Sashe 38
Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ni kike fad'awa magana lallai kuwa kin samu sake,to bari kiji da kike maganar gidan kurkuku to nan tamkar gidan kurkuku ne a wajenki ki aje wannan a cikin zuciyarki."
Shiru tayi kanta a sunkuye idanunta sun cika tab da k'walla.
"Maza kije ki gama aikin da zakiyi,ba tare da tsayawa ba har sai kin gama,tukunnah ma d'akuna nawa kika gama dasu?"
Yanzun na gama da d'akuna hud'u saura hud'u,sannan na dawo kan falo da kitchens."
'Dan Jim tayi tana son ta yi masa magana tana tsoronsa ganin hakan yasa shi cewa.
"Maye kike yi haka kamar wata munafuka,idan zakiyi magana kiyi idan ba zaki yi na ki 'bace Mani da gani."
Cikin inda inda ta fara magana kanta a akasa.
"Nace amm dama Wai dama ummm"
Tsuki yayi tare da daka Mata tsawa
"Ke! dalla gafara can,idan zakiyi magana kiyi kin tsaya kina mun munafurci a nan."
Kanta a sunkuye k'irjinta sai dukan uku-uku yake ta fara magana.
"Dama cewa zanyi kullun zan dinga share da goge falo da kitchen safe da yamma kamar yadda ka ce nayi,sai kuma d'aki guda takwas da kace suma safe da yamma naga yanzun d'akuna uku ake amfani dasu sauran biyar d'in ba'a komai dasu,kuma suna kulle ba datti suke yi ba kuma kace suma safe da yamma shine na ce a dinga barinsu sai ranar juma'a sai na dinga bud'esu ina share su."
Gajeren murmushi ya yi
"Dani dake waye mai gidan?"
"Kai ne"
"Dani dake waye mai ikon fad'a aji?"
"Kai ne"
Dani dake wa ya ajiye wani?"
"Kinga kuwa magana ta ce sama da taki,kije ki gama duk aiyukan da na saka ki kafin kizo kiyi breakfast."
Daga nan ya nufi bedroom d'insa ya barta nan tsaye cike da tausayin kanta.
Haka Inteesar ta cigaba da rayuwa a cikin gidan Muhdeen cikin aikin wahala gashi dai ba aikin da gidan ko d'akunan ke buk'ata amma haka zai ce sai tayi shi,koda duka d'akunan da ba'a amfani dasu gasu fes ba datti ko kad'an amma daboda tsabar mugunta irin na Muhdeen sai ya ce ta goge su ga manyan falo biyu da kitchen guda biyu zata gyara dinning zata goge table da kujerun dinning area d'in,idan ta tashi tun asuba tayi sallah ta fara aikin gidannan tayi wanka ba ita zata samu sararin breakfast ba sai K'arfe biyu na rana.
Gwaggo ce zaune a falo tana sababi wai tunda aka Kai Inteesar gidan Muhdeen ba wanda ya je ya duba halin da suke ciki,ita fa zata je gidan ta zauna tayi sati d'aya,dama yau ne suka cika sati d'aya da tarewa.
Mufida ce ta fito daga kitchen d'auke da basket zata kaiwa su Inteesar abinci,kallonta Gwaggo tayi tare da cewa.
"Ke dama yaune zaki kai abincin k'arshe gidan Inteesar ko?"
Kai Mufida ta jinjina alamun eh
"Hakane Gwaggo daga yau shikenan"
"To idan kinje ki sanar da 'yar albarka cewa rana yata yau zanzo gidan sai nayi wata d'aya zan dawo."
Kallon mamaki Mummy ta bita da shi
"Har wata d'aya Gwaggo?"
"Eh haka nace ko akwai wanda Zai hanani ne?"
Girgiza Kai Mummy tayi
"A Gwaggo ba wanda zai hana ki ai."
"Ato idan ma akwai ne inji bayani."
Murmushi Mufuda tayi
"Yauwa Mummy na mance ban fad'a maki ban tambaye ki ba, Inteesar ta ce tabar wayarta a gidan nan a d'akin Yaya na duba ban gani ba."
Dafe goshi Mummy tayi tare da cewa yauwa namanta ne wlh yana d'akina,tun ranar da suka tafi washe gari na ganshi na d'auka tare da kashe wayan gaba d'aya,ki duba cikin side drawer na ki d'auka ki kai mata."
Ajiye basket d'in tayi tare da nufar d'akin Mummy ba jimawa ta fito da wayar a hannunta,sallama tayi masu ta nufi k'ofar fita,inda Gwaggo ta jaddada mata cewa ta shaidawa Muhdeen zata zo ranar juma'a.
Inteesar na kwance a saman bed d'inta tana barcin wahala,don gaba d'aya a gajiye take Don aikin da take yi yayi mata yawa,jikinta ma ciwo yake mata, ga hawayen da ya bushe a kumatunta da dukkan alamu kuka tayi har barci ya d'auketa.
Lokacin da Direban Mummy ya shigo gidan tare da Mufida lokacin ne kuma Muhdeen ya fito daga cikin gidan,sanye yake da farar shadda tsadadda da ba'kar hula a kansa sai bak'in takalmi da ya sakaba k'aramin kyau yayi ba,kwarjininsa ya k'ara bayyana Ishaq Direbansa ne ke bud'e masa murfin gaban motar, ganin Mufida yasa ya dakata ido ya zuba mata a tare suka sakarwa juna murmushi.
"My lovely bros barka da rana"
Fad'awa jikinsa tayi tare da cewa
"Kayi kyau sosai,ina lovely friend tana ciki"
"My lovely sis tana ciki"
"Okya me take yi?"
Ta'be baki yayi ya ce,
"Ki shiga ki gani mana,ni masallaci zanje sauri nake lokaci yayi."
"Okay ayi juma'a lafiya,ki gaida mutanen gidan."
"A'a Yaya ai wannan karon yini zanyi sai dare zan tafi."
d'an jim yayi yana nazari kafin ya ce,
"Ba Zaki koma gida ki taya Mummy aiki ba?"
"Na fad'a masu sai dare zan dawo,sannan ma Gwaggo ta ce na sanar da ku cewa next week zata zo sai ta yi 1 month sannan zata tafi."
Sai da Muhdeen ya d'an razana da jin zancen zuwan Gwaggo,Amma sai ya dake ya ce,
"To me zaisa tazo ta yi har wata d'aya a nan?ina laifin ta yini ta koma?"
Murmushi Mufida ta yi
"To ina laifi Dan tazo ta yi wata d'aya?kar ka mance cewa Gwaggo na k'aunar Inteesar fiye da tunaninka,bata son 'bacin ranta ko kad'an,ina tunanin zuwanta bai rasa nasaba da k'aunar da take mata da kuma k'aunar da take maka,kasan duk cikin jikokinta ta fi sonka."
Jinjina Kai yayi tare da cewa
" shikenan ki shiga ciki."
Nufar cikin gidan tayi yayinda shi kuma ya shiga cikin motarsa,tunani yake idan Gwaggo tazo gidan nan akwai matsala babba.
Koda Mufida ta shiga ba kowa a falon,hakan yasa Kai tsaye ta nufi d'akin Inteesar,sallama tayi sau uku bata ji an amsa ba hakan yasa ta tura k'ofar d'akin ta shiga,kwance ta same ta ta k'udundune waje guda alamun a takure take,ga hawayen da suka biye fuskarta sun bushe,idonta ma a kumbure alamar ta ci kuka,ido Mufida ta zuba mata ganin yadda ta d'an rame gashi tana barcin amma bata daina ajiyar zuciya ba, hannunta takai ta ta'ba gefen fuskarta a firgice Inteesar ta farka tana zare ido,ganin Mufida ce bata san lokacin da hawaye suka cika mata ido ba yayinda Mufida ta rungumeta.
Daga alk'amin
Zainab Andullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
Don k'arin bayani
09065327995
Love u oll
Comment and shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga.
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi ga kowa ba,idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba,arashi ne Mai kashe auren wawa.
*SADAUKARWA*
Wannan shafin sadaukarwa ce ga duk matar da ta fuskanci k'alubalen aure da uk'ubarsa ta kuma jure,hak'ika ba wata damuwa da zata d'ore har abada komai loaci ne wata rana sai labari.
*BISIMILLAHI RAHMANI RAHEEM*
Page3
Ido Mufida ta zuba mata ganin yadda ta d'an rame gashi tana barcin amma bata daina ajiyar zuciya ba, hannunta takai ta gefen fuskarta a firgice Inteesar ta farka tana zare ido, ganin Mufida ce bata san lokacin da hawaye suka cika mata ido ba yayin da Mufida ta rungumeta.
"Inteesar lafiya kuwa? me ya ke faruwa dake ne?"
Sunkuyar da kanta tayi tare da goge k'wallan da suka cika mata ido.
"Bakomai Mufida me kika gani?"
"Gani nayi duk kinbi kin rame daga ganinki baki cikin jin dad'i."
"Hasashenki ne haka,amma nikam ba abunda ke damuna."
Girgiza kai Mufida tayi cikin rashin yarda da zancenta ta ce,
"Kardai ace har kun fara samun sa'bani da Yaya tun yanzun,ai yakamata ne ace kuna cin amarci ba Wai daga aure an fara samun sa'bani ba,duk da ance zaman aure 'dan hak'uri ne amma yayi wuri da yawa."
"Karki damu Mufida ba komai ba wani sa'anin da muka samu,haka zaman namu yake tun fil'azal."
Da mamaki Mufida ke kallonta.
"Ban gane be Inteesar cewa fa kika yi haka zaman naku yake tun fil'azal."
Murmushin yak'e Inteesar tayi
"Ba haka nake nufi ba,ina nufin haka zaman aure yake tun fil'azal,wato d'an hak'uri ne haka abun yake a ko ina."
Jinjina Kai Mufida tayi
"To wai shin ma me ya had'aku kece mai laifi ko shi?"
Ganin yanayin Inteesar ya d'an canza yasa Mufida yin murmushi tare da dafa kafad'arta.
"Sorry k'awata mubar maganar."
Zama suka yi dab da juna ido Mufida ta zuba mata tana kallonta,kuma tana nazari a cikin zuciyarta,ita dai a iya saninta duk yarinyar da tayi aure sai taga ta canza ta k'ara kyawu da shek'i har k'iba yarinya takan k'ara,idan kuma ba mai kikin k'iba bace sai ta d'an murmure,Amma ita Kam Inteesar sai ramewa tayi gaba d'aya ta fita hayyacinta,amma sai ta bar hakan akan cewa kila dan Inteesar bata son Muhdeen ne auren had'i akayi masu,hakan yasa bata kwantar da hankalinta ba,iska mai d'umi ta furzar daga cikin bakinta,kafin ta fara magana.
"Nasan bakya son Yayana aka aura maki shi,dan Allah kiyi hak'uri ki kar'beshi a matsayin mijinki,ki cire damuwar da take ranki,bakiga shima ya d'auki k'addararsa ba ya rungume ki a matsayin matarsa ba?
Wallahi ya burgeni yadda naga yana nuna damuwarsa akanki,ranar washe garin ranar aurenku da nazo kawo maki breakfast kin tuna yadda yadda dinga ji dake?Wai kada na wahalar masa dake nabi a hankali ni a tunani na fa da naji ya ce haka na d'auka ko a daren farkon kun kashe arna ne kin wahala yasa naji ya ce haka."
Ta k'arasa maganar cikin sigar tsokana, Inteesar bata ce mata komai ba tana da ta sauraronta,inda Mufida ta cigaba da cewa.
Shiru tayi kanta a sunkuye idanunta sun cika tab da k'walla.
"Maza kije ki gama aikin da zakiyi,ba tare da tsayawa ba har sai kin gama,tukunnah ma d'akuna nawa kika gama dasu?"
Yanzun na gama da d'akuna hud'u saura hud'u,sannan na dawo kan falo da kitchens."
'Dan Jim tayi tana son ta yi masa magana tana tsoronsa ganin hakan yasa shi cewa.
"Maye kike yi haka kamar wata munafuka,idan zakiyi magana kiyi idan ba zaki yi na ki 'bace Mani da gani."
Cikin inda inda ta fara magana kanta a akasa.
"Nace amm dama Wai dama ummm"
Tsuki yayi tare da daka Mata tsawa
"Ke! dalla gafara can,idan zakiyi magana kiyi kin tsaya kina mun munafurci a nan."
Kanta a sunkuye k'irjinta sai dukan uku-uku yake ta fara magana.
"Dama cewa zanyi kullun zan dinga share da goge falo da kitchen safe da yamma kamar yadda ka ce nayi,sai kuma d'aki guda takwas da kace suma safe da yamma naga yanzun d'akuna uku ake amfani dasu sauran biyar d'in ba'a komai dasu,kuma suna kulle ba datti suke yi ba kuma kace suma safe da yamma shine na ce a dinga barinsu sai ranar juma'a sai na dinga bud'esu ina share su."
Gajeren murmushi ya yi
"Dani dake waye mai gidan?"
"Kai ne"
"Dani dake waye mai ikon fad'a aji?"
"Kai ne"
Dani dake wa ya ajiye wani?"
"Kinga kuwa magana ta ce sama da taki,kije ki gama duk aiyukan da na saka ki kafin kizo kiyi breakfast."
Daga nan ya nufi bedroom d'insa ya barta nan tsaye cike da tausayin kanta.
Haka Inteesar ta cigaba da rayuwa a cikin gidan Muhdeen cikin aikin wahala gashi dai ba aikin da gidan ko d'akunan ke buk'ata amma haka zai ce sai tayi shi,koda duka d'akunan da ba'a amfani dasu gasu fes ba datti ko kad'an amma daboda tsabar mugunta irin na Muhdeen sai ya ce ta goge su ga manyan falo biyu da kitchen guda biyu zata gyara dinning zata goge table da kujerun dinning area d'in,idan ta tashi tun asuba tayi sallah ta fara aikin gidannan tayi wanka ba ita zata samu sararin breakfast ba sai K'arfe biyu na rana.
Gwaggo ce zaune a falo tana sababi wai tunda aka Kai Inteesar gidan Muhdeen ba wanda ya je ya duba halin da suke ciki,ita fa zata je gidan ta zauna tayi sati d'aya,dama yau ne suka cika sati d'aya da tarewa.
Mufida ce ta fito daga kitchen d'auke da basket zata kaiwa su Inteesar abinci,kallonta Gwaggo tayi tare da cewa.
"Ke dama yaune zaki kai abincin k'arshe gidan Inteesar ko?"
Kai Mufida ta jinjina alamun eh
"Hakane Gwaggo daga yau shikenan"
"To idan kinje ki sanar da 'yar albarka cewa rana yata yau zanzo gidan sai nayi wata d'aya zan dawo."
Kallon mamaki Mummy ta bita da shi
"Har wata d'aya Gwaggo?"
"Eh haka nace ko akwai wanda Zai hanani ne?"
Girgiza Kai Mummy tayi
"A Gwaggo ba wanda zai hana ki ai."
"Ato idan ma akwai ne inji bayani."
Murmushi Mufuda tayi
"Yauwa Mummy na mance ban fad'a maki ban tambaye ki ba, Inteesar ta ce tabar wayarta a gidan nan a d'akin Yaya na duba ban gani ba."
Dafe goshi Mummy tayi tare da cewa yauwa namanta ne wlh yana d'akina,tun ranar da suka tafi washe gari na ganshi na d'auka tare da kashe wayan gaba d'aya,ki duba cikin side drawer na ki d'auka ki kai mata."
Ajiye basket d'in tayi tare da nufar d'akin Mummy ba jimawa ta fito da wayar a hannunta,sallama tayi masu ta nufi k'ofar fita,inda Gwaggo ta jaddada mata cewa ta shaidawa Muhdeen zata zo ranar juma'a.
Inteesar na kwance a saman bed d'inta tana barcin wahala,don gaba d'aya a gajiye take Don aikin da take yi yayi mata yawa,jikinta ma ciwo yake mata, ga hawayen da ya bushe a kumatunta da dukkan alamu kuka tayi har barci ya d'auketa.
Lokacin da Direban Mummy ya shigo gidan tare da Mufida lokacin ne kuma Muhdeen ya fito daga cikin gidan,sanye yake da farar shadda tsadadda da ba'kar hula a kansa sai bak'in takalmi da ya sakaba k'aramin kyau yayi ba,kwarjininsa ya k'ara bayyana Ishaq Direbansa ne ke bud'e masa murfin gaban motar, ganin Mufida yasa ya dakata ido ya zuba mata a tare suka sakarwa juna murmushi.
"My lovely bros barka da rana"
Fad'awa jikinsa tayi tare da cewa
"Kayi kyau sosai,ina lovely friend tana ciki"
"My lovely sis tana ciki"
"Okya me take yi?"
Ta'be baki yayi ya ce,
"Ki shiga ki gani mana,ni masallaci zanje sauri nake lokaci yayi."
"Okay ayi juma'a lafiya,ki gaida mutanen gidan."
"A'a Yaya ai wannan karon yini zanyi sai dare zan tafi."
d'an jim yayi yana nazari kafin ya ce,
"Ba Zaki koma gida ki taya Mummy aiki ba?"
"Na fad'a masu sai dare zan dawo,sannan ma Gwaggo ta ce na sanar da ku cewa next week zata zo sai ta yi 1 month sannan zata tafi."
Sai da Muhdeen ya d'an razana da jin zancen zuwan Gwaggo,Amma sai ya dake ya ce,
"To me zaisa tazo ta yi har wata d'aya a nan?ina laifin ta yini ta koma?"
Murmushi Mufida ta yi
"To ina laifi Dan tazo ta yi wata d'aya?kar ka mance cewa Gwaggo na k'aunar Inteesar fiye da tunaninka,bata son 'bacin ranta ko kad'an,ina tunanin zuwanta bai rasa nasaba da k'aunar da take mata da kuma k'aunar da take maka,kasan duk cikin jikokinta ta fi sonka."
Jinjina Kai yayi tare da cewa
" shikenan ki shiga ciki."
Nufar cikin gidan tayi yayinda shi kuma ya shiga cikin motarsa,tunani yake idan Gwaggo tazo gidan nan akwai matsala babba.
Koda Mufida ta shiga ba kowa a falon,hakan yasa Kai tsaye ta nufi d'akin Inteesar,sallama tayi sau uku bata ji an amsa ba hakan yasa ta tura k'ofar d'akin ta shiga,kwance ta same ta ta k'udundune waje guda alamun a takure take,ga hawayen da suka biye fuskarta sun bushe,idonta ma a kumbure alamar ta ci kuka,ido Mufida ta zuba mata ganin yadda ta d'an rame gashi tana barcin amma bata daina ajiyar zuciya ba, hannunta takai ta ta'ba gefen fuskarta a firgice Inteesar ta farka tana zare ido,ganin Mufida ce bata san lokacin da hawaye suka cika mata ido ba yayinda Mufida ta rungumeta.
Daga alk'amin
Zainab Andullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
Don k'arin bayani
09065327995
Love u oll
Comment and shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga.
Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi ga kowa ba,idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba,arashi ne Mai kashe auren wawa.
*SADAUKARWA*
Wannan shafin sadaukarwa ce ga duk matar da ta fuskanci k'alubalen aure da uk'ubarsa ta kuma jure,hak'ika ba wata damuwa da zata d'ore har abada komai loaci ne wata rana sai labari.
*BISIMILLAHI RAHMANI RAHEEM*
Page3
Ido Mufida ta zuba mata ganin yadda ta d'an rame gashi tana barcin amma bata daina ajiyar zuciya ba, hannunta takai ta gefen fuskarta a firgice Inteesar ta farka tana zare ido, ganin Mufida ce bata san lokacin da hawaye suka cika mata ido ba yayin da Mufida ta rungumeta.
"Inteesar lafiya kuwa? me ya ke faruwa dake ne?"
Sunkuyar da kanta tayi tare da goge k'wallan da suka cika mata ido.
"Bakomai Mufida me kika gani?"
"Gani nayi duk kinbi kin rame daga ganinki baki cikin jin dad'i."
"Hasashenki ne haka,amma nikam ba abunda ke damuna."
Girgiza kai Mufida tayi cikin rashin yarda da zancenta ta ce,
"Kardai ace har kun fara samun sa'bani da Yaya tun yanzun,ai yakamata ne ace kuna cin amarci ba Wai daga aure an fara samun sa'bani ba,duk da ance zaman aure 'dan hak'uri ne amma yayi wuri da yawa."
"Karki damu Mufida ba komai ba wani sa'anin da muka samu,haka zaman namu yake tun fil'azal."
Da mamaki Mufida ke kallonta.
"Ban gane be Inteesar cewa fa kika yi haka zaman naku yake tun fil'azal."
Murmushin yak'e Inteesar tayi
"Ba haka nake nufi ba,ina nufin haka zaman aure yake tun fil'azal,wato d'an hak'uri ne haka abun yake a ko ina."
Jinjina Kai Mufida tayi
"To wai shin ma me ya had'aku kece mai laifi ko shi?"
Ganin yanayin Inteesar ya d'an canza yasa Mufida yin murmushi tare da dafa kafad'arta.
"Sorry k'awata mubar maganar."
Zama suka yi dab da juna ido Mufida ta zuba mata tana kallonta,kuma tana nazari a cikin zuciyarta,ita dai a iya saninta duk yarinyar da tayi aure sai taga ta canza ta k'ara kyawu da shek'i har k'iba yarinya takan k'ara,idan kuma ba mai kikin k'iba bace sai ta d'an murmure,Amma ita Kam Inteesar sai ramewa tayi gaba d'aya ta fita hayyacinta,amma sai ta bar hakan akan cewa kila dan Inteesar bata son Muhdeen ne auren had'i akayi masu,hakan yasa bata kwantar da hankalinta ba,iska mai d'umi ta furzar daga cikin bakinta,kafin ta fara magana.
"Nasan bakya son Yayana aka aura maki shi,dan Allah kiyi hak'uri ki kar'beshi a matsayin mijinki,ki cire damuwar da take ranki,bakiga shima ya d'auki k'addararsa ba ya rungume ki a matsayin matarsa ba?
Wallahi ya burgeni yadda naga yana nuna damuwarsa akanki,ranar washe garin ranar aurenku da nazo kawo maki breakfast kin tuna yadda yadda dinga ji dake?Wai kada na wahalar masa dake nabi a hankali ni a tunani na fa da naji ya ce haka na d'auka ko a daren farkon kun kashe arna ne kin wahala yasa naji ya ce haka."
Ta k'arasa maganar cikin sigar tsokana, Inteesar bata ce mata komai ba tana da ta sauraronta,inda Mufida ta cigaba da cewa.