Sashe 68
Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Komawa sukayi cikin gidan suka share fasassun kwalbar suka zuba a mazubin shara suka goge wajen suka tsaftace shi sannan suka janyo k'ofar suka fito suna fitowa sai ga Direban Muhdeen wato Ishaq ya dawo tare da Mai bawa fulawoyin gidan ruwa, gaishe da Mummy sukayi ta amsa cikin nitsuwa kamar ba abunda ya faru, dai-dai lokacin da mai gadin ya dawo, ya kawo mata ruwan ta ce ya barshi suyi amfani da shi an Kira ta suna sauri zasu tafi, shiga motar sukayi direbanta yaja suka bar gidan akan hanya suka had'u da Jabeer yana ganin su ya fito daga motarsa ya k'arasa wajen motar,Mufida ce a gefen dieban Mummy ta zauna baya ga Inteesar kwanace a gefenta, ya bud'e baki zai gaida Mummy idanunsa suka sauka akan Inteesar zaro ido waje yayi tare da cewa
"Shbhanallah, me ya same ta haka?"
"Shine dalilin kiranka, yanzun ba lokacin bayani so nake ka kaimu wani waje da zaka kula da ita kayi abunda ya dace ko Allah zaisa a samu kanta."
"Gaskiya sai dai mu kaita asibiti"
"Wane asibitin?"
"Asibitin mijinta mana."
Kai Mummy ta girgiza alamun a'a sannan ta ce,
"Ba za'a kaita asibitinsa saboda bana son yasan halinda da take ciki."
Da mamaki Jabeer yake kallonta
"Saboda me Mummy?"
"Yanzun ba lokacin da zamu tsaya dogon magana bane, ina son wajenda bazai san halin da take ciki ba."
Shiru yayi tare da nazari sannan ya ce,
"To mu kaita asibitin aboki na"
Ciro wayarsa yayi daga cikin aljihu sannan ya kira Doctor Salim, bayanin abunda zai kawo yayi masa sannan ya kalli Direban Mummy tare da bashi umarnin ya biyo shi a baya, daga nan ya shiga motarsa tare da yi mata key yabar wajen, Direban Mummy ya bi shi a baya suka bar unguwar.
Suna isa Asibitin da Doctor Salim yake aiki suka tarar da shi a harabar asibitin yana jiran k'arasowarsau, cikin k'anka'anun lokaci aka shigar da ita d'akin da Doctor Salim ya umarce su, nan ya kwantarwa da su Mummy hankali ya ce su jira tukunnah.
Nan suka tsaya suna jira har tsawon awa biyu kafin Doctor Salim ya fito ya same su, ya sanar da su cewa sunyi duk k'ok'arin da zasuyi amma har yanzun bata farfad'o ba, doguwar suma tayi zata iya fardad'owa ko wane lokaci.
Dai-dai lokacin Jabeer ya fito tare da wani Doctor d'auke da kayan aiki, Jabeer ne ya kalli Mummy ya ce,
"Mummy ki kwantar da hankalinki, insha Allah zata dawo hayyacinta,anan za'a kula da ita zaku iya tafiya gida anjima kundawo, koda kun tafi akwai nursess d'in da zasu kuka da ita."
Girgiza kai tayi tare da cewa
"Jabeer bazan iya tafiya nabarta ba."
"Mummy ba yanzun zata farfad'o ba gara ki tafi tukunnah idan yaso sai kibar Mufida ta tsaya, don nima zan koma can Asibiti zuwa d'an anjima zan dawo."
Yana kaiwa k'arshen maganarsa kafin Mummy tayi magana wayarsa ta soma ruri, cirowa yayi yaga Muhdeen ne, don haka ya kalli Mummy tuna cewa ta ce bata san yasan da zancen, hakan yasa ya d'aga wayar tare da cewa
"Doctor ya akayi ne?"
Daga can 'bangare Muhdeen ya fara magana yana cewa
"Wai ina ka shiga ne tun d'azun ka fita daga Asibiti baka dawo ba kuma naka sanar da ni ba."
"Am not sure zan iya sanar da kai inda naje, amma dai gani nan zuwa yanzun nan."
Tsuki Muhdeen yayi tare da katse kiran ya cigaba da duba patient d'insa."
Jabeer ne ya kalli Mummy bayan sauran Doctors sun tafi ya ce,
"Wai garin yaya akayi hakan ta faru?"
Girgiza kai tayi tare bawa Jabeer labarin komai da ke faruwa kamar yadda Mufida ta sanar da ita.
Ransa yakai matuk'ar'baci da jin zancen don kwata-kwata baiyi tunanin hakan ba, ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa
"To waye ya dake ta akai haka?"
"Allah masani sai dai idan ta farfad'o ta sanar damu."
"To Allah yasa haka"
Daga nan yayi masu sallama akan anijima zai dawo, ya tafi zuwa Asibiti.
Wayar Mummy ce tayi ringing ta duba taga Dady ne ke kiranta, d'agwa tayi tare da cewa
"Assalamu alaikum"
Daga can 'bangaren kuwa Dady ne da Gwaggo zaune a falo, jin Mummy ta d'aga wayar ne ya ce,
"Wai ina kika tafi ne tun safe gashi har k'arfe goma sha biyun rana, kuma kun fita baku sanar da kowa inda zaku tafi ba."
'shiru tayi tana nazari idan ta sanar da shi cewa ga abunda ya faru da Inteesar anya zai giyi bayan hukuncin da tayi niyyar d'auka akan Muhdeen kuwa? kada tazo ta sanar da shi yazo yak'i bin bayan hukuncin da zata yanke akai, hakan kuma zai iya bata matsala, don hukuncin da tayi niyyar yankewa k'arshenta bazaiwa kowa dad'i ba, kuma tasan Dady yana da sauk'in kai, zai iya lalata mata k'udirinta don haka ta ce,
"Yanzun zan dawo na tafi dubiya ne"
"Okay Mahaifiyar Inteesar ko?"
"Eh ita"
"To ki gaishe ta nima jiya daddare naje, Allah ya bata lafiya"
Daga nan ta katse kiran ta kalli Mufida ta ce,
Zan tafi gida yanzun duk abunda ake ciki ki kirani a waya ki sanar dani, sannan naga restaurant a nan kuda da su yakamata ki nemi abunda zaki ci, koda take bari nasa Direba ya kawo maki takeaway."
Daga nan ta tafi Mufida ta samu wuri ta zauna.
A 'bangaren Muhdeen kuwa yana zaune a office d'insa gaba d'aya kewarta yake, yana tunanin daren shekaranjiya da ya fara kusantarta yana farin ciki da nishad'i shi kad'ai, don Allah Allah yake ya koma gida ya ganta, gaba d'aya tunaninta ya addabe shi, ji yayi gaba d'aya bazai iya hak'uri ba sai yaje gare ta, don haka ya mik'e don komawa gida ya ganta ko zai samu nutsuwa.
Sai da ya fara zuwa d'akin da aka kwantar da Umman Inteesar d'in, shiga yayi ya gaishe ta a karo na biyu, daga nan ya nufi motarsa don komawa gare ta
Yana k'ok'arin bud'e motar ne sai ga Jabeer ya k'araso wajensa, kallon Jabeer yayi tare da cewa
"Daga ina haka?"
Dariya Jabeer yayi tare da cewa
"Naji kewar matata ce shine zanje naganta."
Dariya Muhdeen yayi lokacin da shima ya tuno da Inteesar d'insa
"Kaidai ka sani sauk'in abun ma nima Ina da tawa, yanzun haka wajenta zanje don gaskiya yanzun nasan dad'in aure wallahi don haka da na tuno da ita naji na kasa hak'uri sai naje na d'an kwashi gara tukunnah, wata kila ma sai gobe dan bana jin zan samu lokacin dawowa."
Murmushin takaici Jabeer yayi don a tunaninsa akan Sumayya yake magana baisan akan Inteesar bane, don haka sharesa kawai yayi yabar wajen, bunsa da kallo yayi tare da ta'be baki yaja motarsa yabar wajen.
Koda ya isa bakin gate horn yayi mai gadi ya wangale masa gate, shiga yayi bayan yayi parking ya fito fuskarsa d'auke da annuri, duk Wanda ya kallesa yasan yana cikin farin ciki.
Kai tsaye d'akinsa ya nufa ganin ba kowa a falon, ba Sumayya ba Inteesar, kayan jikinsa ya rage ya shiga toilet don yin wanka, bayan ya fito ya ya shafa turare mai dad'in k'amshi, k'aramar riga ya saka da wando 3 quarter.
Shikad'ai yake magana kamar yanayi da wani yana cewa
"Bansan yaushe ne ki kuma wani lokaci bane na kamu da sonki, bani da burin da ya wuce na ganni gani gaki, ina jinki tamkar wani sashe na jiki na idan na kasance tare da ke har farin ciki nake ji a cikin raina."
Haka ya dinga magana shi kad'ai har ya gama shirinsa ya fito don zuwa d'akinta, yana fitowa ne yayi kici'bis da Sumayya tana dawowa daga waje, kallo d'aya yayi mata ya kauda kansa ya nufi d'akin Inteesar, ganin haka yasa Sumayya ta k'arasa da sauri ta rungume sa ta baya tare da d'ora ha'barta a kafad'arsa cikin kirsa ta fara magana tana cewa
"Washh baby nagaji wallahi tun jiya da na fita ban dawo ba sai yanzun duk a gajiye nake baby yunwa ya addabe ni me yarinyar nan ta girka muna ne?"
Baice da ita komai ba illa ya janye ta daga jikinsa yayi tafiyarsa, murmushin mugunta tayi ta nufi d'akinta, shi kuma ya nufi d'akin Inteesar.
*Daga alk'alamin*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
Don k'arin bayani
09065327995
Love you oll
Comment & shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izini na ba.
*SANARWA*
Wannan kagaggen labari ne, banyi tunanin rubuta shi dan cin zarafi ga kowa ba, idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarce ni bada niyar yin hakan nayi ba, arashi ne mai kashe auren wawa.
*BISIMILLAHI RAHAMANI RAHEEM*
Page5
Baice da ita komai ba illa ya janye ta daga jikinsa yayi tafiyarsa, murmushin mugunta tayi ta nufi d'akinta, shi kuma ya nufi d'akin Inteesar.
Da sallama ya shiga d'akin bayan ya tura k'ofar, bata cikin d'akin dan haka sai ya zauna a bakin gadon yana jiranta don a tunaninsa tana toilet ne, har tsawon mintuna goma bata fito ba kuma baiji alamun motsin mutum ba, dan haka ya tashi ya k'arasa k'ofar toilet d'in bata ciki tsayawa yayi ya k'arewa d'akin kallo komai tsaf abun sha'awa sai k'amshi ke tashi, murmushi yayi sannan ya fita d'akin.
Kai tsaye kitchen ya nufa nan ma bata ciki har store ya duba bata nan, mamaki ne ya kama sa ina zata je ita da bata zuwa ko ina kullun tana gida to ina ta shiga ne?
Haka ya dinga duba cikin gidan nan duka d'akunan gidan lungu da sak'o ba inda bai neme ta ba amma bai ganta ba, haka ya bincike gidan nan gaba d'aya ba Inteesar ba alamarta, fita harabar gidan yayi ya samu mai gadi da Ishaq Direba da mai bawa filawa ruwa suna fira.
"Shbhanallah, me ya same ta haka?"
"Shine dalilin kiranka, yanzun ba lokacin bayani so nake ka kaimu wani waje da zaka kula da ita kayi abunda ya dace ko Allah zaisa a samu kanta."
"Gaskiya sai dai mu kaita asibiti"
"Wane asibitin?"
"Asibitin mijinta mana."
Kai Mummy ta girgiza alamun a'a sannan ta ce,
"Ba za'a kaita asibitinsa saboda bana son yasan halinda da take ciki."
Da mamaki Jabeer yake kallonta
"Saboda me Mummy?"
"Yanzun ba lokacin da zamu tsaya dogon magana bane, ina son wajenda bazai san halin da take ciki ba."
Shiru yayi tare da nazari sannan ya ce,
"To mu kaita asibitin aboki na"
Ciro wayarsa yayi daga cikin aljihu sannan ya kira Doctor Salim, bayanin abunda zai kawo yayi masa sannan ya kalli Direban Mummy tare da bashi umarnin ya biyo shi a baya, daga nan ya shiga motarsa tare da yi mata key yabar wajen, Direban Mummy ya bi shi a baya suka bar unguwar.
Suna isa Asibitin da Doctor Salim yake aiki suka tarar da shi a harabar asibitin yana jiran k'arasowarsau, cikin k'anka'anun lokaci aka shigar da ita d'akin da Doctor Salim ya umarce su, nan ya kwantarwa da su Mummy hankali ya ce su jira tukunnah.
Nan suka tsaya suna jira har tsawon awa biyu kafin Doctor Salim ya fito ya same su, ya sanar da su cewa sunyi duk k'ok'arin da zasuyi amma har yanzun bata farfad'o ba, doguwar suma tayi zata iya fardad'owa ko wane lokaci.
Dai-dai lokacin Jabeer ya fito tare da wani Doctor d'auke da kayan aiki, Jabeer ne ya kalli Mummy ya ce,
"Mummy ki kwantar da hankalinki, insha Allah zata dawo hayyacinta,anan za'a kula da ita zaku iya tafiya gida anjima kundawo, koda kun tafi akwai nursess d'in da zasu kuka da ita."
Girgiza kai tayi tare da cewa
"Jabeer bazan iya tafiya nabarta ba."
"Mummy ba yanzun zata farfad'o ba gara ki tafi tukunnah idan yaso sai kibar Mufida ta tsaya, don nima zan koma can Asibiti zuwa d'an anjima zan dawo."
Yana kaiwa k'arshen maganarsa kafin Mummy tayi magana wayarsa ta soma ruri, cirowa yayi yaga Muhdeen ne, don haka ya kalli Mummy tuna cewa ta ce bata san yasan da zancen, hakan yasa ya d'aga wayar tare da cewa
"Doctor ya akayi ne?"
Daga can 'bangare Muhdeen ya fara magana yana cewa
"Wai ina ka shiga ne tun d'azun ka fita daga Asibiti baka dawo ba kuma naka sanar da ni ba."
"Am not sure zan iya sanar da kai inda naje, amma dai gani nan zuwa yanzun nan."
Tsuki Muhdeen yayi tare da katse kiran ya cigaba da duba patient d'insa."
Jabeer ne ya kalli Mummy bayan sauran Doctors sun tafi ya ce,
"Wai garin yaya akayi hakan ta faru?"
Girgiza kai tayi tare bawa Jabeer labarin komai da ke faruwa kamar yadda Mufida ta sanar da ita.
Ransa yakai matuk'ar'baci da jin zancen don kwata-kwata baiyi tunanin hakan ba, ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa
"To waye ya dake ta akai haka?"
"Allah masani sai dai idan ta farfad'o ta sanar damu."
"To Allah yasa haka"
Daga nan yayi masu sallama akan anijima zai dawo, ya tafi zuwa Asibiti.
Wayar Mummy ce tayi ringing ta duba taga Dady ne ke kiranta, d'agwa tayi tare da cewa
"Assalamu alaikum"
Daga can 'bangaren kuwa Dady ne da Gwaggo zaune a falo, jin Mummy ta d'aga wayar ne ya ce,
"Wai ina kika tafi ne tun safe gashi har k'arfe goma sha biyun rana, kuma kun fita baku sanar da kowa inda zaku tafi ba."
'shiru tayi tana nazari idan ta sanar da shi cewa ga abunda ya faru da Inteesar anya zai giyi bayan hukuncin da tayi niyyar d'auka akan Muhdeen kuwa? kada tazo ta sanar da shi yazo yak'i bin bayan hukuncin da zata yanke akai, hakan kuma zai iya bata matsala, don hukuncin da tayi niyyar yankewa k'arshenta bazaiwa kowa dad'i ba, kuma tasan Dady yana da sauk'in kai, zai iya lalata mata k'udirinta don haka ta ce,
"Yanzun zan dawo na tafi dubiya ne"
"Okay Mahaifiyar Inteesar ko?"
"Eh ita"
"To ki gaishe ta nima jiya daddare naje, Allah ya bata lafiya"
Daga nan ta katse kiran ta kalli Mufida ta ce,
Zan tafi gida yanzun duk abunda ake ciki ki kirani a waya ki sanar dani, sannan naga restaurant a nan kuda da su yakamata ki nemi abunda zaki ci, koda take bari nasa Direba ya kawo maki takeaway."
Daga nan ta tafi Mufida ta samu wuri ta zauna.
A 'bangaren Muhdeen kuwa yana zaune a office d'insa gaba d'aya kewarta yake, yana tunanin daren shekaranjiya da ya fara kusantarta yana farin ciki da nishad'i shi kad'ai, don Allah Allah yake ya koma gida ya ganta, gaba d'aya tunaninta ya addabe shi, ji yayi gaba d'aya bazai iya hak'uri ba sai yaje gare ta, don haka ya mik'e don komawa gida ya ganta ko zai samu nutsuwa.
Sai da ya fara zuwa d'akin da aka kwantar da Umman Inteesar d'in, shiga yayi ya gaishe ta a karo na biyu, daga nan ya nufi motarsa don komawa gare ta
Yana k'ok'arin bud'e motar ne sai ga Jabeer ya k'araso wajensa, kallon Jabeer yayi tare da cewa
"Daga ina haka?"
Dariya Jabeer yayi tare da cewa
"Naji kewar matata ce shine zanje naganta."
Dariya Muhdeen yayi lokacin da shima ya tuno da Inteesar d'insa
"Kaidai ka sani sauk'in abun ma nima Ina da tawa, yanzun haka wajenta zanje don gaskiya yanzun nasan dad'in aure wallahi don haka da na tuno da ita naji na kasa hak'uri sai naje na d'an kwashi gara tukunnah, wata kila ma sai gobe dan bana jin zan samu lokacin dawowa."
Murmushin takaici Jabeer yayi don a tunaninsa akan Sumayya yake magana baisan akan Inteesar bane, don haka sharesa kawai yayi yabar wajen, bunsa da kallo yayi tare da ta'be baki yaja motarsa yabar wajen.
Koda ya isa bakin gate horn yayi mai gadi ya wangale masa gate, shiga yayi bayan yayi parking ya fito fuskarsa d'auke da annuri, duk Wanda ya kallesa yasan yana cikin farin ciki.
Kai tsaye d'akinsa ya nufa ganin ba kowa a falon, ba Sumayya ba Inteesar, kayan jikinsa ya rage ya shiga toilet don yin wanka, bayan ya fito ya ya shafa turare mai dad'in k'amshi, k'aramar riga ya saka da wando 3 quarter.
Shikad'ai yake magana kamar yanayi da wani yana cewa
"Bansan yaushe ne ki kuma wani lokaci bane na kamu da sonki, bani da burin da ya wuce na ganni gani gaki, ina jinki tamkar wani sashe na jiki na idan na kasance tare da ke har farin ciki nake ji a cikin raina."
Haka ya dinga magana shi kad'ai har ya gama shirinsa ya fito don zuwa d'akinta, yana fitowa ne yayi kici'bis da Sumayya tana dawowa daga waje, kallo d'aya yayi mata ya kauda kansa ya nufi d'akin Inteesar, ganin haka yasa Sumayya ta k'arasa da sauri ta rungume sa ta baya tare da d'ora ha'barta a kafad'arsa cikin kirsa ta fara magana tana cewa
"Washh baby nagaji wallahi tun jiya da na fita ban dawo ba sai yanzun duk a gajiye nake baby yunwa ya addabe ni me yarinyar nan ta girka muna ne?"
Baice da ita komai ba illa ya janye ta daga jikinsa yayi tafiyarsa, murmushin mugunta tayi ta nufi d'akinta, shi kuma ya nufi d'akin Inteesar.
*Daga alk'alamin*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
Don k'arin bayani
09065327995
Love you oll
Comment & shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izini na ba.
*SANARWA*
Wannan kagaggen labari ne, banyi tunanin rubuta shi dan cin zarafi ga kowa ba, idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarce ni bada niyar yin hakan nayi ba, arashi ne mai kashe auren wawa.
*BISIMILLAHI RAHAMANI RAHEEM*
Page5
Baice da ita komai ba illa ya janye ta daga jikinsa yayi tafiyarsa, murmushin mugunta tayi ta nufi d'akinta, shi kuma ya nufi d'akin Inteesar.
Da sallama ya shiga d'akin bayan ya tura k'ofar, bata cikin d'akin dan haka sai ya zauna a bakin gadon yana jiranta don a tunaninsa tana toilet ne, har tsawon mintuna goma bata fito ba kuma baiji alamun motsin mutum ba, dan haka ya tashi ya k'arasa k'ofar toilet d'in bata ciki tsayawa yayi ya k'arewa d'akin kallo komai tsaf abun sha'awa sai k'amshi ke tashi, murmushi yayi sannan ya fita d'akin.
Kai tsaye kitchen ya nufa nan ma bata ciki har store ya duba bata nan, mamaki ne ya kama sa ina zata je ita da bata zuwa ko ina kullun tana gida to ina ta shiga ne?
Haka ya dinga duba cikin gidan nan duka d'akunan gidan lungu da sak'o ba inda bai neme ta ba amma bai ganta ba, haka ya bincike gidan nan gaba d'aya ba Inteesar ba alamarta, fita harabar gidan yayi ya samu mai gadi da Ishaq Direba da mai bawa filawa ruwa suna fira.