Sashe 31
Inteesar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan shigar ta d'akin ne,Abba ta kalli Unma ya ce,
"Dama kinsan munyi maganar kayan d'akinta akan zan siyar da dabbobi na a siya Mata kayan d'aki tunda auren ba shiyawa akayi ba."
"Eh na sani haka ne"
Cewar Umma dake goge hawayent,Abba ya d'aura da cewa
"Naje na samu kadintan nan dake bakin titi muna maganar kayan d'akin ne sai naga Alh.sani ,wato mahaifin Muhdeen ya tsaya da motarsa Yana horn,juyawa sai naganshi na k'arasa muka gaisa nan yake sanar Dani cewa kada muce zamu siye ki cokali domin su day kansu zasuyi Mata komai.Shi ya d'auki naiyin kayan d'aki komai zai siya matarsa kuma Hajiya Fatima zata siya Mata kayan kitchen,da na nuna cewa yayi yawa shine yake ce Mani Wai na manta cewa Inteesar 'yarsu ce?ko da ace ba d'ansu ne zai aure ta ba zasuyi Mata kayan d'aki ballantana tuwo na maina."
Cikin jindad'i Umma ta sanya masu albarka.
'Bangaren Muhdeen kuwa yana komawa gida Kai tsaye ya nufi d'akin Sumayya,yana Isa k'ofar d'akin kuwa ya samu K'ofar a wangale,Kai tsaye ya tura Kai cikin d'akin amma bata nan ga 'barnar da tayi kaca-kaca.Closet d'in ta ya duba kayayyakin da ta yayyaga kawai ke ciki, toilet ya nufa k'ofar toilet d'in ma a bud'e take,yana makin ina Sumayya ta shiga don dai bata shiga kitchen amma duk da haka ya kutsa Kai a cikin kitchen d'in ya duba bata nan.Gaba d'aya haka ya bincike gidan nan ko wane d'aki lungu da sak'o ba Sumayya ba alamarta,sai yayi dabarar tambayar Mai gadin ko yaga fitarta nan mai gadin ya sanar dashi cewa ta fita bayan fitarsa ba dad'ewa.Nan hankalinsa yayi masifar tashi har ya rufe mai gadin gidan da fad'a kamar zai rufe shi da duka shi dai hak'uri kawai yake bashi,don yasan bashida laifi amma yasa shi gaba da fad'a alhalin shi a matsayinsa na mai gadi ya isa ya hana matar gida fita?haka ya k'araci fad'arsa ya fice.
Gurin ajiye motocinsa ya nufa ya figi motar a guje Mai gadin ya wangale masa gate ya fice ya fice daga gidan.Parking yayi a gefen titi yana ta sak'e-sak'e ina Sumayya zata tafi?gashi Dad d'inta da Mum d'inta basa nan sun koma London,dama can suka fi zama ko sunzo Nigeria basa jimawa zasu koma.yanzun ta Yaya kuma ta Ina zai fara?
Kai tsaye gidan k'awarta Jumy ya nufa a k'ofar gidansu ya sameta tana zance da saurayinta a cikin mota,bayan yayi parking ne kasancewar Jumy ta hangi motarsa yasa ta fito,bayan sun gaisa ne ya tambayeta k'awar ta sanar dashi bata ga Sumayya ba ya sanar da ita cewa bata gida kuma wayoyinta duka basa shiga,daga Nan dai ya yi Mata sallama ya tafi,gidan Shila ya nufa nan ma bata nan k'arshe dai haka ya hak'ura ya nufi gidan Abokinsa Salisu,daga waje ya tsaya ya kira Salisu a waya ya sanar dashi cewaa yana gida ya shigo ciki.
Bayan ya shiga cikin gidan ne ya samu Salisu a fall da matarsa Saliha sai 'yarsu k'arama 'yar shekara d'aya mai suna Hidaya da sallama ya shigo falon.
"Assalamu Alaikum"
"Wa'alaika salam"
Salisu ya fad'a yana mik'ewa tsaye ya k'arasa wurin Muhdeen ya bashi hannu sukayi musabaha tare da janyo shi ya zauna kan kujera.
"Abokina da alama yau dai kayi 'batan hanya ne ko?"
Murmushi kawai Muhdeen yayi tare da cewa
"Bari kawai"
Saliha matar Salisu ne ta gaida Muhdeen
"Ina wuni ango?"
Murmushin yak'e yayi tare da cewa
"Lafiya lau Saliha"
"Ya amarya?da Safen nan muka gama zancen zuwa gidanka naga amarya."
Murmushin yak'e kawai yayi tare da d'aukar Hidaya Yana Mata wasa.
Saliha ce ta nufi kitchen take ta kawo masa abun ta'awa,duk d yunwar da yake ji baya tunanin zai iya kai want abu a bakinsa.ganin Saliha na zaune ne kum ga shi magariba ta kusa yasa ya mi'ke yayi Mata Sallama ya nufi k'ofar fita inda Salisu yabi bayansa suka fice.
A Harabar gidan suka tsaya Salisu ya zuba masa idanu ganin yadda yadda gaba d'aya ya canza lokaci guda.
"Lafiya kuwa?naga gaba d'aya ka sauya me ya faru ne?"
Ajiyar zuciya Muhdeen ya sauke,sannan ya bawa Salisu labarin duk abunda ya faru.A jiyar zuciya Salisu ya sauke.
"Lallai kana cikin yanzun abuda za'ayi shine mu bari muyani Ko Sumayya zata dawo idan har takai dare bata dawo ba zuwa gobe da sassafe sai mu san abunyi."
Nan dai suka cigaba tattaunawa kafin sukayi Sallama ya tafi.
Washe gari ne ya kama ranar da za'aje a had'o ma Inteesar kayan lefe,kuma a ranar ne za'a d'auko ta a kawo ta gidan su Mummy.Da misalin k'arfe goma na safe ne Aunty Abla k'anwar Mummy da kuma k'awar Mummy Hajiya Ameera suka zo don siyowa Inteesar kayan lefe.su uku suka tafi Mummy da Aunty Abla da Aunty Ameera ne suka tafi,aka bar Gwaggo da Mufida a gida.
'Bangaren Inteesar kuwa kwana sukayi ita da Ummanta tana tayi mata nasiha Inteesar tasha kuka kamar ba gobe har idanunta sun kumbura,ita dai bata san waye mijinta ba abunda ta sani kawai ance mata an aurar da ita, kuma an sanar da ita cewa yau zata koma gidan Mummy da zama kafin ranar juma'a akaita gidan mijinta.Bayan wannan bata san komai ba.Haka dai dai tayi ta Addu'a tana Kai kukanta ga Allah akan auren nan yasa ya zama alkhairi a rayuwarta.
Da misalin k'arfe biyu na rana Mummy da su Aunty Abla suka dawo nik'i -nik'i da akwatunan da kayyaki a ciki akwatunan guda takwas ne da kayan da duk ake had'awa a cikin lefe,komai yayi kyau masha Allah.Nan dai aka bajewa Gwaggo kayan tana dubawa tana Sanya alkhairi da Addu'a Allah yasa shekara Mai zuwa ta Muhdeen da Inteesar.
'Bangaren Muhdeen kuwa ya yi neman Sumayya har ya gaji,ya Kira layin wayarta bila adadin shida Salisu tun safe suke ta nemanta Amma ba Sumayya ba labarinta,duk inda yasan tana da alak'a da mutanen wajen sun tafi wajen amma basu sameta ba. a cikin kwana d'aya muhdeen yabi ya zabge ya fita hayyacinsa domin hankain Muhdeen yafi jirgin sama tashi.
Daga alk'amin
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
*DOMIN K'ARIN BAYANI*
09065327995
Love u oll
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga.
Wannan kagaggen labari ne, banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi ga kowa ba,idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba.Arashi ne mai kashe auren wawa.
Page3
A cikin kwana d'aya muhdeen yabi ya zabge ya fita hayyacinsa, domin hankalin Muhdeen yafi jirgin sama tashi.
A yammacin ranar ne Gwaggo da Aunty Abla da Hajiya Ameera suka je gidansu Inteesar dan d'auko ta.Umma ce da k'anwar ta Huraira sai k'awayenta su biyo da kuma mak'ota da suka shigo Umma ta sanar dasu,duk da ba taron biki akayi ba amma za'ayi taron biki ranar juma'a a gidan Mummy.Mama Huraira k'anwar Umma ce ta shirya Inteesar cikin atamfa riga da zani da Ummanta ta d'nika mata sai mayafi fari da aka yafa mata ta lullu'be fuskarta da shi,idan ka ganta sai ka tausaya Mata idanunta duk sun kumbara sunyi jazir hatta fuskarta ma duk tayi ja ta kumbura saboda tsabar kuka.Ita dai gata zata rabu da Abbanta da Ummanta,zata je can wani gida inda zata shirya sabuwar rayuwa gashi ita kanta ba'a fad'a mata waye mikinta ba kuma itama bata tambaya ba, tambayar da taketayiwa kanta shine,shin shima mijin bai santa ba kamar yadda itama bata sanshi ba?shin wace irin rayuwa zata yi?yanzun shikenan ta rabu da Ummanta da Abbanta kenan sai randa yazo gaishe su?
Kuka ne yaci k'arfinta dakyar mama Huraira ta rarrasheta tayi shiru ta dakatar da kukan da takeyi.Nasiha sukayi mata Mai ratsa jiki sannan aka ja hannunta don tafiya,nan fa ta coge ta ri'ke hannun Umma tana kuka dakyar aka 'ban'bare hannun Umma daga nata,hakan yasa Umma itama hawayen da ta rik'e suka samu nasarar zubowa.A haka tana kuka suka nufi hanyar fita inda Mama Huraira ta tsaya da ita zauren gidan wajen Abba,shima ya d'ora da nasa nasihar sai kuka Inteesar take yi,haka dai aka ja hannunta suka nufi hanyar fita, inda aka jera motoncin.Motoci guda uku ne aka shiga da Amarya d'aya inda Mama Huraira da k'awayen Ummin suka shiga mota d'a ma'kotansu ma d'aya,yayinda su Gwaggo da Aunty Abla ma suka shiga d'aya.duk da cewar unguwa d'aya ce basu da nisa minti kad'an suka isa gidan,bayan Mai gadi ya wangale masu gate ne suka shiga nan aka firfito Mama Huraira ce ta rungume Inteesar ta gefen kafad'arta suka shiga cikin gidan.
Part d'in Muhdeen da ya zauna kafin ya auri Sumayya nan aka ajiyeta,duk da cewar ba dad'ewa yayi da barin d'akin ba sati biyu kenan,ba wani k'ura sosai dama Mummy ta sanya Mufida ta gyara part d'in.Da sallama suka shiga falon ba kowa sai k'amshi ke tashi,har bedroom aka shiga da ita inda aka zaunar da ita bakin gado.kasncewar lokacin sallar magariba ne yasa sukayi Mata sallama akan cewa zasu dawo ranar juma'a,waro ranar da za'a kaita gidan mijinta.
Har yanzun Inteesar Bata san waye mijinta ba ta d'auka saboda shak'uwar da ke tsakaninta da 'yar gidan su Mummy yasa aka ce ta zauna nan gidan kafi akaita gidan mijinta.
Bayan kowa ya watse ne ita kad'ai ta ragae a d'akin,ido ta zubawa d'akin tana k'are masa kallo a zuciyarta tana cewa d'akin wannan mugun aka kawo ni,mutum sai mugunta da da bak'in hali a haka dai ta nufi toilet ta d'auro alwala tazo ta shimfid'a sallaya ta tada sallah.
"Dama kinsan munyi maganar kayan d'akinta akan zan siyar da dabbobi na a siya Mata kayan d'aki tunda auren ba shiyawa akayi ba."
"Eh na sani haka ne"
Cewar Umma dake goge hawayent,Abba ya d'aura da cewa
"Naje na samu kadintan nan dake bakin titi muna maganar kayan d'akin ne sai naga Alh.sani ,wato mahaifin Muhdeen ya tsaya da motarsa Yana horn,juyawa sai naganshi na k'arasa muka gaisa nan yake sanar Dani cewa kada muce zamu siye ki cokali domin su day kansu zasuyi Mata komai.Shi ya d'auki naiyin kayan d'aki komai zai siya matarsa kuma Hajiya Fatima zata siya Mata kayan kitchen,da na nuna cewa yayi yawa shine yake ce Mani Wai na manta cewa Inteesar 'yarsu ce?ko da ace ba d'ansu ne zai aure ta ba zasuyi Mata kayan d'aki ballantana tuwo na maina."
Cikin jindad'i Umma ta sanya masu albarka.
'Bangaren Muhdeen kuwa yana komawa gida Kai tsaye ya nufi d'akin Sumayya,yana Isa k'ofar d'akin kuwa ya samu K'ofar a wangale,Kai tsaye ya tura Kai cikin d'akin amma bata nan ga 'barnar da tayi kaca-kaca.Closet d'in ta ya duba kayayyakin da ta yayyaga kawai ke ciki, toilet ya nufa k'ofar toilet d'in ma a bud'e take,yana makin ina Sumayya ta shiga don dai bata shiga kitchen amma duk da haka ya kutsa Kai a cikin kitchen d'in ya duba bata nan.Gaba d'aya haka ya bincike gidan nan ko wane d'aki lungu da sak'o ba Sumayya ba alamarta,sai yayi dabarar tambayar Mai gadin ko yaga fitarta nan mai gadin ya sanar dashi cewa ta fita bayan fitarsa ba dad'ewa.Nan hankalinsa yayi masifar tashi har ya rufe mai gadin gidan da fad'a kamar zai rufe shi da duka shi dai hak'uri kawai yake bashi,don yasan bashida laifi amma yasa shi gaba da fad'a alhalin shi a matsayinsa na mai gadi ya isa ya hana matar gida fita?haka ya k'araci fad'arsa ya fice.
Gurin ajiye motocinsa ya nufa ya figi motar a guje Mai gadin ya wangale masa gate ya fice ya fice daga gidan.Parking yayi a gefen titi yana ta sak'e-sak'e ina Sumayya zata tafi?gashi Dad d'inta da Mum d'inta basa nan sun koma London,dama can suka fi zama ko sunzo Nigeria basa jimawa zasu koma.yanzun ta Yaya kuma ta Ina zai fara?
Kai tsaye gidan k'awarta Jumy ya nufa a k'ofar gidansu ya sameta tana zance da saurayinta a cikin mota,bayan yayi parking ne kasancewar Jumy ta hangi motarsa yasa ta fito,bayan sun gaisa ne ya tambayeta k'awar ta sanar dashi bata ga Sumayya ba ya sanar da ita cewa bata gida kuma wayoyinta duka basa shiga,daga Nan dai ya yi Mata sallama ya tafi,gidan Shila ya nufa nan ma bata nan k'arshe dai haka ya hak'ura ya nufi gidan Abokinsa Salisu,daga waje ya tsaya ya kira Salisu a waya ya sanar dashi cewaa yana gida ya shigo ciki.
Bayan ya shiga cikin gidan ne ya samu Salisu a fall da matarsa Saliha sai 'yarsu k'arama 'yar shekara d'aya mai suna Hidaya da sallama ya shigo falon.
"Assalamu Alaikum"
"Wa'alaika salam"
Salisu ya fad'a yana mik'ewa tsaye ya k'arasa wurin Muhdeen ya bashi hannu sukayi musabaha tare da janyo shi ya zauna kan kujera.
"Abokina da alama yau dai kayi 'batan hanya ne ko?"
Murmushi kawai Muhdeen yayi tare da cewa
"Bari kawai"
Saliha matar Salisu ne ta gaida Muhdeen
"Ina wuni ango?"
Murmushin yak'e yayi tare da cewa
"Lafiya lau Saliha"
"Ya amarya?da Safen nan muka gama zancen zuwa gidanka naga amarya."
Murmushin yak'e kawai yayi tare da d'aukar Hidaya Yana Mata wasa.
Saliha ce ta nufi kitchen take ta kawo masa abun ta'awa,duk d yunwar da yake ji baya tunanin zai iya kai want abu a bakinsa.ganin Saliha na zaune ne kum ga shi magariba ta kusa yasa ya mi'ke yayi Mata Sallama ya nufi k'ofar fita inda Salisu yabi bayansa suka fice.
A Harabar gidan suka tsaya Salisu ya zuba masa idanu ganin yadda yadda gaba d'aya ya canza lokaci guda.
"Lafiya kuwa?naga gaba d'aya ka sauya me ya faru ne?"
Ajiyar zuciya Muhdeen ya sauke,sannan ya bawa Salisu labarin duk abunda ya faru.A jiyar zuciya Salisu ya sauke.
"Lallai kana cikin yanzun abuda za'ayi shine mu bari muyani Ko Sumayya zata dawo idan har takai dare bata dawo ba zuwa gobe da sassafe sai mu san abunyi."
Nan dai suka cigaba tattaunawa kafin sukayi Sallama ya tafi.
Washe gari ne ya kama ranar da za'aje a had'o ma Inteesar kayan lefe,kuma a ranar ne za'a d'auko ta a kawo ta gidan su Mummy.Da misalin k'arfe goma na safe ne Aunty Abla k'anwar Mummy da kuma k'awar Mummy Hajiya Ameera suka zo don siyowa Inteesar kayan lefe.su uku suka tafi Mummy da Aunty Abla da Aunty Ameera ne suka tafi,aka bar Gwaggo da Mufida a gida.
'Bangaren Inteesar kuwa kwana sukayi ita da Ummanta tana tayi mata nasiha Inteesar tasha kuka kamar ba gobe har idanunta sun kumbura,ita dai bata san waye mijinta ba abunda ta sani kawai ance mata an aurar da ita, kuma an sanar da ita cewa yau zata koma gidan Mummy da zama kafin ranar juma'a akaita gidan mijinta.Bayan wannan bata san komai ba.Haka dai dai tayi ta Addu'a tana Kai kukanta ga Allah akan auren nan yasa ya zama alkhairi a rayuwarta.
Da misalin k'arfe biyu na rana Mummy da su Aunty Abla suka dawo nik'i -nik'i da akwatunan da kayyaki a ciki akwatunan guda takwas ne da kayan da duk ake had'awa a cikin lefe,komai yayi kyau masha Allah.Nan dai aka bajewa Gwaggo kayan tana dubawa tana Sanya alkhairi da Addu'a Allah yasa shekara Mai zuwa ta Muhdeen da Inteesar.
'Bangaren Muhdeen kuwa ya yi neman Sumayya har ya gaji,ya Kira layin wayarta bila adadin shida Salisu tun safe suke ta nemanta Amma ba Sumayya ba labarinta,duk inda yasan tana da alak'a da mutanen wajen sun tafi wajen amma basu sameta ba. a cikin kwana d'aya muhdeen yabi ya zabge ya fita hayyacinsa domin hankain Muhdeen yafi jirgin sama tashi.
Daga alk'amin
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
*DOMIN K'ARIN BAYANI*
09065327995
Love u oll
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by
Zainab Abdullahi
(Maman Ihsan)
ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad
akarwa, ilimantarwa da kuma nishad
antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad
ai ke maganin k
ishi_
*Alk
alaminmu
yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga.
Wannan kagaggen labari ne, banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi ga kowa ba,idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba.Arashi ne mai kashe auren wawa.
Page3
A cikin kwana d'aya muhdeen yabi ya zabge ya fita hayyacinsa, domin hankalin Muhdeen yafi jirgin sama tashi.
A yammacin ranar ne Gwaggo da Aunty Abla da Hajiya Ameera suka je gidansu Inteesar dan d'auko ta.Umma ce da k'anwar ta Huraira sai k'awayenta su biyo da kuma mak'ota da suka shigo Umma ta sanar dasu,duk da ba taron biki akayi ba amma za'ayi taron biki ranar juma'a a gidan Mummy.Mama Huraira k'anwar Umma ce ta shirya Inteesar cikin atamfa riga da zani da Ummanta ta d'nika mata sai mayafi fari da aka yafa mata ta lullu'be fuskarta da shi,idan ka ganta sai ka tausaya Mata idanunta duk sun kumbara sunyi jazir hatta fuskarta ma duk tayi ja ta kumbura saboda tsabar kuka.Ita dai gata zata rabu da Abbanta da Ummanta,zata je can wani gida inda zata shirya sabuwar rayuwa gashi ita kanta ba'a fad'a mata waye mikinta ba kuma itama bata tambaya ba, tambayar da taketayiwa kanta shine,shin shima mijin bai santa ba kamar yadda itama bata sanshi ba?shin wace irin rayuwa zata yi?yanzun shikenan ta rabu da Ummanta da Abbanta kenan sai randa yazo gaishe su?
Kuka ne yaci k'arfinta dakyar mama Huraira ta rarrasheta tayi shiru ta dakatar da kukan da takeyi.Nasiha sukayi mata Mai ratsa jiki sannan aka ja hannunta don tafiya,nan fa ta coge ta ri'ke hannun Umma tana kuka dakyar aka 'ban'bare hannun Umma daga nata,hakan yasa Umma itama hawayen da ta rik'e suka samu nasarar zubowa.A haka tana kuka suka nufi hanyar fita inda Mama Huraira ta tsaya da ita zauren gidan wajen Abba,shima ya d'ora da nasa nasihar sai kuka Inteesar take yi,haka dai aka ja hannunta suka nufi hanyar fita, inda aka jera motoncin.Motoci guda uku ne aka shiga da Amarya d'aya inda Mama Huraira da k'awayen Ummin suka shiga mota d'a ma'kotansu ma d'aya,yayinda su Gwaggo da Aunty Abla ma suka shiga d'aya.duk da cewar unguwa d'aya ce basu da nisa minti kad'an suka isa gidan,bayan Mai gadi ya wangale masu gate ne suka shiga nan aka firfito Mama Huraira ce ta rungume Inteesar ta gefen kafad'arta suka shiga cikin gidan.
Part d'in Muhdeen da ya zauna kafin ya auri Sumayya nan aka ajiyeta,duk da cewar ba dad'ewa yayi da barin d'akin ba sati biyu kenan,ba wani k'ura sosai dama Mummy ta sanya Mufida ta gyara part d'in.Da sallama suka shiga falon ba kowa sai k'amshi ke tashi,har bedroom aka shiga da ita inda aka zaunar da ita bakin gado.kasncewar lokacin sallar magariba ne yasa sukayi Mata sallama akan cewa zasu dawo ranar juma'a,waro ranar da za'a kaita gidan mijinta.
Har yanzun Inteesar Bata san waye mijinta ba ta d'auka saboda shak'uwar da ke tsakaninta da 'yar gidan su Mummy yasa aka ce ta zauna nan gidan kafi akaita gidan mijinta.
Bayan kowa ya watse ne ita kad'ai ta ragae a d'akin,ido ta zubawa d'akin tana k'are masa kallo a zuciyarta tana cewa d'akin wannan mugun aka kawo ni,mutum sai mugunta da da bak'in hali a haka dai ta nufi toilet ta d'auro alwala tazo ta shimfid'a sallaya ta tada sallah.