← Book details Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 99

Sashe 5

Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A cikin kwana biyu aka gama shiryawa Inteesar komai na makarantar an basu inda ta fara karatu class d'in su daya da Mufida jss 3 kullun direban gidan su mufida zai kaisu, Inteesar da wuri take shirywa Don idan ta idar da sallar asuba tayi azkar bata kuma kwanciya barci,zata hura wuta tayi wanke-wanke ta gyara d'akin ta da share tsakr gidan idan Koko zasusha ta dama idan kuma d'umame ne tayi kafin karfe bakwai ta gama ayyukan gidan nan ta karya karfe bakwai zata nufi gidan su mufida,kullun idan taje takan samu Mummy a kitchen tana had'a breakfast,haka zataje ta tayata su kammala,ko Mummy tayi ta fama da ita taci wani abun ko tea tasha amma sai tak'i.wata rana ma ita take taya Mufida shiryawa don idan ta Mufida ce sai suyi lettin zuwa school, Ita kuma Asiya tunda ba school d'aya suke ba bata bi ta kansu,ko gaisuwar Inteesar ma Bata amsawa sai dai idan taga idanun mummy,don kallo wulakanci take mata,don bata d'auko halin Mummy ba tana da kyamatar talaka gata mishkila ce,Dady ma ya nunawa Inteesar k'auna da kulawa,musamman da yaga matar sa da kuma autar sa Mufida suna k'aunar Inteesar Shima yake kaunar ta kamar shi ya haife ta,don ko abu zai siyowa yaran nasa guda uku yake siyo komai Asiya, mufida, inteesar.haka 'bangaren mummy komai tar take masu ko Kaya ne dinki ma iri daya ne take masu,haka takalma da d'an kunne,kayan kwalliya gyale ne kawai idan zata siya masu sai ta siyawa Inteesar Hijab kasancewar Bata saka gyale ko ansiye Mata zata a jiye shi ne,Abban Inteesar da Ummata ma takanas sukazo yiwa Dady da Mummy godiyar d'awainiyar da suke da 'yar su, Mummy tana son kowane lokaci Inteesar tana gidan ta,
Wata rana Da yamma Inteesar tana zaune a tsakiyar gidan su tana wanke-wanke.Mufidaa tayi sallama ta shigo da far'ar ta ta k'araso cikin Jin dadi take cewa Inteesar Babban yayan mu ya dawo kizo muje ki gansa,dama baki taba ganin sa ba.

Cikin Jin dadi tace,
"Haba da gaske kikeyi"?

Murmushi Jin dadi Mufida tayi kafin tayi magana ne umma ta fito daga d'aki tana kallon Mufida ta ce,
"Mufida kece a gidan namu?"
Durk'usawa tayi ta gaida Umma
"Ina yini Umma?"
"Lapiya qalau ya mutanen gidan?"
Cikin yanayin da take ciki na jindadi tace
"Umma Yayan mu ya dawo shine nazo Kiran Inteesar tazo su gaisa."
"Masha Allahwanda yake can kasar turai ko?"
Cewar umma
"Eh umma"
Da-dai lokacin Inteesar ta k'arasa gama wanke-wanke ta saka hijab Mufida taja hannun ta suka tafi tana sallamar Umma.

"Umma sai na dawo"
"To ki gaishe su."
Koda suka karasa gidan a falon ba kowa kowa yayi d'aki,dama sun Dad'e suna fira kasancewar da ya iso Mufida na barci bata sani ba ta farka ne ta gansa take sanar da aminiyar ta.

Kai tsaye part din sa suka nufa baya falo, knocking Mufida sukayi yabada izinin shiga.da sallama suka shiga ya na magana da wani a waya da alama abokin sa ne,yana tozali da Inteesar gabansa ya fad'i ya mik'e da sauri tare da cire wayar a kunnen sa,kallon mamaki yake mata,don tabbas itace yarinyar da yake gani cikin mafarkinsa ,nuna ta yayi da yatsa tare da furta
" kee!"
Daga alk'amin
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
*DON K'ARIN BAYANI*
09065327995
Love u oll
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace ba tare da izini na ba.

Wannan kagaggen labari ne, banyi tunanin rubutashiubuta ta Shi dan cinzarafi ga kowa ba.idan suna ko hali yazo daya to ku gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba.Arashi ne Mai kashe Auren Wawa.
*BISMILLAHIR RAHMANI RAHIM*
Page0
Nuna ta yayi da yatsa tare da furta
"Kee!"
Inteesar cikin tsananin mamaki take kallon shi ganin yadda yake Mata kallon mamaki,alhalin ita bata ta'ba ganin sa ba,
Acikin zuciyar ta kuwa ta ce,
"Anya kuwa wannan mutumim Yana da hankali?duk yabi ya rikice har da tambayar ta Wai ni ce?alhalin ban taba ganin sa ba."
Muryar mufida ce ta katsae ta Jin tana cewa,
"Yaya lapiya kuwa?"
K'ok'arin dai daita nutsuwar sa yayi don kada su fahimci wani abu game dashi,sannan ya ce,
"Babu komai"
Murmushi tayi tare da kamo hannun Inteesar din ta ce,
"Yaya wannan itace Inteesar d'in da nake baka labari"
Kai ya gyad'a ba tare da ya kalle su ba.inteesar ce tadan durk'usa cikin girmamawa ta ce,
"Ina yini?"
"Lafiya"
Ya amsa Mata a gajerce ba tare da ya kalle ta ba,ta Kara cewa
"kadawo lafiya?"
Bai kalle ta ba,balle tasa ran zai amsa kallon Mufida yayi tare da yamutse fuska yace,
"Pls kud'an fita dan ina son na Dan huta."
Kwa'be Fuska ta tare da cewa
"Yaya Wai yau nice kake Kora daga d'akin ka abunda baka taba yi maniba?"
Jinjina Kai ta yi
" Koda kanajin barci sai dai idan nice naga alamun haka na fita?

Kuma gani tare da k'awa ta sannan ko gaisuwar kirki baku..."
Dakatar da ita yayi ta hanyar daga Mata hannu,sanan ya nuna Mata kofar fita yace "please"
Rau rau tayi da idanu kamar zatayi kuka,taja hannun Inteesar suka fice daga dak'in,suna fita ya samu yayi ajiyar zuciya,don har ga Allah baiji dad'in abunda da yawa k'anwar tasu ba,amma ba yadda yadda iya dole yayi hakan ki zai samu sassauci, domin tunda ya kalli Inteesar gabansa yake ta lugude don ya girgiza da ganin ta.fitar nata shine samun sau'kin sa.

Bangaren su Mufida kuwa suna barin d'akin sa Kai tsaye d'akin Mummy suka nufa, Inteesar ce kadai tayi sallama Mufida kuwa idanun ta tab da kwallah suke,kadan take jiran tayi kuka, Mummy dake shirya kayan da mai masu wanki da guga ya kawo ne take shiya su a cikin wardrobe din kayana ta.

Juyowa tayi ta kalle su ganin su cikin wani yanayin yasa ta dakatar da abunda takeyi ta karaso bakin gadon ta janyo hannayen su ta zauna dasu bakin gadon tare da cewa,
"ku lapiya kuwa?me ya faru?"
Cikin shagwaba ta da muryar kuka take cewa,
"Wai daga mun shiga mu gaida Yaya Inteesar da bata San shi ba sai a photo nace muje ta gaishe sa,shine kawai harda korar mu ko gaisuwar ta bai amsa ba."
Ido Mummy ta zuba masu tare da yin tunanin ko me yasa yayi masu hakan?

"Kunga wata K'ila akwai abunda ke damun sa ne,kuma kun cika shi da suruta.ke mufida ai kinsan baya son hayaniya,wata Kila shiyasa ya Kore ku,Amma kada hakan ya dame ku kuyi hak'uri kunji?"
Ta karasa maganar tana shafar gefen fuskokin su
Mufida tayi saurin cewa
"Wlh ba hayaniyar da muka damesa dashi,ko gaisuwar kirki basuyi ba.

To naji ku saki ranku sai dai idan akwai abunda yake damun sa.cewar mummy kenan."
Mik'ewa tayi ta nufi d'akin sa,Murda handle din kofar tayi tare da yin sallama.zaune yake bakin gadon say yayi tagumi.jin muryar Mummy ce yasa ya amsa sallamar tare da amsa sallamar da tayi masa.

Murmushi ya k'ak'alo ganin mummy ta zuba masa idanu Tana karantar yanayin sa.

"Mummy sannu da shigowa"
"Yauwa "
tace tare da karasawa ta zauna saman side drawer.

"Son lapiyar ka kuwa ko akwai abunda yake damun ka ne ban sani ba?"
Murmushi ya k'ak'alo wanda iya fatar bakin sa ta tsaya,bata Kai zuci ba.

"Lapiya qalau Mummy kawai dai nagaji ne"
Kai ta girgiza tare da cewa,
"Akwai mana son,nifa mahaifiyar ka ce idan ma kana cikin damuwa ka sanar dani mana,kada ka boye Mani."
"Kada ki damu Mummy gajiya ce,I will be fine."
Mikewa tayi tace
"To shikenan tunda haka kace,amma baikamta ko Kori kannen ka ba,da suka shigo gaishe ka,musamman ma Inteesar da karon faroko kenan tasan ka,tazo kaishe ka sannan zaka kure su?"
Jinjina Kai yayi alamun gamsuwa
"To Mummy insha Allah hakan bazata sake faruwa ba,daga ta fita tabar masa dakin."
Haka rayuwa tayi ta tafiya yayin da Mummy da Dady da kuma mufida ke Kara k'aunar Inteesar,don har mommy taso a ce Inteesar ta dawo gidanta da zama gaba d'aya,amma ganin cewa ita kad'ai iyayen ta suka haifa kuma tana taimaka wa mahaifiyarta da aikace-aikacen gida gida yasa ta ha'kura.kullun Inteesar idan ta idar da sallar asuba tayi azkar Bata kuma kwanciya zata Fara aikace-aikacen gida,shara wanke kwanuka d'ora masu abun abun da zasuyi kalaci dashi wankin bandaki gyaran d'akunan gidan duk itace.kuma kafin karfe bakwai ta gama komai tayi Shirin zuwa school bayan ta gaida iyayen ta ta sallame su.kai tsaye zata nufi hanyar gidan su Mufida kullu taje zata 9tarar da ma'aikatan gidan nata aiki tunda kan Mai gadi da Mai bawa fulawa ruwa da masu sharar harabar gidan da masu goge windows kowa na aiki harda Mai wankin mota.sai da ta gaishe su sannan ta nufi cikin gidan,nan ta tarar da Mai aikin su tana goge-goge Mummy kuwa kullum tana kitchen Tana hada breakfast din mutanen gidan.Yayin da jummai ke girka na ma'aikatan gidan.don Dady bayason Abincin masu aiki.kullun sai Inteesar sai ta taya mummy karasa hada breakfast tajira mufida tayi breakfast sannan su tafi.

A bangaren Muhdeen kuwa sai K'ara tsanr yarinyar yakeyi a cikin zuciyar sa.har ita kanta Inteesar din ta fahimci hakan.cewa baya kaunar ta Wanda ita kanta ta rasa dalilin da yasa haka.don ko had a ido sukayi zai galla Mata harara ko ta gaishe sa sai dai idan a gaban mutanen gidan ne yake amsawa idan basu nan kuwa ki ta gaishe say sai yayi tsaki ko ya harare ta
Kwanci tashi asarar Mai rai.har muhdeen ya kammala karatun sa na likitanci ya dawo Nigeria inda Dady ya gina masa Babban Asibiti a nan cikin garin Minna.inda Jabir wato d'an yayan Dady zasu dinga tafiyar da asibitin a tare,don Shima abunda ya karanta kenan.
Chapter 5 · 0% Book details