki fahimci ya fara sha'awar kusantarta, tunda ya fara kuwa bai wuya zai shiga hannunta sai yadda tayi dashi."
Kallon inteesar tayi tare da cewa
"Duk ranar da ya nemi kusantarki kada ki k'ara guje masa kamar yadda kikayi a baya."
Da sauri ta kalle ta
"Eh hakan zakiyi ba ki da wani za'bi
Daga alk'alamin
Zainab Abdullah K.N T
(Maman Ihsan)
Don Karin bayani
09065327995
Love you oll
Comments and shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullah K.N.T
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izinina ba.
*SANARWA*
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubuta shi dan cin zarafi ga kowa ba, idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarce ni bada niyyar yin hakan nayi ba, arashi ne mai kashe auran wawa.
*BISIMILLAHI RAHMANI RAHEEM*
Page5
"Duk ranar da ya nemi kusantarki kada ki k'ara guje masa kamar yadda kikayi a baya."
Da sauri ta kalle ta
"Eh hakan za'ayi baki da wani za'bi"
Tura baki tayi tare da cewa
"Shifa ya ce baya sona kuma da zarar matarsa ta dawo gidan nan zai rabu da ni, to kuma mutumin da baya k'auna ta zan bawa kaina? ya raba ni da budurci na fa kenan sannan ya rabu dani."
Ta k'arasa maganar tana sunkuyar da kanta k'asa,
Dariya sukayi dukansu, Aunty Abla ta d'ora da cewa
"Wa ya fad'a maki zai rabu dake?"
"Shine da bakinsa ya fad'a mani fah."
"Ya dai fad'a ne amma bai isa ya rabu da ke ba, domin rabuwa da ke tamakar bijirewa iyayensa yayi, kuma nasan shi yana da biyayya bazai iya bijirewa maganarsu ba, don haka idan kina tunannin zai rabu dake be to ki daina, kisan yadda zakiyi ki mallaki zuciyarsa kawai."
"Nima fa ba sonsa nake ba, jira nake ya rabu dani kawai na koma gidanmu."
Murmushi kawai Aunty Abla tayi tare da cewa
"To kiyi ta addu'a duk abunda yafi zama alkhairi a gare ki Allah ya tabbatar maki da shi."
Daga nan Hajiya Bilkisu ta bud'e jakkarta ta fito da wasu goruna guda uku, ta mik'awa inteesar d'aya kar'bi ki shanye shi nan da kwana uku safe da yamma zaki dinga sha."
Ta d'auko wani goran ta mik'a mata ta ce,
"Wannan rubutun kuma ki shanye shi yanzun nan ki bani goran."
Ba musu ta kar'ba tare da yin Bisimillah ta shanye ta mik'a mata goran, sai ta mik'a mata cikon ta ukun tare da cewa
"Wannan zumar kuma zaki sha cokali d'aya a rana, sai kuma washe gari sau d'aya ake sha a rana saboda yana da k'arfi."
Jakarta ta bud'e ta fito da wani turare ta ce,
"Wannan dai kinsan irinsa na tsugunno ne, na maki amfani da shi lokacin kina gida na."
Ta ciro wasu ta ce
"Wad'annan turarurruka ne da sabulun wanka ki dinga amfani da su kowane lokaci."
Nasiha suka k'ara mata da shawarwari suka k'ara bata hak'uri, sannan sukayi suka tafi, har zata raka su suka ce ta yi zamanta komawa tayi ta kwanta.
A falo suka samu Muhdeen yana waya, ganinsu yasa ya katse kiran tare da cewa
"Aunty har kun fito?"
Hajiya Bilkisu ce tayi masa sallama ta fice, yayin da Aunty Abla ta zuba masa ido ba tare da ta ce komai ba, tunani ya shiga yi ko dai inteesar ta kai k'ararsa ne? bai gama tunani ba ya ji murayar Aunty Abla na cewa
"Son kaji tsoron Allah yarinyar nan inteesar amana ce a wajenka, kamar yadda ba'ayi shawara da kai ba aka d'aura maka aure da ita haka itama, ba'ayi shawara da ita ba aka aura mata kai, hak'uri zakayi da ita ko baka sonta ka kyautata mata ka sauke duk wani hakki nata da Allah ya d'ora maka, kada kaga cewa ita waccan soyayya ce ta had'aku ka fifita ta akan inteesar, Allah yana ji kuma yana ganinka kuma zai tambaye ka, kafa ka tashi a ranar tashin alk'iyama 'barin jikinka yana karkata, ka sani kake sani, bata kowa sai ta baro gidan iyayenta saboda kai kada ka wulak'anta ta."
Daga nan bata sake magana ba tayi ficewarta, don har ga Allah taji zafin abunda yakewa inteesar a baya, musamman da ta tuna cewa farkon aurensu ya dinga wahalar da ita ba tausayawan alhalin bata masa laifin komai ba.
Cikin sanyin jiki ya koma kan kujera ya zaun, yana tunanin maganganun da Aunty Abla ta sanar da shi kuma yasan tabbas bai kyautawa inteesar ba, a d'an zamansa da ita ba wani abu na kyautatawa ko adalci da ya mata, sai musguna mata da wahalar da ita da yayi, kuma yasan tabbas a halin yanzun idan ya ce zai kwatanta adalci a tsakaninsu to za'a samu matsala da Sumayya, domin sai da ya sanar da ita cewa inteesar kamar mai aiki ce aka kawo mata ba kishiya ba kuma ko kallo bata ishe sa ba sannan ta yadda ta dawo, tunda ba abunda ta iya inteesar ce zata dinga mata.
Mik'ewa yayi ya nufi d'akinta, tura k'ofar d'akin yayi ya shiga da sallama, d'agowa tayi da sauri ta kalle shi cike da fargabar me zai biyo baya, ta dai san arziki da alkhairi baya sa ya shigo d'akinta, idan ya shigo to wani muguntar be zai mata, a zuciyarta ta ce, na shiga uku me kuma nayi masa ya biyo ni d'aki na? ko dai aikin wahalar ne zan cigaba tunda Gwaggo ta tafi, sannan wannan ne karo na farko da ya shigo da sallama a d'akinta, cikin sanyin muryarta ta ce,
"Wa'alaika salam"
K'arasowa yayi gabanta ya ce,
"Wace magana kukayi da su Aunty Abla?"
Gabanta ne ya fad'i amma sai ta dake ta ce
"Bakomai"
Zuba mata Ido yayi yana karantarta kafin ya ce,
"Akwai yanayin maganarta ya tabbatar mani da cewa akwai maganar da kika fad'a mata, wato ke baki iya rik'e sirrin gidanki ko?"
"Ba abunda na fad'a mata ta ce,wai na rame ne "
Shiru yayi sannan ya d'ora da cewa
"Mata ta dai ta dawo yau, saboda haka kiyi mata biyayya a matsayinta na uwar gida wacce kika zo kika tarar, dole ki girmama ta,bayan haka kuma ko a shekaru ba tsaranki bace ta girme maki nesa ba kusa ba, sannan kuma ita ta taso daga gidan iyayenta bata aikin komai masu aiki ke mata gyaran d'aki da girki bata komai sai dai ayi mata bata iya ba, kuma ni bana son ace 'yar aiki zata girka abincin da zanci, kuma bana son ace 'yar aiki zata shiga ta gyara mani bedroom, shine nake neman alfarma a wajenki da ki dinga taimaka mata da ayyukan tunda bata iya komai ba, kinga matsayin ya take a gare ki shekarunta talatin ke kuma shekarunki goma Sha takwas kinga ai ta cancanci kiyi mata ko?"
Shiru tayi tana nazari ba tare da ta ce, komai ba, ganin shirun nata yayi yawa ne yasa shi cewa
"Kinsan cewa na tsani shariya ko?"
Ahiyar zuciya ta sauke ta d'ora da cewa
"Zan iya mata gurkin abincin da zata ci kuma na wanke kwanikan da ta ci, amma gaskiya bazan iya zuwa na gyara mata d'aki na wanke toilet ba."
Zuba mata ido yayi kafin ya ce,
"Saboda me? kinfi k'arfin haka ne?to ki kafin a aura mani ke ni nake wannan aikin ballantana ke."
Murmushi tayi ba tare da ta kalle shi ba ta ce,
"Ballantana ni 'yar talaka ko? nasan abunda zaka fad'a kenan, matarka ta gama zagin iyaye na kaima yanzun zaka d'ora daga inda ta tsaya."
Ta k'arasa maganar tana goge k'walla da suka taru mata a ido.
"Ki kika fad'i haka, kuma na gama yanke shawara dan haka umarni na baki dole kiyi."
Daga nan yasa kai ya bar d'akin, a falo ya tarar da Sumayya da alama shi take nema, tana ganinsa ya fito daga d'akin inteesar ta tamke fuska ranta a 'bace ta ce,
"Baby me kaje yi a d'akin wannan kucakar yarinyar?"
"Naje sanar da ita ayyukan da zata yi ne."
Hannunta yaja suka nufi bedroom d'insa.
Haka rayuwa tayi ta tafiya, kullun inteesar idan ta idar da sallar asuba bata kowa ta kwanta, zata fara gyaran gidan idan ta gama ta shiga kitchen da had'a masu breakfast, bayan ta kammala ne lokacin da suka tashi daga barci zata shiga bedroom d'insu ta gyara masu, su kuma su zauna suna breakfast, duk randa zata shiga ta gyarawa Sumayya d'aki zara tarar ko ina a hargitse da kaya hatta kayan jikinta idan ta cire anan zata barsu zube a k'asa, ko kuma a watsa su saman gado.
'Dakun Muhdeen ne dai idan ta shiga bata shan wahalar gyarawa, domin komai a tsari yake yinsa ko kayan datti ne zai zuba a basket dake cikin toilet suke zuba kayan datti, idan mai wanki da guga yazo a had'a masa.