← Book details Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 99

Sashe 41

Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A hankali ya bud'e idanunsa a kanta
"Dan tsabar iskanci da wulak'anci kika shanyani ina jirnaki ko?"
"Kayi hak'uri"
"Bari na fad'a maki abu d'aya mintuna talatin na baki kiyi a cikin gidanku,kada ki wuce haka,kina jina ko?"
Kai ta jinjina masa
"Dan Allah ka k'ara mani lokaci kaga Abbana baya nan koda awa d'aya ne ka k'ara mani don Allah."
"Bana son Musu umarni na baki."
Daga nan ta shige gaba suka nufi cikin gidan tana gaba Yana biye da ita a baya.
*KUYI HAKURI DA WANNAN BA LALLAI BANE NA DINGA MAKU POSTING WEEKEND DAN BANA SAMUN ISASHSHEN LOKACI*
Daga alk'amin
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
Don k'arin bayani
09065327995
Love u oll
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izini na ba.

Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi kowa ba,idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba arashi ne mai kashe auren wawa.
*BISIMILLAHI RAHMANI RAHEEM*
Page 4
Daga nan ta shige gaba suka nufi cikin gidan tana gaba yana biye da ita a baya.

Tun a bakin k'ofar zauren ya yi sallama,Umma ta lek'o ta amsa masa sallamar tare da ce masa ya shigo, takalminsa ya cire a k'ofar d'akin.

"Assalamu Alaikum"
"Wa'alaika salam"
Shiga cikin d'aki.

Ya yi ya durk'usa k'asa
"Ina wuni Umma?"
"Lafiya lau Muhammad ya aiki,ya kuma hak'uri?"
Sunkuyar da kai ya yi tare da sakin murmushi
"Alhamdulillah"
Kallon Inteesar Umma ta yi tare da cewa
"Kawo masa ruwa mana"
Mi'kewa Inteesar ta yi ta ta fita waje ta d'auko kofin silba da murfin sa tazo ta bud'e randar k'asa ta d'ebo ruwan cikinta mai sanyi kamar na fridge,ta rufe kofin ta nufi d'akin a zuciyarta tana cewa nasan ma ba Shan wannan ruwan zaiyi ba,mutumin da ya saba da shan ruwan gora ta ina ma zai iya Shan wannan ruwan namu bari dai na kai masa.

Da sallama ta shiga d'akin inda ta ajiye masa ruwan a gabansa,itama ta zauna daga gefe.

"Muhammad ga ruwa kasha"
Murmushi ya yi tare da d'aukar bud'e murfin kofin ya d'auki ruwan ya sha,kallonsa Inteesar ta yi don bata ta'ba tunanin zaisha ba kasancewar shi muyum mai k'yank'ami,bayan yasha ne ya rufe kofin,kafin ya d'ora da cewa
"Abba baya gida ne?"
"Eh ya tafi kasuwa"
Kud'i ya ciro kimanin dubu a hamsin daga aljihunsa,ya ajiye a saman tabarmar sannan ya ce,
"Umma idan ya dawo a gaishe shi to sai na sake shigowa."
Umma ta nuna cewa yabar kud'in sunyi yawa ba za'ayi haka ba,ya nuna ba wani abu bane dan ya yi masu hidima,sallama ya yi ya fita inda Inteesar ta duba agogo saura mintuna ashirin cikin mintuna talatin da ya bata, ajiyar zuciya ta sauke tana tunananin cewa wata irin rayuwa ne wannan a ce a ce mace tazo gidan iyayenta ba za'a badi ta yini ba wai mintuna talatin ya bata.

A k'ofar gida kuwa wasu matasan samari su biyu Muhdeen ya gani sunzo wacewa ya kira su,but d'in motar ya bud'e kayan da suka tsaya ya siya a hanya ne ya ce su shiga dasu cikin gidan nan,buhun shinkafa ne da carton d'in taliya da makaroni,sai na semovita da maggi da galan man gyad'a da na manja,haka suka shiga nik'i -nik'i da kayan sallama suka yi Umma ta lek'o ganinsu nik'i -nik'i da kaya da mamaki ta tambaye su.

"Samari daga ina da kaya?"
"Wani ne da ya fito daga nan gidan ya ce mu shigo da kayan nan."
Da mamaki Umma ke kallon kayan har suka gama jidesu,ta juya ta kalli Inteesar ta ce,
"Inteesar mijin naki har da d'awainiya kuam?haba ai da baki badshi ya kashe kud'i da yawa haka ba ga kud'in da ya bamu ai d'awainiya ta yi yawa."
Inteesar dai bata ce komai ba,suka dinga kama kayan suna shigar dashi cikin d'aki.

Nan dai suka zauna suna firan bayan rabuwa,kafin Inteesar ta ankare har ta kwashe awa d'aya, lokacin da ta ankare gabanta ya fad'i rasss da k'arfi.

"Na shiga uku"
Da sauri Ummanta ta kalleta
"Lafiya me ya faru?"
Shiru ta d'anyi don bata son Ummanta tasan halin da take ciki kada ta saka damuwa a ranta,hakan yasa ta ce,
"Ina sauri ne Umma zan koma"
Da mamaki Umman nata ta kalleta
"Gida tun yanzun kuma? ba Zaki bari Abban naku ya zo ku gaisa ba?"
Murmushin ya k'e Inteesar ta yi
"Abunda ya sa zan tafi dama zanyi bak'i ne,lokacin da muna hanya ne suka sanar damu shine muka ce su d'an jira mu mun fita yanzun zamu dawo."
Ido Umman nata ta zuba mata,don Inteesar bata iya k'arya ba indai ta fad'i maganar da k'arya ce tsab yanayinta ke nunawa,hakan yasa Umma dai ta yi shiru Dan ta fahimci akwai abunda take 'boyewa,bata son k'ureta ne yasa ta dai yi shiru tare da cewa
"To shi mijin naki fa?"
"Yana jira na a mota"
Kai Umma ta jinjina ta ce,
"To shikenan tunda haka kika ce,zan k'ara mai maita maki zaman aure sai hak'uri ki k'ara hak'uri akan wanda kike da shi yi nayi bari na bari dan Allah kibi mijinki sau da k'afa ki zama mai hak'uri da juriya a gidan mininki.

"To Umma insha Allah"
Hawaye ne suka cika mata ido ta mayar da su day sauri ta nufi k'ofar fita ta fice,sai da ta Kai zauren gidan ta tsaya ta saki kukan da ya taso mata,sanna ta tsagaita tare da share hawayen ta fice gabanta na dukan uku uku ta fita waje,wajen motar ta nufa bud'ewa ta yi ta shiga bayan ta shiga ne ta rufe murfin motar,yana zaune waya ya ke da alama Jabeer ne ya kirasa a waya inda yake cewa.

"Badamuwa Jabeer,Kai da wa zakuzo goben ne?"
Daga can 'bangaren Jabeer ke cewa
"Nida Salisu ne da Bilyaminu,sai kuma Bashir dan har sunyi fushi ganin ko d'aurin auren baka sanar da su ba,na dai basu hak'uri sun ce gobe zasu zo suga amarya."
Shiru ya yi na d'an lokaci kafin ya d'aura da cewa
"Allah ya kaimu gaben sai kunzo."
Daga nan ya katse kiran ba tare da ya kalli Inteesar ba ya ce,
"Minti nawa na baki?"
Shiru ta yi kafin ta ce,
"Mintuna talatiin"
Jinjina kai ya yi
"Yanzun mintuna nawa kika yi?"
"Awa d'aya nayi wallahi muna fira da Ummana ne bansan lokaci ya yi nisa ba shiyasa."
Jin muryarta alamun ta yi kuka yasa ya kalleta
"Saboda baki son komawa yasa kike kuka?to ai da kin fad'a mata baki son zaman auren Kinga shikenan kowa ya huta,ko an fad'a maki nima son zama nake dake?ala dole ala lalurati yasa nake zaune dake,dama Zaki taimaka yanzun ki koma ki fad'a Mata cewar baki so na ba Zaki iya zaman aure da ni ba sai dai na sauwak'e maki,kuma yanzu.

Idan mun tafi gidanmu ki fad'awa Gwaggo cewa baki sona ba Zaki zauna dani ba wallahi da kin burgeni,ki nunawa Gwaggo cewa ita da ta had'a auren tasa na sauwak'e maki wallahi da kin burgeni ni,don sai na maki Babbar kyauta amma da ya ke mayya ce ke kika lik'e."
Shiru ta yi tana jinsa bata ce komai ba.

"Koda ya ke nan ba da dad'ewa ba zan sake ki ne, saboda Sumy na bata son zama da kishiya,buri na Komai ya dai daita ta dawo gida na a lokacin ke kuma Zaki bar gidan don wuta da auduga basa zama waje guda."
Tana jin sa irin munanan maganganun da yake fad'a mata bata ce komai ba,tada motar ya yi ya yin da yake cewa
"Isakancin banza daga mintuna talatin ta barni zaune ina jiranta sai da taga damar fitowa ta fito."
Gyad'a Kai ya yi tare da yin kwafa
"Kinci sa'a ba a gida muke ba da ace a gida muke da kika karya Mani doka wallahi sai kin gane kurenki."
Ya cigaba da driving yana ta ta fad'a ita dai uffan ba ta masa ba,har suka k'arasa k'ofar gidansu inda ya yi horn mai gadin gidan ya wangale masu gate.

Bayan ya shiga ya yi parking ne ya kalleta tare da cewa,
"Ina fatan baki mance da abunda na fad'a maki a baya ba ki? matuk'ar kika nunawa Mummy da Gwaggo wani alamu na rashin jituwa ko na rashin sabo da juna sai kin gane kurenki,kada ki nuna d'ari ko wani shakkata da kike idan kunne ya ji jiki ya tsira.

Bud'e murfin motar ya yi ya fito itama ta fito,inda ta tsaya gaida su Mallam Ibrahim Mai gadi da sauran ma'aikatan gidan,inda suka ta ya ta murna da Allah sanya alkhairi,sannnan suka gaida Muhdeen,nan suka nufi hanyar cikin gidan tana gaba Yana binta a baya saida suka k'arasa k'ofar falon sai ji kawai tayi ya rik'o hannunta cikin nasa da sauri ta kalle shi,ji kawai ya ja hannunta suka shiga falon bakinsa d'auke da sallama.

"Assalamu Alaikum"
Gaba d'ayansu suka amsa sallamar tare da kallonsu, Gwaggo,Dady, Mummy,da Mufida.

Kunya ce ta rufe Inteesar ta yi k'ok'arin zame hannunta cikin nasa Amma ina bai bata wannan damar ba, sunkuyar da kanta k'asa ta yi har suka k'araso wajensu,Gwaggo sai washe baki take tana cewa
"Lale marhaba da zuwa 'yar albarka,lale lale."
Zaunawa sukayi a saman center carpet kusa da Mufida, Mummy ma ta ji dad'in zuwansu sosai da yadda tagansu sai ta yi farin ciki matuk'ar jin dad'i ta nuna,har lokacin bai saki hannunta ba, Gwaggo ta ce,
"Dalla sake mani hannun yarinyar albarka mu gaisa,ka wani rirrik'eta kamar za'a k'wace maka ita."
Gwaggo ta janyo hannunta ta janyota gaban kujerar da take zaune ido ta zuba mata ma wasu 'yan mintuna kafin ta ce,
"Muhammadu haka aka aura maka yarinyar Nan?"
Kallon Gwaggon ya yi don ya san me zata ce,kauda kansa ya yi daga dubanta ya maida dubansa ga Dady.

"Dady ina wuni."
Cikin sakin fuska ya amsa masa da
"Lafiya kalau Muhammad ya iyalin?
Chapter 41 · 0% Book details