Sashe 40
Turken Gida Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Wato saboda ya yi mini kishiya na zama abin dariyan shi kaɗan ya rage ban ture shi ba amma na yi masa bakam sai ya fara min cakulkuli tun ina kannewa har na kasa ina dariya na mirgina ina faɗin" Ka bari mana Yallaɓai."
Amma bai ƙyale ni, sai da ya ga na kusa fita hayyacina har ina hawaye duk mun birkita gadon sannan ya ƙyaleni shi ma ɗin bi na ya yi ya danne ya na min wasu abubuwan, tun ina ture shi har dai ya fi ƙarfina dole na ba da kai bori ya hau, sai da muka samu natsuwa sannan muka yi wanka muka kwanta da asuba ma bayan ya dawo masallci sai da ya ƙara nema mana wani ɓarnan ruwan
"Yallaɓai da sanyin nan kasan ɓarnan ruwa akwai wahala."
Ya na shafa fuskata kafin ya ce" Ya fi daɗi ne. Kuma kin san cewa kin ƙara daɗi Madam?
Ya faɗa ya na sumbatar goshina lokacin muna kwance a tare ne, saboda kalamansa sun yi kama da na yaudara yasa na yi masa banza. Wai kin ƙara daɗi! Duk da bai san na ƙara daɗi ba ne sai yanzu da ya je ya ɗanɗano wata? Ɗan renin wayau kawai.
"So na ke yi na sake ajiyar mai sunan Alhajinmu ko Baban Gwammaja"
Ya faɗa ya na shafa cikina zuwa saman marata, nima sai na ɗora hannuna saman hannun shi har na ji tahowar ƙwallah.
"Allah ya sa haka Yallaɓai na."
Ina so na sake haihuwa ni ko da guda É—aya ne."
Na faɗa ina jin sukan abin daga ƙasan raina.
"In sha Allahu za ki ƙara haihuwa ba ma ɗaya ba dozin."
Mirmishi kawai na yi amma ban yi mgana ba.
"Ya ku ka yi da Likita zuwan ki na ƙarshe asibiti?
Bayani na fara yi masa da cewa gwajin na ƙarshe ma ya na lap on 12 january zan koma in na karɓa sai na je na kai mata na ji me za ta ce tukunna.
" In sha Allahu ba matsala."
Na amsa da Allah ya sa.
Bai kuma ƙyale nin ba sai da ya saka mu muka sake ɓarnan ruwa da safen nan. Ranar dai a gida ya yini bai fita ba saboda shi ma na ƙi dukan Baby domin tunda ta tashi barci ta ga ba Jidda ta fara rigima da Yallaɓai baya nan da tuni jikinta ya faɗa mata, shi ya zauna ya na lallashinta ni ko kallo ba su ishe ni ba. Sai washegari ya fita ya ce min zai biya ya duba Gimbiya daga nan zai shiga Office. Baby ta nace masa da ita ya tafi da cewa wai zai dawo da ita in zai dawo gida ni dai ban yi magana ba ina jiran na ga iya gudun ruwan shi.
Sai ga shi tare da Gimbiyar suka kawo Jidda da Baby tun da yau ɗin ya na wajen ta ne. Ba su dade ba ni ma kuma ko fuska ban ba su ba muna gama gaisawa na bar su a falo na yi shigewata ciki sai da ya biyo ni muka yi sallama, hug ɗin ma na ƙi yarda na shige tiolet na bar shi nan dole ya wuce sai da na ji sun bar gidan na fito. Baby sun dawo da chaculte sai cincin da su alhaki suna ta budirinsu kallo ba su isheni ba suma ɗin haushin Ubansu ne duk ya shafe su.
Tun ina ganin lamarin Yallaɓai in ya yi kwana biyu a gidana ya je can ya yi kwana biyu a wasa har na tabbatar da cewa gaskiya ne. Ba ni kaɗai ba ce matar Yallaɓai yanzu ba. Yana da wata matar shi ya sa ko cefane yanzu biyu ne Musbahu ya kawo min itama ya kai mata. Ya na kawo ta gidana su zo tare amma ni ban taɓa marmarin zuwa gidanta ba. Kuma in dai ya na gidana sai ya dauki Jidda ya kai mata in kuma ya ma can sai ya dawo da ita yadda bai taɓa min magana kan Jidda ba nima ban taɓa yi masa ba. Kwanaki can ya yi min maganar kan me ya haɗamu da Anty Bahijja.?
a lokacin sai na tambaye sa.
"Me ta ce maka hala?
"Kawai ta na ta faÉ—a ne wai kin yi mata rashin kunya."
Sai na jinjina kai kafin na ce" Ita ya É—auke shi a rashin kunya amma ni ba haka na ke nufi ba"
Sai ya tambaye ni mai ya haɗamu na ɗan faɗa masa da cewa" Na faɗa mata ko kai da na ke zaman ka, in ka matsa min da zuwa haƙuri zan ba ka. Ina ga shi ne ta ji haushi."
A lokacin bai ce komai ba amma dai ya ce na kira ta na bata haƙuri ni ko dai na ce masa toh amma ban kira ba domin ban ga abin da na yi mata da zan kira ta na bata hakuri ba in ta so kar Allah ya sa ta haƙura in mun haɗu in na gaisheta kar ta amsa ita ta sani.
Shi daman Yallaɓai ba mai damuwa da bin diddigi ba ne bai ma ƙara ta da mganar ba, ba ni ƙila ma tuni ya manta da batun in dai ba ita Anty Bahijjan ta sake masa mgana ba. Ga shi muna cikin sati na biyilu da tariyan Gimbiya tun ina tunanin zan iya sabawa da sallaman Yallaɓai in zai bar gidana har na fara tunanin har abada ba a sabawa kullum ne lamarin ni sabo na ke kallon shi a idanuwana. Ga shi tun bayan bikin ba wanda ya dawo gidana sai dai mu yi magana da su Hauwa ta waya Suwaiba ma sai da na kirata sannan ta turamin hotunan da ta ɗauke mu ni da Yallaɓai sun yi kyau amma ko status ban yi da su ba amma dai na ga Anty Maimuna ta sassaka hotunan su na bikin tariyan ƙila a lokacin ba ta samu sukunin sakawa ba, duk na kalla daga baya ne na yi ta daman kalla domin har da hoton Yallaɓai da Gimbiya su biyu, ta kwantar da kanta saman kafaɗansa ta na dariya shi kuma ya juya ya na kallonta kamar dai magana ya ke yi mata aka ɗau hoto.
A ƙasan hoton ta saka caption.
"Tafida da Gimbiyarsa. Alƙawarin Allah ya tabbata."
Lalle fa Gimbiyarsa. Hoton nan da na gani ya daɗe yana gilmamin a cikin mafarkina da zahirina. Duk in da na zauna ko na kwanta da na runtse ido su na ke gani sai da na yi ta kiran sunan Allah sannan na samu sukuni da salama. Sai a yanzu na ke ganin cewa daman tun can Yallaɓai na son Gimbiya dama ne bai samu ba. Wannan rawan jikin kam ya na yi mata a gaba na kuma sai ya riƙa nuna ni ya ke yi ma rawan jiki, wai ni Yallaɓai zai maida ƙaramar yarinya Allah na tuba wani dare ne jemage bai gani ba ai sai dai daren mutuwarsa.
****
20January 2016.
Tuni na koma asibiti na ga Dr. Aisha Alhandulillah abin farincikina duka na tsallake matakin gwaje gwajen su kuma ta ba ni tabbacin ba wata matsala mai girma. Sai dai kawai side effect ya taɓa ni sannan kuma hormones ɗina sun ɗan yi rauni ne amma ta rubutamin manganganun da za su dai dai tamin al'ada da wanda za su ƙara taimaka min wajen samun ciki suna da tsada domin da na je phamarcy ma kuɗin da Yallaɓai ya ba ni ba su isa ba, na yi ta kiran wayar shi ban samu ba sai na kira na Musbahu shi ya faɗa masa sai shi kuma ya taho asibitin ya same ni, bayan ya biya kuɗin magunguna ya ɗauke ni ya maida ni gida. Duk da ina da kuɗi a cikin acct da gangan na ƙi taɓa su ni fa yanzu na fara jin ƙyashi yin hidimar da nawa ba, ba kamar da ba da shi kan shi ya san wani abun ma ba na jiran shi.
Kan jiki kan karfi na dage na fara shan magunguna na saboda fata na da burina ni ma Allah ya sake ba ni wani cikin ko É—aya ne na sake haifa.
Kwana biyu tsakani na je gidan Hauwa daga can ni da ita muka je gidan Munnira muka haɗu muna ta hira. Sun tambayeni ya yanayin zaman na ce lafiya lau. To me zan ce? Zaman da yanzu aka fara ai sai tafiya ta tafi sannan halin kowa ma zai bayyana. Hauwa ita dai faɗi ta ke yi Yallaɓai ɗan halas ne, ni ko a raina na ce ai ba a yabon ɗan kuturu sai ya shekara da yatsa a hannun shi.
Sai yamma muka rabu Hauwa ta hau adaidaita anguwarsu nima na hau ta anguwarmu na koma gida. Ina komawa ma na iske Marwa ta zo daga asibiti ta biyo ba na gida, daman Saude na bari a gida tare da su Jidda sai da dawo suka tafi gabaÉ—aya.
Amma bai ƙyale ni, sai da ya ga na kusa fita hayyacina har ina hawaye duk mun birkita gadon sannan ya ƙyaleni shi ma ɗin bi na ya yi ya danne ya na min wasu abubuwan, tun ina ture shi har dai ya fi ƙarfina dole na ba da kai bori ya hau, sai da muka samu natsuwa sannan muka yi wanka muka kwanta da asuba ma bayan ya dawo masallci sai da ya ƙara nema mana wani ɓarnan ruwan
"Yallaɓai da sanyin nan kasan ɓarnan ruwa akwai wahala."
Ya na shafa fuskata kafin ya ce" Ya fi daɗi ne. Kuma kin san cewa kin ƙara daɗi Madam?
Ya faɗa ya na sumbatar goshina lokacin muna kwance a tare ne, saboda kalamansa sun yi kama da na yaudara yasa na yi masa banza. Wai kin ƙara daɗi! Duk da bai san na ƙara daɗi ba ne sai yanzu da ya je ya ɗanɗano wata? Ɗan renin wayau kawai.
"So na ke yi na sake ajiyar mai sunan Alhajinmu ko Baban Gwammaja"
Ya faɗa ya na shafa cikina zuwa saman marata, nima sai na ɗora hannuna saman hannun shi har na ji tahowar ƙwallah.
"Allah ya sa haka Yallaɓai na."
Ina so na sake haihuwa ni ko da guda É—aya ne."
Na faɗa ina jin sukan abin daga ƙasan raina.
"In sha Allahu za ki ƙara haihuwa ba ma ɗaya ba dozin."
Mirmishi kawai na yi amma ban yi mgana ba.
"Ya ku ka yi da Likita zuwan ki na ƙarshe asibiti?
Bayani na fara yi masa da cewa gwajin na ƙarshe ma ya na lap on 12 january zan koma in na karɓa sai na je na kai mata na ji me za ta ce tukunna.
" In sha Allahu ba matsala."
Na amsa da Allah ya sa.
Bai kuma ƙyale nin ba sai da ya saka mu muka sake ɓarnan ruwa da safen nan. Ranar dai a gida ya yini bai fita ba saboda shi ma na ƙi dukan Baby domin tunda ta tashi barci ta ga ba Jidda ta fara rigima da Yallaɓai baya nan da tuni jikinta ya faɗa mata, shi ya zauna ya na lallashinta ni ko kallo ba su ishe ni ba. Sai washegari ya fita ya ce min zai biya ya duba Gimbiya daga nan zai shiga Office. Baby ta nace masa da ita ya tafi da cewa wai zai dawo da ita in zai dawo gida ni dai ban yi magana ba ina jiran na ga iya gudun ruwan shi.
Sai ga shi tare da Gimbiyar suka kawo Jidda da Baby tun da yau ɗin ya na wajen ta ne. Ba su dade ba ni ma kuma ko fuska ban ba su ba muna gama gaisawa na bar su a falo na yi shigewata ciki sai da ya biyo ni muka yi sallama, hug ɗin ma na ƙi yarda na shige tiolet na bar shi nan dole ya wuce sai da na ji sun bar gidan na fito. Baby sun dawo da chaculte sai cincin da su alhaki suna ta budirinsu kallo ba su isheni ba suma ɗin haushin Ubansu ne duk ya shafe su.
Tun ina ganin lamarin Yallaɓai in ya yi kwana biyu a gidana ya je can ya yi kwana biyu a wasa har na tabbatar da cewa gaskiya ne. Ba ni kaɗai ba ce matar Yallaɓai yanzu ba. Yana da wata matar shi ya sa ko cefane yanzu biyu ne Musbahu ya kawo min itama ya kai mata. Ya na kawo ta gidana su zo tare amma ni ban taɓa marmarin zuwa gidanta ba. Kuma in dai ya na gidana sai ya dauki Jidda ya kai mata in kuma ya ma can sai ya dawo da ita yadda bai taɓa min magana kan Jidda ba nima ban taɓa yi masa ba. Kwanaki can ya yi min maganar kan me ya haɗamu da Anty Bahijja.?
a lokacin sai na tambaye sa.
"Me ta ce maka hala?
"Kawai ta na ta faÉ—a ne wai kin yi mata rashin kunya."
Sai na jinjina kai kafin na ce" Ita ya É—auke shi a rashin kunya amma ni ba haka na ke nufi ba"
Sai ya tambaye ni mai ya haɗamu na ɗan faɗa masa da cewa" Na faɗa mata ko kai da na ke zaman ka, in ka matsa min da zuwa haƙuri zan ba ka. Ina ga shi ne ta ji haushi."
A lokacin bai ce komai ba amma dai ya ce na kira ta na bata haƙuri ni ko dai na ce masa toh amma ban kira ba domin ban ga abin da na yi mata da zan kira ta na bata hakuri ba in ta so kar Allah ya sa ta haƙura in mun haɗu in na gaisheta kar ta amsa ita ta sani.
Shi daman Yallaɓai ba mai damuwa da bin diddigi ba ne bai ma ƙara ta da mganar ba, ba ni ƙila ma tuni ya manta da batun in dai ba ita Anty Bahijjan ta sake masa mgana ba. Ga shi muna cikin sati na biyilu da tariyan Gimbiya tun ina tunanin zan iya sabawa da sallaman Yallaɓai in zai bar gidana har na fara tunanin har abada ba a sabawa kullum ne lamarin ni sabo na ke kallon shi a idanuwana. Ga shi tun bayan bikin ba wanda ya dawo gidana sai dai mu yi magana da su Hauwa ta waya Suwaiba ma sai da na kirata sannan ta turamin hotunan da ta ɗauke mu ni da Yallaɓai sun yi kyau amma ko status ban yi da su ba amma dai na ga Anty Maimuna ta sassaka hotunan su na bikin tariyan ƙila a lokacin ba ta samu sukunin sakawa ba, duk na kalla daga baya ne na yi ta daman kalla domin har da hoton Yallaɓai da Gimbiya su biyu, ta kwantar da kanta saman kafaɗansa ta na dariya shi kuma ya juya ya na kallonta kamar dai magana ya ke yi mata aka ɗau hoto.
A ƙasan hoton ta saka caption.
"Tafida da Gimbiyarsa. Alƙawarin Allah ya tabbata."
Lalle fa Gimbiyarsa. Hoton nan da na gani ya daɗe yana gilmamin a cikin mafarkina da zahirina. Duk in da na zauna ko na kwanta da na runtse ido su na ke gani sai da na yi ta kiran sunan Allah sannan na samu sukuni da salama. Sai a yanzu na ke ganin cewa daman tun can Yallaɓai na son Gimbiya dama ne bai samu ba. Wannan rawan jikin kam ya na yi mata a gaba na kuma sai ya riƙa nuna ni ya ke yi ma rawan jiki, wai ni Yallaɓai zai maida ƙaramar yarinya Allah na tuba wani dare ne jemage bai gani ba ai sai dai daren mutuwarsa.
****
20January 2016.
Tuni na koma asibiti na ga Dr. Aisha Alhandulillah abin farincikina duka na tsallake matakin gwaje gwajen su kuma ta ba ni tabbacin ba wata matsala mai girma. Sai dai kawai side effect ya taɓa ni sannan kuma hormones ɗina sun ɗan yi rauni ne amma ta rubutamin manganganun da za su dai dai tamin al'ada da wanda za su ƙara taimaka min wajen samun ciki suna da tsada domin da na je phamarcy ma kuɗin da Yallaɓai ya ba ni ba su isa ba, na yi ta kiran wayar shi ban samu ba sai na kira na Musbahu shi ya faɗa masa sai shi kuma ya taho asibitin ya same ni, bayan ya biya kuɗin magunguna ya ɗauke ni ya maida ni gida. Duk da ina da kuɗi a cikin acct da gangan na ƙi taɓa su ni fa yanzu na fara jin ƙyashi yin hidimar da nawa ba, ba kamar da ba da shi kan shi ya san wani abun ma ba na jiran shi.
Kan jiki kan karfi na dage na fara shan magunguna na saboda fata na da burina ni ma Allah ya sake ba ni wani cikin ko É—aya ne na sake haifa.
Kwana biyu tsakani na je gidan Hauwa daga can ni da ita muka je gidan Munnira muka haɗu muna ta hira. Sun tambayeni ya yanayin zaman na ce lafiya lau. To me zan ce? Zaman da yanzu aka fara ai sai tafiya ta tafi sannan halin kowa ma zai bayyana. Hauwa ita dai faɗi ta ke yi Yallaɓai ɗan halas ne, ni ko a raina na ce ai ba a yabon ɗan kuturu sai ya shekara da yatsa a hannun shi.
Sai yamma muka rabu Hauwa ta hau adaidaita anguwarsu nima na hau ta anguwarmu na koma gida. Ina komawa ma na iske Marwa ta zo daga asibiti ta biyo ba na gida, daman Saude na bari a gida tare da su Jidda sai da dawo suka tafi gabaÉ—aya.