Sashe 65
Turken Gida Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yallaɓai ya maida ni gida ni da Baby da Saude saboda su Anty Maimuna duk sun zo, har a cikin zuciyata na yi murna da ba abin da ya faru. Da wani abu ya faru ai da na shiga uku ashe na gudu ban tsira ba ne, kwanan Gimbiya uku a asibiti aka sallameta nan ta ke aka wuce da ita wajen Nene. Ban yi magana ba amma a raina na ce gwara haka can ɗin in wani abu ya faru sai su ce uwar su ce sila. Ni dai na ga tun ana gobe za a sallami Gimbiya da na je asibitin duk ba wacce ta yi min wata mgana amma na ga suna yi mini wani kallo har da Halima da ita kanta Gimbiyar ta sauya min sai ban kawo komai a raina ba shi ya sa ana sallamota na shirya washegari da safe na je Gwammaja daman mun yi da su Hauwa suma za su je duba ta sai na ce kawai mu haɗu a can. Musamman na yi dambun shinkafa da zogale sanin Nene na so ya sa na diɓa na tafin mata da shi na je Ɗakin Nene cike da su Anty Bahijja kaf da ƴaƴanta Anty Maimuna Halima, Su Suwaiba ina gidan Hauwa ta ƙariso daman na iske Munnira.
Na shiga har ɗaki na gaida Nene na kuma kai mata Dambun da na zo da shi, ta karɓa ta yi godiya
Bayan na fito na shiga ɗakin da Gimbiya ke ciki, su Anty Bahijja na ciki da na yi sallama ba wacce ta amsa har ita Gimbiya sannan suna ganina suka yi shuru. Na gaishe su suka amsa min a daƙile, Gimbiya ina cewa ya jiki ko kallona ba ta yi ba a laɓanta ta amsa da.
"Da sauƙi."
"Allah ya ƙara lafiya."
"Amin."
Ta faɗa kamar ba ta so, sai jikina ya yi sanyi wulaƙanci ƙiri ƙiri suka yi min a ciki sai na fito na koma falo wajen su Hauwa ina ƙirkiran mirmishi ban nuna musu ma wani abu ya faru ba. muna zaune Anty Bahijja ta zo ta wuce ɗakin Nene ba jimawa sai ga shi ta fito da kulan Dambun da na kawo ma Nene muna ji Nene na ƙwala mata kira har sai da ta fito da kanta.
"Bahijja magana fa na ke yi miki."
"Nene ba za ki ci dambun nan ba fa Kawai ke ma ta saka miki mgani ta kashe mana ke kamar yadda ta so kashe abin da ke cikin Gimbiya. Tun da daman ita É—in dangin asiri ne an saba shige shige."
"Bahijja ba na ce ki bar mganar nan ba ne?
Har ta na wani jijiyan wuya wajen faɗin" Nene to sai a ƙyaleta bayan kowa ya san gaskiya?
Ta faɗa ta na hararana ni fa da farko ban ma gane in da ta dosa ba ne sai da na ga ta na kallona sannan na fara dawo da abin da ya faru tun shigowata gidan nan, ban san lokacin da na miƙe ba haka ma su Hauwa saboda sai yanzu na gane in da Anty Bahijja ta dosa.
"Ban ga ne ba? A kan wa kike mgana?
Na faɗa ina kallonta sai kawai a gabana ta ɗaga kulan dambun ta sake shi ta a ƙasa murfin ya buɗe dambun ya Zube ƙasa idanuwana har sun ƙanƙance saboda ɓacin rai.
"Me kenan kika yi?
"Abin da idanuwanki suka gane miki."
Ta faɗa ta na kallona ai sai na ƙarisa gabanta Hauwa na riƙe min hannu na fizge ita kuma Munnira na faɗin"Subhanallah zubar da abinci me ya yi zafi Anty Bahijja?
Sai gabaɗaya har su Gimbiyar suka fffito Nene kuma faɗi ta ke yi" Sadiya ƙyaleta kin ji."
"Ke dai za ki faÉ—a min abin da kike nufi da zubar da abinci da na kawo. Sannan da mganganun da kike a kaina?waye zai kashe muku uwa? Sannan waye ya so kashe abin da ke cikin gimbiya? Sannan waye dangin asiri? Kar dai ki ce da ni ki ke ?
Na faɗa ina kallonta domin har duhu duhu na fara gani, ni za a yi ma tijara a bainar na si, ni za a ƙulla ma sheri a ci mutumcina da mutumcin dangina
"Na ce ina fatan ba da ni kike ba ko?
"Da ke ake ko kina da mgana ne?
Sai kawai na ƙura mata ido ina kallonta.
"Kika ce da ni kike? Ni ce mai yin asirin?
"Ke ce mana. Kin so zubar da cikin Gimbiya Allah ya fiki. Ai duk mun san komai. Mun san cewa Yayar mamanki asiri ta yi ma abokiyar zamanta kaikayi ya koma kan masheƙiya ta mutu cikin hauka, kowa ya san wannan labarin saboda asirinta ya tonu."
Mamaki ya hana ni mgana, idanuwana sun kawo ruwa cikin rawam murya na ce" A ina kika ji wannan labarin?
"A bakin da ba zai yi min ƙarya ba. Ma'u ce ta faɗa min ko za ta yi miki ƙarya ne?
"Ma'u."
Na maaimata sunan a saman laɓɓana.
Na kasa ma yin wani motai bakina na rawa na kasa mgana jikina ba in da baya rawa zuciyata ina jin kamar za ta faso ƙirjina ta fito saboda halin da na ke ciki.
"Ma'u fa?
Ma'u ƴar uwata da muka taso tare ita ce za ta zo dangin mijina ta yi min ƙazafi. Daman na san wannan bini binin na ta ba na lafiya ba ne. Sai ta ga na tozarta sannan hankalinta zai kwanta. Lalle ko akwai yaƙin duniya na uku tsakanina da Ma'u da duk wanda ke da hannu wajen yi min wannan mummunan ƙazafin.
*Janafty*
*TKG017*
"Bahijja kina mata wani sanyi sanyi ke Sadiya har mganin asirin suke kawo miki har gida. Gimbiya ta gan ki lokacin da ƙanwar mamanki ta kawo miki su har gida ko shima za ki ƙarya ta ne?
Kalaman Anty Maimuna suka buga min kai kamar an dake ni da ƙarfe sai da na ji kaina ya yi dum na ɗago ina kallonta ba bakina ba har idanuwana suna rawa ne a lokacin.
"Haba Anty Maimuna me ya sa haka?
Hauwa ta faɗa kamar ta yi kuka Munnira kuma sai ta hau tafa hannu ta na faɗin" Yanzu me Sadiya ta yi muku da za ku yi mata wannan mummunan ƙazafin?
Ni kuma Gimbiya na ke kallo cikin mamakinta ina so na tabbatar da gaske ita ce ta faɗi ta ga ƙanwar Mamana ta kawo min asiri? sai na ga ta kauda kaita alamun kenan da gaske ne. Sai kawai na ji na fara jijjiga ni kaɗai saboda ɓacin rai ranar da Inna Mariya ta zo kawo min mganin na dawo min a cikin idanuwa. Oh shi ya sa daman ta ce min ta ga ta na ta kallon mu? Kenan zargin ta kawo min asiri ta ke yi min tun da gashi har ta kawo labarin gaba. Kuma tunda ina shige shige kuma ina baƙin ciki da cikin da ke jikinta tun da ni ban taɓa haihuwa ba shi ya sa na ba ta mgani ta ci a abinci cikinta ya zube sai Allah ya fini asirina ya tonu cikin bai zube ba. Shi ne aka zauna aka tattauna gwara a turke ni a ci min mutumci, duk a lokaci ɗaya na gama hango abin da ya faru shi ya sa ban san na yi wata dariya ba sai da na ga ina yin ta cikin mamaki suke kallona Anty Bahijja na nuna da yatsa na ina faɗin.
"Ba a haifi wani É—a namijin da zan kauce ma Allah saboda shi ba Bahijja"
"Kuma kika kaucen?
"Tunda kin yarda na kauce kuma na yi asirin tun da kin ce ni yar na gada ce, sannan ma ai an ce an ga tabbaci me kike jira Bahijja?
Na kira sunanta cikin tsawa kafin ta samu zarafin magana na zare mayafin jikina na É—aure a kuguna ina faÉ—in
"Na ce tunda kin samu tabbaci me kike jira? Ba sai ki É—au mataki ba Bahijja?
Na faɗa ina nuna ta da yatsa, Itama ta so min tana faɗin zan ko ga matakin da za ta ɗauka Hauwa da Munnira na rike ni ina fizgewa, ita ma Bahijja su Maimuna na riƙe ta Nene ma ta mgana ba wanda ya ji ta, Hayaniya ya sa har su Hajiya Iya da Maman farko sai da suka shigo lokacin Anty Bahijja na faɗin zan ga abin da zai faru.
"Ba abin da zan gani sai alheri me zan gani? Ya wuce ki saka ƙanin ki ya sake ni? To sai me? Kaina farau zawarci ke in ba ki saka shi ya yi min saki uku ba tabbas ke Bahijja ba ki haufu cikin uwarki da uban ki ba."
"Ke Sadiya ki yi shuru"
In ji Maman farko Suwaiba na ja na ita da su Hauwa ta na faÉ—in" Sadiya mu je mu je Sadiya."
"Ni kike zagi don uban ki Sadiya. Ni sa'ar ki ce?
"An zage ki ɗin ke uwata ce da ba za ki zagu ba? Har ni za ki yi ma kazafi na so zubar da ciki? To ni na zubar da cikin gimbiya na ci riban me? Ko haihuwa ce ban taɓa yi ba da za ta zame min baƙuwa? Amma ba laifin ki ba ne, laifin wacce ta faɗa miki ne. Amma ina so ki sani da ke da wacce ta faɗa miki na rantse da wanda raina ke hannun shi sai na yi ƙaran ku a wajen hukuma."
Daƙyar su Suwaiba suka fita da ni daga ɗakin Nene tana zagina ina zaginta. Itama ana riƙe ta tana cewa a sake ta, ta doke ni "Na ce ku sake ta mana ta zo ta ga in zan bugun mata ko wanda na ke aure bai isa ya doke ba ballantana ke banza a banza."
Itama ana riƙe ta tana fizgewa faɗi ta ke yi wai ai ba ƙarya aka yi min ba. Ina shige shige na wanke gaba na ba ma Tafida ya sha da ba ya ganin laifina, na shanye musu ɗan'uwa ko auran shi ma da Gimbiya Allah ne ya fi ƙarfina shi ya sa aka yi auren.
Na shiga har ɗaki na gaida Nene na kuma kai mata Dambun da na zo da shi, ta karɓa ta yi godiya
Bayan na fito na shiga ɗakin da Gimbiya ke ciki, su Anty Bahijja na ciki da na yi sallama ba wacce ta amsa har ita Gimbiya sannan suna ganina suka yi shuru. Na gaishe su suka amsa min a daƙile, Gimbiya ina cewa ya jiki ko kallona ba ta yi ba a laɓanta ta amsa da.
"Da sauƙi."
"Allah ya ƙara lafiya."
"Amin."
Ta faɗa kamar ba ta so, sai jikina ya yi sanyi wulaƙanci ƙiri ƙiri suka yi min a ciki sai na fito na koma falo wajen su Hauwa ina ƙirkiran mirmishi ban nuna musu ma wani abu ya faru ba. muna zaune Anty Bahijja ta zo ta wuce ɗakin Nene ba jimawa sai ga shi ta fito da kulan Dambun da na kawo ma Nene muna ji Nene na ƙwala mata kira har sai da ta fito da kanta.
"Bahijja magana fa na ke yi miki."
"Nene ba za ki ci dambun nan ba fa Kawai ke ma ta saka miki mgani ta kashe mana ke kamar yadda ta so kashe abin da ke cikin Gimbiya. Tun da daman ita É—in dangin asiri ne an saba shige shige."
"Bahijja ba na ce ki bar mganar nan ba ne?
Har ta na wani jijiyan wuya wajen faɗin" Nene to sai a ƙyaleta bayan kowa ya san gaskiya?
Ta faɗa ta na hararana ni fa da farko ban ma gane in da ta dosa ba ne sai da na ga ta na kallona sannan na fara dawo da abin da ya faru tun shigowata gidan nan, ban san lokacin da na miƙe ba haka ma su Hauwa saboda sai yanzu na gane in da Anty Bahijja ta dosa.
"Ban ga ne ba? A kan wa kike mgana?
Na faɗa ina kallonta sai kawai a gabana ta ɗaga kulan dambun ta sake shi ta a ƙasa murfin ya buɗe dambun ya Zube ƙasa idanuwana har sun ƙanƙance saboda ɓacin rai.
"Me kenan kika yi?
"Abin da idanuwanki suka gane miki."
Ta faɗa ta na kallona ai sai na ƙarisa gabanta Hauwa na riƙe min hannu na fizge ita kuma Munnira na faɗin"Subhanallah zubar da abinci me ya yi zafi Anty Bahijja?
Sai gabaɗaya har su Gimbiyar suka fffito Nene kuma faɗi ta ke yi" Sadiya ƙyaleta kin ji."
"Ke dai za ki faÉ—a min abin da kike nufi da zubar da abinci da na kawo. Sannan da mganganun da kike a kaina?waye zai kashe muku uwa? Sannan waye ya so kashe abin da ke cikin gimbiya? Sannan waye dangin asiri? Kar dai ki ce da ni ki ke ?
Na faɗa ina kallonta domin har duhu duhu na fara gani, ni za a yi ma tijara a bainar na si, ni za a ƙulla ma sheri a ci mutumcina da mutumcin dangina
"Na ce ina fatan ba da ni kike ba ko?
"Da ke ake ko kina da mgana ne?
Sai kawai na ƙura mata ido ina kallonta.
"Kika ce da ni kike? Ni ce mai yin asirin?
"Ke ce mana. Kin so zubar da cikin Gimbiya Allah ya fiki. Ai duk mun san komai. Mun san cewa Yayar mamanki asiri ta yi ma abokiyar zamanta kaikayi ya koma kan masheƙiya ta mutu cikin hauka, kowa ya san wannan labarin saboda asirinta ya tonu."
Mamaki ya hana ni mgana, idanuwana sun kawo ruwa cikin rawam murya na ce" A ina kika ji wannan labarin?
"A bakin da ba zai yi min ƙarya ba. Ma'u ce ta faɗa min ko za ta yi miki ƙarya ne?
"Ma'u."
Na maaimata sunan a saman laɓɓana.
Na kasa ma yin wani motai bakina na rawa na kasa mgana jikina ba in da baya rawa zuciyata ina jin kamar za ta faso ƙirjina ta fito saboda halin da na ke ciki.
"Ma'u fa?
Ma'u ƴar uwata da muka taso tare ita ce za ta zo dangin mijina ta yi min ƙazafi. Daman na san wannan bini binin na ta ba na lafiya ba ne. Sai ta ga na tozarta sannan hankalinta zai kwanta. Lalle ko akwai yaƙin duniya na uku tsakanina da Ma'u da duk wanda ke da hannu wajen yi min wannan mummunan ƙazafin.
*Janafty*
*TKG017*
"Bahijja kina mata wani sanyi sanyi ke Sadiya har mganin asirin suke kawo miki har gida. Gimbiya ta gan ki lokacin da ƙanwar mamanki ta kawo miki su har gida ko shima za ki ƙarya ta ne?
Kalaman Anty Maimuna suka buga min kai kamar an dake ni da ƙarfe sai da na ji kaina ya yi dum na ɗago ina kallonta ba bakina ba har idanuwana suna rawa ne a lokacin.
"Haba Anty Maimuna me ya sa haka?
Hauwa ta faɗa kamar ta yi kuka Munnira kuma sai ta hau tafa hannu ta na faɗin" Yanzu me Sadiya ta yi muku da za ku yi mata wannan mummunan ƙazafin?
Ni kuma Gimbiya na ke kallo cikin mamakinta ina so na tabbatar da gaske ita ce ta faɗi ta ga ƙanwar Mamana ta kawo min asiri? sai na ga ta kauda kaita alamun kenan da gaske ne. Sai kawai na ji na fara jijjiga ni kaɗai saboda ɓacin rai ranar da Inna Mariya ta zo kawo min mganin na dawo min a cikin idanuwa. Oh shi ya sa daman ta ce min ta ga ta na ta kallon mu? Kenan zargin ta kawo min asiri ta ke yi min tun da gashi har ta kawo labarin gaba. Kuma tunda ina shige shige kuma ina baƙin ciki da cikin da ke jikinta tun da ni ban taɓa haihuwa ba shi ya sa na ba ta mgani ta ci a abinci cikinta ya zube sai Allah ya fini asirina ya tonu cikin bai zube ba. Shi ne aka zauna aka tattauna gwara a turke ni a ci min mutumci, duk a lokaci ɗaya na gama hango abin da ya faru shi ya sa ban san na yi wata dariya ba sai da na ga ina yin ta cikin mamaki suke kallona Anty Bahijja na nuna da yatsa na ina faɗin.
"Ba a haifi wani É—a namijin da zan kauce ma Allah saboda shi ba Bahijja"
"Kuma kika kaucen?
"Tunda kin yarda na kauce kuma na yi asirin tun da kin ce ni yar na gada ce, sannan ma ai an ce an ga tabbaci me kike jira Bahijja?
Na kira sunanta cikin tsawa kafin ta samu zarafin magana na zare mayafin jikina na É—aure a kuguna ina faÉ—in
"Na ce tunda kin samu tabbaci me kike jira? Ba sai ki É—au mataki ba Bahijja?
Na faɗa ina nuna ta da yatsa, Itama ta so min tana faɗin zan ko ga matakin da za ta ɗauka Hauwa da Munnira na rike ni ina fizgewa, ita ma Bahijja su Maimuna na riƙe ta Nene ma ta mgana ba wanda ya ji ta, Hayaniya ya sa har su Hajiya Iya da Maman farko sai da suka shigo lokacin Anty Bahijja na faɗin zan ga abin da zai faru.
"Ba abin da zan gani sai alheri me zan gani? Ya wuce ki saka ƙanin ki ya sake ni? To sai me? Kaina farau zawarci ke in ba ki saka shi ya yi min saki uku ba tabbas ke Bahijja ba ki haufu cikin uwarki da uban ki ba."
"Ke Sadiya ki yi shuru"
In ji Maman farko Suwaiba na ja na ita da su Hauwa ta na faÉ—in" Sadiya mu je mu je Sadiya."
"Ni kike zagi don uban ki Sadiya. Ni sa'ar ki ce?
"An zage ki ɗin ke uwata ce da ba za ki zagu ba? Har ni za ki yi ma kazafi na so zubar da ciki? To ni na zubar da cikin gimbiya na ci riban me? Ko haihuwa ce ban taɓa yi ba da za ta zame min baƙuwa? Amma ba laifin ki ba ne, laifin wacce ta faɗa miki ne. Amma ina so ki sani da ke da wacce ta faɗa miki na rantse da wanda raina ke hannun shi sai na yi ƙaran ku a wajen hukuma."
Daƙyar su Suwaiba suka fita da ni daga ɗakin Nene tana zagina ina zaginta. Itama ana riƙe ta tana cewa a sake ta, ta doke ni "Na ce ku sake ta mana ta zo ta ga in zan bugun mata ko wanda na ke aure bai isa ya doke ba ballantana ke banza a banza."
Itama ana riƙe ta tana fizgewa faɗi ta ke yi wai ai ba ƙarya aka yi min ba. Ina shige shige na wanke gaba na ba ma Tafida ya sha da ba ya ganin laifina, na shanye musu ɗan'uwa ko auran shi ma da Gimbiya Allah ne ya fi ƙarfina shi ya sa aka yi auren.