← Book details Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 99

Sashe 48

Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wani turare da bata ta'ba amfani da shi ba ta d'auko ta shafa son turaren yana da wani sirri na musamman shiyasa ma Hajiya Bilkisu ta sanar da ita cewa idan har zata fita daga gida kada ta shafa turarenta sai dai idan tana cikin gida ne,bayan ta shafa turaren ne ta fito ta zo falo inda ta tarar da Gwaggo,
"Barka da hutawa Gwaggo"
"Ke ni ba wani barka wallahi,haka gidan naku yake?"
"Me ya faru Gwaggo?"
"Tambayar me ya faru kike 'yar albarka ?meye ma bai faru ba?to Ni ban saba da haka ba,ace mutum bazai ci abinci sassafe ba sai k'arfe goma?so kike ki kashe ni da yunwa ko?to wallahi bazan iya ba matuk'ar haka zaki dinga yi to zan kira waya a turo direba ya d'auke ni,ko a gidan Fatima koda ba zata karya da wuri ba sassafe zata kawo mani nawa har d'aki,wata rana ma kece kike kawo mani,amma daga yin aurenki zaki koyi mugun hali na barin bak'o da yunwa to kika sake mani haka zan bar gidan nan."
Da sauri Inteesar ta durk'usa tana rok'on Gwaggo akan tayi hak'uri,kada ta tafi don idan ta tafi farin ciki ya k'are mata a gidan.

"Tuba nake Gwaggo ki gafarceni bazan sake ba insha Allah."
"To shikenan naji,yunwa nake ji kije d'akin mijinki ki Kira shi yazo muyi karin kumallo a tare."
Gabanta ne ya fad'i Jin abunda Gwaggo ta ke cewa,don haka ta ce
"Gwaggo kamar barci yake,mu barshi idan ya tashi sai ya ci nasa."
"A'a kedai kije ki Kira shi,kawai."
Ba yadda ta iya ranta baiso ba ta nufi d'akinsa,tura k'ofar ta yi tare da sallama,kwance ya ke kan gado idanunsa a lumshe kamar mai barci amma ba barcin yake ba,ganin kamar yana barci yasa ta k'araso d'akin cikin sand'a, waige-waige ta dingayi tana tunanin ina ya ajiye mata wayarta da amshe a hannunta.

Shi kuma tunda ta shigo k'amshin turaren Hajiya Bilkisu ya fara aiki,don turaren na musamman ne mai d'auke da wani sirri wanda idan mace ta shafa turaren namiji ya shak'a kamshinsa sai shauk'i ya kamashi,to kuwa tunda Muhdeen ya ji k'amshin turaren nan gaba d'aya ya rasa nutsuwarsa ji yake kamar ya rungumeta
Rasa ina ya aje wayar ta yi har ta nufi closet zata duba sai ta fasa duk yana kallonta, side drawer ta duba takaddu ne kawai zagayawa ta yi d'aya 'bangaren da ta janyo side drawer na jikin gado na sama kasancewar tayi kusa da shi sosai k'amshin turaren ya k'ara hautsina shi, sunkuyawar da tayi ne ya fincikota ta fad'o jikinsa,had'a ta yayi da k'irjinsa ya fara kissing nata ta ko ina,jikinsa sai rawa suke idanunsa sun fara janaza kala zuwa ja tun tana k'ok'arin k'watar kanta har ta kasa don abun nasa na yau yafi na jiya yamutse ta ya dingayi ta ko ina kuma son ransa a haka suka kwashe mintuna talatin,ganin yana neman wuce gona da iri ne kuma ta kasa k'watar kanta don bai bata wannan damar ba yasa ta sakar masa kuka,sakinta ta yi tare da maida numfashi,gashin kanta duk sun yamutse,d'an kwalinta ta d'auka ta nufi hanyar fita har ta kai bakin k'ofa ta tsaya ta goge hawayenta sannan ta jiyo ta kalleshi tare da harararsa ta ce
"Wallahi sai Allah ya saka mani abunda ka yi Mani."
Mi'kewa taga ya yi ta fita a guje,dariya ya yi tare da cewa
"matsoraciya ai da kin tsaya"
Fita shima ya yi don bai gaisa da Gwaggo ba.

Gwaggo na zaune a falo ta had'a tagumi daga cewa Inteesar ta kira Muhdeen shikenan ba ita ba shi fiye da rabin awa, Inteesar gaba d'aya kunya ce ta kamata ganin yadda duk kayan jikinta suka yamutse haka ma gashin kanta,ba yadda za'ayi ta shiga d'akinta ba tare da Gwaggo ta ganta ba,kuma ita gaskiya tana jin kunyar Gwaggo ta ganta a haka don sai ta zargi want abu, tsaye ta yi a jikin k'ofar da zata sada ta da falonta inda Gwaggon ta ke,ji ta yi kawai an rik'e hannunta ana janta zuwa falon,juyawa tayi da sauri ta kalle shi,kafin ta yi magana ne har ya janyota sun shigo falon,ido Gwaggo ta zuba masu daga shi har ita,kallo d'aya ta ma Inteesar ta fahimci komai don haka kauda kanta kawai ta yi kunya duk ya ishi Inteesar amma shikam ko a jikinsa,gaida Gwaggo ta yi tare da cewa
"Ina kwana Gwaggo?"
"Ina wuni zaka ce mani ba ina kwana ba,k'arfe nawa yanzun ku shige d'aki kaida matarka Kuna ta jarabarka a d'aki kun banzatar dani ko?kuma kafi kowa sanin cewa bana iya zama da yunwa ciwona zai tashi ko."
Kallon Gwaggon ya yi ya kalli Inteesar ya ce
"Gwaggo dama bakiyi breakfast ba?"
"Lokacin da na tura matarka ta kira mani kai bata fad'a maka ba?"
"A'a Gwaggo bata fad'a mani ba"
Kallon Inteesar Gwaggo ta yi tare da cewa
"To da na aike ki baki fad'a ba ko?kika rik'e shi a d'aki kika k'i fad'a masa ko?ke ga jarababbiya uwar son miji,kinje kinyi muk'us a d'aki kin samu abunda kike so ni yunwa ta kase ni ko?indai ke buk'atarki ta biya ni ko oho ko?'yar yarinya dake sai jaraba,to ba sai ki mani Kora da hali ba kinbarni da yunwa ba tafiya ta zanyi kuje can ku k'arata
*KUYI HAKURI DA WANNAN*
Daga alk'amin
Zainab Abdullahi
(Maman Ihsan)
Don k'arin bayani
09065327995
Love u oll
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izini na ba.

Wannan kagaggen labari ne,banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi ga kowa ba, Idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba,arashi ne mai kashe auren wawa.
*BISIMILLAHI RAHMANI RAHEEM*
Page 4
"'yar yarinya dake sai jaraba,to ba sai kin mani kora da hali kin barni da yunwa ba,tafiya ta zanyi kuje can ku k'arata."
Tsabar takaici yasa Inteesar sakin kuka ta fad'a jikin Gwaggo ta kasa magana sai kuka kawai take, rik'e ta Gwaggo tayi ta rungumeta tana cewa
"To me aka maki na kuka tsabar sangarta ne ko kuma me?dan na fad'i gaskiya shine zaki saka ni gaba kina mani kuka haba 'yar albarka me kuma zaki zauna kina ma kuka?ya isa hakanan."
Ta k'arasa maganar tana shafa bayanta alamaun rarrashi.

"Bana son kukanki wallahi ki daina mana kada ki tayar mani da gankali."
'Dagowa ta yi tare da goge hawayenta ta ce,
"To kada ki tafi ki zauna da ni,idan kika tafi nima bazan zauna a gidan nan ba."
Kallonta kawai Gwaggo ta yi tare janyeta daga jikinta,ta shi tayi ta janyo hannun Inteesar ta mik'ar da ita tsaye.

"Taso muje mu ci abinci."
Binta ta yi ba tare da ta ce komai ba,shima bayansu ya bi yana kallon ikon Allah daga magana sai kuka.

Kwanci ta shi ba a wurin Allah,a haka har Gwaggo ta cika sati biyu a cikin gidan,kullun tana mak'ale jikin Gwaggo,shi kuma Muhdeen na zuwa Asibiti idan ya tafi da safe sai yamma ya ke dawowa,wani lokacin yakan je gidansu ya gaida Mummy da Dady,Mufida ma ta zo da k'awayensu Saliha da wasila sunzo gidan Inteesar,har ya wannan lokacin Muhdeen bai ba Inteesar wayarta ta ba.

Kwance take a saman cinyar Gwaggo suna fira, Mufida ce ta shigo.

"Assalamu alaikum"
Mi'kewa Inteesar ta yi da fara'arta ta rungume Mufida, Mufida ce ta gaida Gwaggo sannan ta juya ta kalli Inteesar ta ce,
"Wai me ya samu wayarki ne?"
Ta'be baki Inteesar ta yi tare da cewa
"Ba abunda ya same ta"
"Mummy na ta kiranki bata shiga, the same thing."
"Waya ta tana wajen yaya."
Kallon mamaki tayi Mata
"Me wayarki yake yi a wajensa?"
"Kar'bewa yayi wai bazai bani ba."
"Me ya faru haka da zafi da zai kar'be maki waya?"
Shiru Inteesar tayi tana nazari don bata jin zata iya sanar da kowa halin zaman da suke yi da Muhdeen,duk da cewar Mufida k'awarta ce amma ai kuma k'anwa ce a gurin Muhdeen,don haka ta ce,
"Mubaar maganar kawai"
"Me kuma kike 'boye mani Inteesar?mufa aminan juna ne bana 'boye maki komai kema baki 'boye mani,amma tunda kika yi aure kika fara mani 'boye-'boye."
Dariya ta yi tare da kallon Mufida.

"To ai kema kinsani akwai Banbanci tsakanin matar aure da wacce ba matar aure,kuma ai duk mace ta gari bata fitar da sirrin gidanta."
Ta'be baki Mufida ta yi tare da cewa
"To mace ta gari,idan miji na gari na ciki kije ki sanar da shi Mahaifiyar k'awarki Wasila ta rasu."
Dafe k'irji Inteesar tayi tare de cewa
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un,Yaushe ta rasu?"
"Jiya"
Salatin Inteesar ne yasa hankalin Gwaggo ta dawo gare su,don ta yi nisa waje kallon T.V
"Allah sarki Allah ya jik'anta da rahama."
Gaba d'ayansu suka amsa, Mufida ce ta kalli Gwaggo ta ce
"Dama can gidan rasuwar zanje,na kira Inteesar a waya na sanar da ita amma ban same ta ba,shine na ce bari na biyo ko zata samu zuwa."
Kallonta Gwaggo tayi tare da cewa
"Gashi mijinki baya gidan bare ki nemi izininsa ki bita ku tafi."
Marairaice fuska tayi
"Gwaggo ki barni na tafi idan ya dawo sai a sanar dashi."
Girgiza kai Gwaggo tayi tare da cewa
"Ba nice na ajiye ki ba,ba kuma zama na kike ba,saboda haka ki kirashi a waya ki nemi izininsa,idan ya amince sai ku tafi."
Shiru Inteesar ta yi tana tunanin ta ina ma zata fara,dan ita ko kashe ta ma za'ayi bata san lamabar wayarsa ba,Mufida ce ta ce,
"Yauwa bari na kira maki shi da waya ta,idan ya barki sai muntafi."
Murmushi kawai ta yi a zuciyarta tana addu'ar Allah yasa ya amince ya barta.
Chapter 48 · 0% Book details