Sashe 74
Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Koda ya k'arasa k'ofar gidaan Salisu ya same sa yana jiransa, Salisu me ya k'araso ya bud'e murfin motar Muhdeen ya shiga ciki, hannu ya mik'a masa suka gaisa kafin ya ce,
"Mutumi na lafiya kake kuwa? naga kayi wani zuru-zauru?"
Ajiyar zuciya ya sauke ya ce,
Ba dole kaga na rame ba?Salisu ina cikin tashin hankali?wallahi akwai damuwa sosai a tattare da ni, banga Inteesar ba tun jiya da safe rabo na da ita, tunda aka kira ni da sassafe a Asibiti akayi mani kiran gaggawa na tafi na barta tana barci, koda na dawo gida da rana banganta ba, abu kamar wasa har yau ba ita ba labarinta."
"Inalillahi wa'inna ilaihi raji'un,kunyi fad'a da ita ne? yasa ta tafi ta barka?sannan yakamata ka je gidan iyayenta dan ba zata wuce can ba."
"Salisu bata gidan iyayenta kuma bata gidan iyayae na, nasa Mufida ta kira dukkan k'awayensu ta tambaye su ko ta je can, nan ma sun tabbatar da cewa bata gidansu, duk inda yakamata ace ta je bata nan."
"Kuma bansan inda ta shiga ba, kuma ni fargabar da nake kada ya kasance ta fad'a mugun hannu, idan wani abu ya same ta bazan iya jurewa ba."
Ajiyar zuciya Salisu yayi tare da cewa
"To yanzun neye mafita?"
"Ko zamuje police station ne da gidan redo ko Allah zaisa a dace."
Take Muhdeen yayiwa motar key suka tafi police station, sukayi report daga nan suka nufi gidan redio ,bayan sunbar gidan redio ne suna tafiya akan hanyarsu ne yayi parking a gefen hanya, Salisu ya kalle sa ya ce,
"Lafiya ka tsaya ko akwai wata matsalar ne?"
Girgiza kansa yayi cikin yanayi na damuwa da yake ciki ne ya kalle shi ya ce,
"Wane lafiya kuma zaka tambaye ni? bayan kasan halin da nake ciki ai ba lafiya, har sai ranar da naga mata ta sannan hankali na zai kwanta."
"Kada ka damu ka kwantar da hankalinka addu'a ce kawai mafita a gare ka, duk abunda yayi tsanani sauk'i na zuwa, insha Allah zamu same ta cikin k'oshin lafiya Allah zai bayyana muna ita aduk inda take, nasan yadda kake ji a zuciyarka amma amma ka daure kayi ta addu'a har Allah ya bayyana mata."
Murmushi Muhdeen yayi tare da cewa
"Naji dad'in kalamanka Salisu har cikin raina, hak'ik'a tunda wannan abun ya faru ba wanda ya ta'ba fad'a mani magana mai dad'i kwatankwacin wanda ka fad'a mani, ba wanda ya nuna damuwarsa akan lamari na sai kai, hatta aminina Jabeer bai damu da halin da nake ciki ba, babbar abunda zai baka mamaki ma Mummy da Dady cewa sukayi wai na nemo ta duk inda ta ke."
Haka Salisu yayi ta bashi baki yana kwantar masa da hankali, sai da ya tabbatar ya d'an saki ransa kafin suka cigaba da tafiya, sauke shi yayi a k'ofar gida inda ya ajiyae shi kafin yaja motarsa ya nufi gidansa.
Koda ya shiga ba kowa a falo don ko motsin Sumayya bai ji ba, da alama bata gidan ta fita kenan, kai tsaye d'akinsa ya nufa, lokacin k'arfe d'aya na rana komai baici ba bai sha ba, rabonsa da abinci tun jiya da yasha yoghurt bai sake saka ko da ruwa a cikinsa ba, gashi wani masifaffen yunwa yake ji na addabarsa amma baya jin zai iya cin abincin duk da yunwar da ta addabe shi, toilet ya shiga yayi wanka ya fito ya saka kaya ya nufi masallaci, bayan an idar da sallah ne yayi addu'a sosai akan Allah ya bayyana masa Inteesar.
Daga masallaci gida ya dawo a falo ya d'an kishingid'a, ba abuda yake tunani sai Inteesar, tuna yadda ya dinga wahalar da ita da azabtar da ita tun kafin aurensu har ya zuwa bayan aurensu, ya tuna irin biyayyar da take masa duk k'untatawa da yake mata bata ta'ba tsallake maganarsa ba, duk abunda ya umarce ta da tayi sai tayi shi koda hakan zai zama bak'in cikinta ne, zata yi masa indai zai faranta ransa, bata damu da halin da zata shiga ba.
Nadama ce ta kama sa tare da danasanin abunda yayi mata a baya, tabbasa da zai ganata yanzun zai gyara kura kuransa ne, ya nuna mata kulawa da k'aunar da yake mata, yana nan zaune ya shagala da tunani bai ankara ba sai jin Kiran sallar la'asar yayi, mik'ewa yayi ya d'auro alwala ya nufi masallaci, kuma har lokacin baici komai ba a cikinsa, bayan idar da sallar ne ya d'auki motarsa ya koma gidan iyayensa.
Da sallama ya shiga falon Mummy ce zaune a falo, amsa sallama tayi masa tare da kallonsa, ganin yadda ya rame cikin k'ank'anin lokaci yiyi zuru-zauru kamar ba shi ba, mamaki ne ya kamata ganin ramar da yayi, a tunaninta baya son Inteesar kamar yadda ta sani, amma yanzun ganin yadda ya koma ne yasa ta shakku akan abunda ta sani, domin kuwa don idan baya sonta bai kamata a ce ya shiga damuwa har haka ba, kenan yana sonta? to me yasa ya wulak'anta ta alhalin ya damu da ita har haka, uwa uwa ce duk da tana fushi da shi amma bata ji dad'in ganinsa haka ba.
K'arasowa yayi ya durk'usa a gabanta
"Ina wuni Mummy?"
Ba yabo ba fallasa ta amsa masa
"Lafiya lau"
Zama yayi a saman center carpet dake falon, daga shi har Mummy ba wanda yayi magana, ganinsa tayi da alamar yunwa a tattare da shi, dan haka ta kalle shi ta ce,
"Ka zo ka ci abinci"
Bata jira cewarsa ba ta nufi dinning area, bin bayanta yayi duk da ba jin cin abincin yake ba amma yaji dad'i, ganin Mummy wannan karon ta d'an kula da shi, zama yayi a d'aya daga cikin dinning d'in tayi serving d'insa, white rice and stew ne da ya ji naman kaza, kunun aya da ta zuba masa a cup ya fara sha, take gabansa ya fad'i, don tabbas idan har Inteesar tayi masa kunun aya haka yake jin d'and'anonsa, abincin ya d'eba da cokali yakai bakinsa ya tauna a zabure ya mik'a tsaye, kallonsa Mummy tayi tare da cewa
"Lafiya kuwa?"
"Mummy ina take?"
Da mamaki ta kalle shi ta ce,
"Wake nen?"
"Mummy Inteesar tana gidan nan, me yasa aka mani haka?"
"Waye ya ce maka tana gidan nan?"
"Mummy ba wanda ya fad'i mani amma tana gidan nan, don wannan abincin da na ci tabbas ita ta dafa shi, wannan kunun aya ma ita ce ta had'a shi, tunda na d'and'ana abincin nan nasan ita ta girka shi wannan d'and'anon girkinta ne, nasan d'and'anon girkinta nasan naki wallahi Umma ita ce ta girka shi, kuma tana cikin gidan nan."
Mik'ewa yayi ya nufi falo yana k'wala mata kira da k'arfi
"INTEESAR!
INTEESAR!!
INTEESAR!!!"
Inteesar dake zaune a akan sallaya sanye da hijab, tunda ta idar da sallar la'asar bata tashi ba ta zauna tana azkar, gabanta ne ya fad'i jin muryarsa yana k'wala mata Kira yasa gabanta ya fad'i ta furta kalmar
"Inalillahi wa'inna ilaihi raji'un"
Dama ita kad'ai ce a d'akin Mufida ta fita Mummy ta aike ta gidan Aunty Abla, Gwaggo dake d'akinta ta fito tana cewa
"Wannan kuma haukar me yake mana a gida ne?
Kazo kana d'agawa mutane murya ."
Ranasa a 'bace yake kallon Gwaggo, yana shirin bata amsa ne sai idonsa ya sauka akan dady dake saukowa, kallon fusakar Dadyn yayi a murtuk'e ya ce,
"Muhammad fitar mani a gida."
Da ya ke kallon Dady jin kalmar bakinsa, bud'e baki yayi da niyyar magana Dady ya d'aga masa hannu alamun dakatarwa ya ce,
"Get out in my house"
Yadda yayi maganaar a tsawa ce, da ganin irin 'bacin ran da ya gani a fuskar Dady yasa ya nufi hanyar fita.
A harabar gidan ya had'u da Mufida da suka dawo da Direb, ganinsa ta tasan akwai damuwa, da har zai wuce sai ya tamabaye ta
"Da Inteesar tazo gidan nan mai ta sanar da su Dady da Mummy ne?"
"Nima ban sani ba"
"Kada kiyi mani k'arya ki sanar da ni gaskiya, me ke faruwa da kowa ya d'auki zafi da ni."
"Yaya ai dole kowa ya d'auki zafi da kai, da badon Allah yasa munje gidanka ba kuma Allah yasa tana da sauran numfashi ai da wani zancen ake ba wannan ba."
Kallon rashin fahimta yake mata kafin ya sake tambayarta
"Kamar ya please ki sanar dani abunda ya shige Mani duhu."
Ajiyar zuciya ta sauke sanan ta bashi labarin yadda suka tafi gidansa ita da Mummy, suka tarar da Inteesar kwance bata numfashi, kanta na fitar da jini, ta kuma tabbatar masa da cewa Sumayya ce tayi yunk'urin kashe Inteesar, take idanunsa suka kad'a zuwa ja jikinsa gar rawa yake, ya. nufi motarsa cikin k'unar rai da fusata ya shiga motarsa, key yayi mata ya dinga danna horn sai da kiwa ya firgita da yadda ya dinga horn, Mallam Ibrahim mai gadi ya wangale masa gate ya fita a guje zuciyarsana masa zugi, Mallam Ibrahim ya kalli bayan motar ya ce,
"Allah dai ya kiyaye hanya amma wannan tuk'in akwai hatsari a cikinsa."
*DAGA ALK'ALAMIN*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
*Don k'arin bayani*
09065327995
Love you oll
Comments & shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izinina ba.
*SANARWA*
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubuta shi dan cin zarafi ga kowa ba, idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarce ni bada niyar yin hakan nayi ba, arashi ne mai kashe auren wawa.
*BISIMILLAHI RAHAMANI RAHEEM*
Page6
"Allah dai ya kiyaye hanya, amma wannan tuk'in akwai hatsari a cikinsa.
Driving yake kamar zai tashi sama, gaba d'aya Allah kawai ne zai kaishi gida lafiya, gudu kawai yake akan titi kamar zai tashi sama.
"Mutumi na lafiya kake kuwa? naga kayi wani zuru-zauru?"
Ajiyar zuciya ya sauke ya ce,
Ba dole kaga na rame ba?Salisu ina cikin tashin hankali?wallahi akwai damuwa sosai a tattare da ni, banga Inteesar ba tun jiya da safe rabo na da ita, tunda aka kira ni da sassafe a Asibiti akayi mani kiran gaggawa na tafi na barta tana barci, koda na dawo gida da rana banganta ba, abu kamar wasa har yau ba ita ba labarinta."
"Inalillahi wa'inna ilaihi raji'un,kunyi fad'a da ita ne? yasa ta tafi ta barka?sannan yakamata ka je gidan iyayenta dan ba zata wuce can ba."
"Salisu bata gidan iyayenta kuma bata gidan iyayae na, nasa Mufida ta kira dukkan k'awayensu ta tambaye su ko ta je can, nan ma sun tabbatar da cewa bata gidansu, duk inda yakamata ace ta je bata nan."
"Kuma bansan inda ta shiga ba, kuma ni fargabar da nake kada ya kasance ta fad'a mugun hannu, idan wani abu ya same ta bazan iya jurewa ba."
Ajiyar zuciya Salisu yayi tare da cewa
"To yanzun neye mafita?"
"Ko zamuje police station ne da gidan redo ko Allah zaisa a dace."
Take Muhdeen yayiwa motar key suka tafi police station, sukayi report daga nan suka nufi gidan redio ,bayan sunbar gidan redio ne suna tafiya akan hanyarsu ne yayi parking a gefen hanya, Salisu ya kalle sa ya ce,
"Lafiya ka tsaya ko akwai wata matsalar ne?"
Girgiza kansa yayi cikin yanayi na damuwa da yake ciki ne ya kalle shi ya ce,
"Wane lafiya kuma zaka tambaye ni? bayan kasan halin da nake ciki ai ba lafiya, har sai ranar da naga mata ta sannan hankali na zai kwanta."
"Kada ka damu ka kwantar da hankalinka addu'a ce kawai mafita a gare ka, duk abunda yayi tsanani sauk'i na zuwa, insha Allah zamu same ta cikin k'oshin lafiya Allah zai bayyana muna ita aduk inda take, nasan yadda kake ji a zuciyarka amma amma ka daure kayi ta addu'a har Allah ya bayyana mata."
Murmushi Muhdeen yayi tare da cewa
"Naji dad'in kalamanka Salisu har cikin raina, hak'ik'a tunda wannan abun ya faru ba wanda ya ta'ba fad'a mani magana mai dad'i kwatankwacin wanda ka fad'a mani, ba wanda ya nuna damuwarsa akan lamari na sai kai, hatta aminina Jabeer bai damu da halin da nake ciki ba, babbar abunda zai baka mamaki ma Mummy da Dady cewa sukayi wai na nemo ta duk inda ta ke."
Haka Salisu yayi ta bashi baki yana kwantar masa da hankali, sai da ya tabbatar ya d'an saki ransa kafin suka cigaba da tafiya, sauke shi yayi a k'ofar gida inda ya ajiyae shi kafin yaja motarsa ya nufi gidansa.
Koda ya shiga ba kowa a falo don ko motsin Sumayya bai ji ba, da alama bata gidan ta fita kenan, kai tsaye d'akinsa ya nufa, lokacin k'arfe d'aya na rana komai baici ba bai sha ba, rabonsa da abinci tun jiya da yasha yoghurt bai sake saka ko da ruwa a cikinsa ba, gashi wani masifaffen yunwa yake ji na addabarsa amma baya jin zai iya cin abincin duk da yunwar da ta addabe shi, toilet ya shiga yayi wanka ya fito ya saka kaya ya nufi masallaci, bayan an idar da sallah ne yayi addu'a sosai akan Allah ya bayyana masa Inteesar.
Daga masallaci gida ya dawo a falo ya d'an kishingid'a, ba abuda yake tunani sai Inteesar, tuna yadda ya dinga wahalar da ita da azabtar da ita tun kafin aurensu har ya zuwa bayan aurensu, ya tuna irin biyayyar da take masa duk k'untatawa da yake mata bata ta'ba tsallake maganarsa ba, duk abunda ya umarce ta da tayi sai tayi shi koda hakan zai zama bak'in cikinta ne, zata yi masa indai zai faranta ransa, bata damu da halin da zata shiga ba.
Nadama ce ta kama sa tare da danasanin abunda yayi mata a baya, tabbasa da zai ganata yanzun zai gyara kura kuransa ne, ya nuna mata kulawa da k'aunar da yake mata, yana nan zaune ya shagala da tunani bai ankara ba sai jin Kiran sallar la'asar yayi, mik'ewa yayi ya d'auro alwala ya nufi masallaci, kuma har lokacin baici komai ba a cikinsa, bayan idar da sallar ne ya d'auki motarsa ya koma gidan iyayensa.
Da sallama ya shiga falon Mummy ce zaune a falo, amsa sallama tayi masa tare da kallonsa, ganin yadda ya rame cikin k'ank'anin lokaci yiyi zuru-zauru kamar ba shi ba, mamaki ne ya kamata ganin ramar da yayi, a tunaninta baya son Inteesar kamar yadda ta sani, amma yanzun ganin yadda ya koma ne yasa ta shakku akan abunda ta sani, domin kuwa don idan baya sonta bai kamata a ce ya shiga damuwa har haka ba, kenan yana sonta? to me yasa ya wulak'anta ta alhalin ya damu da ita har haka, uwa uwa ce duk da tana fushi da shi amma bata ji dad'in ganinsa haka ba.
K'arasowa yayi ya durk'usa a gabanta
"Ina wuni Mummy?"
Ba yabo ba fallasa ta amsa masa
"Lafiya lau"
Zama yayi a saman center carpet dake falon, daga shi har Mummy ba wanda yayi magana, ganinsa tayi da alamar yunwa a tattare da shi, dan haka ta kalle shi ta ce,
"Ka zo ka ci abinci"
Bata jira cewarsa ba ta nufi dinning area, bin bayanta yayi duk da ba jin cin abincin yake ba amma yaji dad'i, ganin Mummy wannan karon ta d'an kula da shi, zama yayi a d'aya daga cikin dinning d'in tayi serving d'insa, white rice and stew ne da ya ji naman kaza, kunun aya da ta zuba masa a cup ya fara sha, take gabansa ya fad'i, don tabbas idan har Inteesar tayi masa kunun aya haka yake jin d'and'anonsa, abincin ya d'eba da cokali yakai bakinsa ya tauna a zabure ya mik'a tsaye, kallonsa Mummy tayi tare da cewa
"Lafiya kuwa?"
"Mummy ina take?"
Da mamaki ta kalle shi ta ce,
"Wake nen?"
"Mummy Inteesar tana gidan nan, me yasa aka mani haka?"
"Waye ya ce maka tana gidan nan?"
"Mummy ba wanda ya fad'i mani amma tana gidan nan, don wannan abincin da na ci tabbas ita ta dafa shi, wannan kunun aya ma ita ce ta had'a shi, tunda na d'and'ana abincin nan nasan ita ta girka shi wannan d'and'anon girkinta ne, nasan d'and'anon girkinta nasan naki wallahi Umma ita ce ta girka shi, kuma tana cikin gidan nan."
Mik'ewa yayi ya nufi falo yana k'wala mata kira da k'arfi
"INTEESAR!
INTEESAR!!
INTEESAR!!!"
Inteesar dake zaune a akan sallaya sanye da hijab, tunda ta idar da sallar la'asar bata tashi ba ta zauna tana azkar, gabanta ne ya fad'i jin muryarsa yana k'wala mata Kira yasa gabanta ya fad'i ta furta kalmar
"Inalillahi wa'inna ilaihi raji'un"
Dama ita kad'ai ce a d'akin Mufida ta fita Mummy ta aike ta gidan Aunty Abla, Gwaggo dake d'akinta ta fito tana cewa
"Wannan kuma haukar me yake mana a gida ne?
Kazo kana d'agawa mutane murya ."
Ranasa a 'bace yake kallon Gwaggo, yana shirin bata amsa ne sai idonsa ya sauka akan dady dake saukowa, kallon fusakar Dadyn yayi a murtuk'e ya ce,
"Muhammad fitar mani a gida."
Da ya ke kallon Dady jin kalmar bakinsa, bud'e baki yayi da niyyar magana Dady ya d'aga masa hannu alamun dakatarwa ya ce,
"Get out in my house"
Yadda yayi maganaar a tsawa ce, da ganin irin 'bacin ran da ya gani a fuskar Dady yasa ya nufi hanyar fita.
A harabar gidan ya had'u da Mufida da suka dawo da Direb, ganinsa ta tasan akwai damuwa, da har zai wuce sai ya tamabaye ta
"Da Inteesar tazo gidan nan mai ta sanar da su Dady da Mummy ne?"
"Nima ban sani ba"
"Kada kiyi mani k'arya ki sanar da ni gaskiya, me ke faruwa da kowa ya d'auki zafi da ni."
"Yaya ai dole kowa ya d'auki zafi da kai, da badon Allah yasa munje gidanka ba kuma Allah yasa tana da sauran numfashi ai da wani zancen ake ba wannan ba."
Kallon rashin fahimta yake mata kafin ya sake tambayarta
"Kamar ya please ki sanar dani abunda ya shige Mani duhu."
Ajiyar zuciya ta sauke sanan ta bashi labarin yadda suka tafi gidansa ita da Mummy, suka tarar da Inteesar kwance bata numfashi, kanta na fitar da jini, ta kuma tabbatar masa da cewa Sumayya ce tayi yunk'urin kashe Inteesar, take idanunsa suka kad'a zuwa ja jikinsa gar rawa yake, ya. nufi motarsa cikin k'unar rai da fusata ya shiga motarsa, key yayi mata ya dinga danna horn sai da kiwa ya firgita da yadda ya dinga horn, Mallam Ibrahim mai gadi ya wangale masa gate ya fita a guje zuciyarsana masa zugi, Mallam Ibrahim ya kalli bayan motar ya ce,
"Allah dai ya kiyaye hanya amma wannan tuk'in akwai hatsari a cikinsa."
*DAGA ALK'ALAMIN*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
*Don k'arin bayani*
09065327995
Love you oll
Comments & shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izinina ba.
*SANARWA*
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubuta shi dan cin zarafi ga kowa ba, idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarce ni bada niyar yin hakan nayi ba, arashi ne mai kashe auren wawa.
*BISIMILLAHI RAHAMANI RAHEEM*
Page6
"Allah dai ya kiyaye hanya, amma wannan tuk'in akwai hatsari a cikinsa.
Driving yake kamar zai tashi sama, gaba d'aya Allah kawai ne zai kaishi gida lafiya, gudu kawai yake akan titi kamar zai tashi sama.