Sashe 94
Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read
******
*MURFI..*
*After 10 Years..*
Bayan shekaru goma da suka Gabata.
Dr.Rumana Muhammad wamako Yar kimamin Shekaru Talatin da Biyar a Duniya zaune take Cikin Babban Office dinta Dake cikin Asibitin Specialist Hospital Abuja,Bangaran yara paediatriction Inda anan take aiki Shekaru Uku da suka Gabata.
In ka kalleta Dole ka kara kallonta Kamar ba itace ta mallaki wannan Shekarun ba Har yanzu yarintarta da wannan Mirmishin nata mai karamata kwarjini da kima Sanye take da Doguwar riga kirar Armani Tayi Rolling din mayafin Rigar sai wani Siririn glass din Dake idanuwanta mai kara mata karfin gani ta ko"ina Rayuwa ta yi kyau Sai son barka.
Ashekarin da suka Shude abubuwa Dadama sun Faru an samu rashi,an kuma samu karuwar abubuwa Dadama acikin Rashin da akayi sun Rasa Ayya Shakarun baya Allahu akbar Allah ya jikanta da Rahma
Sun samu karuwa Domin tayi Haihuwan Farko ita da Diza Diza ta Rigata Haihuwa da Sati Biyu kafin itama ta Ssuka Dukkansu mata suka Haifa sai suka ci Hajja da Mommy,Wato Hajara da Asiya kenan kuma suna kiransu da Hajja da Mommy ne suna Boye sunansa,Bayan Mommy,Rumana ta kara Haihuwan Habib wanda yaci Sunan Baba Habibu sai Diza Data kara Haihuwan mai sunan Umma,suna kiranta da Ummanti,Rumana sai ta Dakata da Haihuwa saboda Karatunta sai Diza ce ta samu mai sunan Daddy Sunusi,sai da Rumana ta gama karatunta tayi ma Mastur Takwara Shima,Wanda Dagashi bata kara Haihuwa ba sai Diza ce ta Kara Haihuwan Mace taci Ayya suna kiranta da Ayya,Gidan Mastur Ya cika da ya'ya Alhamdulillah,Ahalin Dayake Ciki yanzu ya tashi Daga Dcp Mastur ya koma IGP Nakasa Gabadaya Shekaru Biyu da suka Gabata,Suka Tattaro suka Dawo nan Abuja da Zama,Cikin katon Gidansu da Mastur ya mallaka mai Dauke da Shashi masu Girma da tsari,
Mastur ya cika Burin marigayi Mansur yakai Duka iyayansu Makka,Daddy mommy,Hajja Baba Habibu da Baba sule da Inna Zainaba sai Kawu Usman da Inna Balaraba wadanda Mastur ya sa aka gyara musu Gidansu ya koma na Zamani.
Sai bayan sun dawo ne Shima Dashi da Iyalansa Gabadaya sukaje sukayi Hajja,Daganan suka wuce India sukayi sati Biyu suka Dawo gida saboda Yara da karatunsu.
Lokacin kafin su koma Abuja yawanci Diza tafi zaman porthercourt,ita kuma Rumana tana Zaria saboda Karatunta sai ya zamana sai ta samu Hutu take zuwa ma Mastur,Yawanci yaran Diza duk ita ta Reno su ita dasu Hajja Diza dai ta kan Haifa Ta barma Rumana Shiyasa ko taki ko taso Rumana mace ce mai Girma da Daraja acikin Idanuwan kowa.
Gabadaya Mastur ya inganta Rayuwar iyayansa ya Dawo da Baba Sule da iyalansa nan Zaria agidansu,da suka bari Rayuwa tayi Dadi Mardiya tayi aure a kaduna har ta Haiyayyafa haka su Maryama da su Sakina kowacce ta zama uwa sosai,Basma kawar Rumana tayi aure anan zaria ta auri Sagir Allah yace shine mijinta yaransu Biyu,Haka ma Aisha bala tayi aure a lagos Ashekarar Data gabata itama Dayake ta tsaya Cigaban karatunta bangaran mata wato Gyneacologist
Rayuwa tayi Dadi sai son Barka Mastur ya Riga ya Dauke Dukkan Nauyin Dake kansa wanda abaya Dashi da Mansur suke Daukesa Albarka iyaye da yan"uwa bazata bar Zagaye dash ba.
Mansur Karami Dayake amsa sunan Mansur S.Mansur Doguwa yana Bording school anan Abujan sai sun samu Hutu yake zuwa Sauran yaran kuma suna Day ne anan garin Abujan Direba kai kaisu ko Diza ta kai su ta Dawo dasu Ita ta zama Hajiya yanzu manya Cateing gareta Har Abuja Da kaduna,Mastur ya Tallafa mata sosai ta Bunkasa aikinta da kasuwancinta yanzu bama Nageria ba Harta Kashashen waje sun san Labarin Diza Catering and Makeup da Diza Beuty Saloon.
Yanzu da suka Dawo waje Daya Diza ce ke kula da yaran duk da Rumana ta Dauko Juma jikar Goggo Jumai sun taho da ita nan Abuja Tana Taimaka musu,Ita daman Tun Safe take Fita sai yammah ita da Ogan da kansa Sai Diza agida in ba an kirata ta Fita yin wani bane wajen Catering dinta Tana gida Tana Hutawa.
*****
Rumana Tana tsaka da Duba patient Misalin karfe 6pm na yammah Sauri take ta tashi bata son Tukin Dare kuma Yallabai Mastur sam bayaso Fada yake mata,Tana Haraman Tashi ne kiran Diza ya Shigo wayarta ta Daga Tana Fadin"Ga ni nan a Hanya..Yanzu na Tashi Mamin yara..!
Haka take cemata Tunda haka yaran ke kiranta ayayinta ita kuma suke Cemata Mama Diza Dagachan Bangaran Tace'Mamansu Gida fa yau ba kowa..Duka yara basa nan..!
Rumana cikin mamaki tace"Bangane ba? basu Dawo Daga School bane..!
Diza tace"Sun dawo kin mata yau suka samu Hutu..suna Dawowa suka Iske Direban Daddy yazo suka Hau Shiri sai sun Bishi na Kira Yallabai na gayamai yace na Tattarasu duka ya kaisu Wajen su Hajja.."
Rumana Tayi Dariya Tana Fadin"Daman ance wannan karon Zaria za"aje Tunda wanchan Hutun Umma akayi ma shi.."Diza tace"Aikuwa su Mommy nachan na Murna yanzu muka gama waya da ita Har sun isa .Ban kira ki bane sanin kina aiki..!
Rumana tace"Yayi kyau muma ma Huta ina..Megidana..!
Diza tace"Dashi aka tafi..!
Rumana ta waro ido Tana Fadin"Na shiga uku..Yaron nan ya Cika Rigima mamin yara..!
Diza tace"Kuka ya Dinga yi Dayaga zasu tafi..Yallabai najin haka yace a hadamai kayansa a kaima Hajja Babban Mutum dinta..!
Rumana tace"Shikenan sai na kariso..!
Daga haka suka yanke kiran Lapcot dinta ta Dauka da wayarta sai Jakarta ta Fito Tana Amsa gaisuwan Likitoci da Nurse din Dake kai da kawo Tana Fita Haraban asibitin ta Shiga Motarta Kirar Prado ta Fice Daga asibiti.
Anguwan Maitama suke da zama nan ta Nufa ana Bude mata Wagegen get din ta Sulala ciki ne nan Motar IGP Mastur Habib Doguwa ta sawo kai Shima yana Daga Baya Direba na jansa,Kusan Lokaci Daya suka Shigo Gidan.
Rumana Data Fito sai da ta jira Mastur wanda Direba ya Budemai ya Fito Dan kimamin Shekaru 50 da wani abu Duniya ammh jin Dadi da Hutu sun Boye haka sanye yake da Uniform dinsa Domin Daga Villa yake sunyi ganawar Sirri da Shugaban kasa Tunda ga nesa suke sakin ma Juna Mirmishi kafin su Fara taku zuwa ga junansu.
Rumgume juna sukayi Cikin Shauki Mastur na Fadin"Dr na..!Rumana na..!
Itama Rumanan din Cikin farinciki take fadin"Yallabaina..Mastur dina..!
Dariya suka saka Gabadayansu Kafin su Nufi kofar da zata sadasu da Babban Falon gidan
Wani Dan Sanda na Binsu da wayoyin Yallabai.
Suna Shiga Falon da Sallama Kamshin ya Dakesu a tare suka Lumshe ido Lokaci Daya suka Furta.."Mamin yara..!
Suka Fada Lokaci Daya suna kallon juna Shi dai Dan sandan nan shiga yayi ya zube Wayoyin saman Wani Tamgamemin Glass Dake Tsakiyar falon ya sara kafin ya Fice.
Sun Fara takawa zuwa Tsakiyar Falon hannunsu Rike da juna Juma ta Fito Daga Kitchen Tana yi musu maraba da sauri ta koma Kirchen ta Hado Abun sha da Lemi ta kawo musu Lokacin har sum samu matsugunni a kan Daya Daga cikin kujerin Falon Rumana ta Tsiyaya Ruwa a glass cup Cup ta mikama Mastur itama ta Zuba Tana sha Tana mamakin ina Diza taShiga Juma ta kwalama kira Bayan tazo tace mata Ina Diza kafin ma ta bata amsa sai ga Diza tana Fitowa Daga Kitchen Tana Turo wani Katon tubur na glass Dauke da wani katon Cake taci kwalliya sosai da ka ganta kaga Dizan Mansur Dizan Mastur sai dai ta kara Girma da cikar Haihuwa data Hutu da jin Dadi.
Baki sake suke kallonta Tana Karisowa gabansu ta ja ta tsaya Tana Fadin"Happy 15 years Marrige Annivesery...Dr.Rumana muhammad wamako and ur Lovely Husband IGP Mastur Sulaiman Doguwa..!
Tafada Lokaci Daya wasu Fulawars na Zubowa ta saman kansu Cikin Sha"awa ta juya tana Dagama juma Hannu alamun jinjina itama ta Dagamata Domin tare suka Shirya komai.
Bakinsu yaki Rufuwa saboda Murna Gabadaya sun ma manta,Yau ne suke cika Shekaru goma Sha Biyar da aure Matakin Rayuwa kala kala sun taka da Farinciki.
Rumana sai Hawaye ya Ciko Idanuwanta Ta Rumgume Diza Tana mata godiya Dukkansu Mastur ya Hada ya Rumgume,Tuni Juma ta kawo Wukan yankar Cake karama Rumana da Mastur suka Rike hannu zasu yanka Cake Rumana ta Jawo hannun Diza ta Dora saman nasu ta Dagamata kai suka yanka gabadaya,Mastur shi ya Fara basu Dukkansu abaki kafin kowacce ta bama Yar'uwanta Lokaci Daya suka Tarovsuka Turama Mastur Cake abaki kamar zai yi amai yana Haki yace"Kai kai..Ku mugaye ne ko..?
Suna jin haka Diza da Rumana suka kalli juna kafin su Lakuti Cake din suka Laftamai a Fuska ya Kwabe Fuska yana kallonsu kafin yace'Lala..Mamansu da maminsu sai fa na Rama nima..!
Fadar haka yasa shima ya lakuti Cake din ya Dumfaresu da gudu suka Dare suna Darewa suka Fara Zagayen Falon Shi kuma yana Binsu yana Fadin"Mugaye sai na Rama..!
Juma Dake Kitchen Tana kallonsu ta Girgiza kai Tana Fadin"Ya Allah ka Cigaba da Dauwamar da Farinciki a wannan gidan da Zuru"arsu gabadaya..!
Ammh har gaban Abada bazasu Taba mantawa da Rashin da sukayi ba Rashin Mansur Sulaiman Doguwa wani Rashi ne daHar Abada wanda wannan ahalin bazasu mantashi ba,kaf yaran ba wanda baisan labarin Marigayi Baba Mansur ba Daga bakin Daddynsu ba haka kuma Office dinsa da Dakin barcinsa makale da Hotunan Mansur din da suke Dauka Lokacin suna raye.
Mansur karami ya san ba Mastur ne ya Haifesa ba ammh kuma Bashi da maraicin wani bango
Rumana ce uwarsa har gobe Mastur Ubansu Diza kuma Anty take awajensa..!
*Tammat Bihamdullahi*
*Alhamdulillah nan na kawo karshen wannan Labarin nawa..Abunda na Rubuta Daidai Allah ya bani ladansa Kuskuran Dake ciki kuma Allah ya yafemin ina Godiya Masoya da kuka Nunamin kauna wajen Siyan Littafaina Allah ya saka muku da alheri Sai mun hadu a Sabuwar Shekara Cikin wata Tafiyar..!*
*Shakira*
*Janafty*
*Intelligent writer"s asso*
*23/12/2021*
*MURFI..*
*After 10 Years..*
Bayan shekaru goma da suka Gabata.
Dr.Rumana Muhammad wamako Yar kimamin Shekaru Talatin da Biyar a Duniya zaune take Cikin Babban Office dinta Dake cikin Asibitin Specialist Hospital Abuja,Bangaran yara paediatriction Inda anan take aiki Shekaru Uku da suka Gabata.
In ka kalleta Dole ka kara kallonta Kamar ba itace ta mallaki wannan Shekarun ba Har yanzu yarintarta da wannan Mirmishin nata mai karamata kwarjini da kima Sanye take da Doguwar riga kirar Armani Tayi Rolling din mayafin Rigar sai wani Siririn glass din Dake idanuwanta mai kara mata karfin gani ta ko"ina Rayuwa ta yi kyau Sai son barka.
Ashekarin da suka Shude abubuwa Dadama sun Faru an samu rashi,an kuma samu karuwar abubuwa Dadama acikin Rashin da akayi sun Rasa Ayya Shakarun baya Allahu akbar Allah ya jikanta da Rahma
Sun samu karuwa Domin tayi Haihuwan Farko ita da Diza Diza ta Rigata Haihuwa da Sati Biyu kafin itama ta Ssuka Dukkansu mata suka Haifa sai suka ci Hajja da Mommy,Wato Hajara da Asiya kenan kuma suna kiransu da Hajja da Mommy ne suna Boye sunansa,Bayan Mommy,Rumana ta kara Haihuwan Habib wanda yaci Sunan Baba Habibu sai Diza Data kara Haihuwan mai sunan Umma,suna kiranta da Ummanti,Rumana sai ta Dakata da Haihuwa saboda Karatunta sai Diza ce ta samu mai sunan Daddy Sunusi,sai da Rumana ta gama karatunta tayi ma Mastur Takwara Shima,Wanda Dagashi bata kara Haihuwa ba sai Diza ce ta Kara Haihuwan Mace taci Ayya suna kiranta da Ayya,Gidan Mastur Ya cika da ya'ya Alhamdulillah,Ahalin Dayake Ciki yanzu ya tashi Daga Dcp Mastur ya koma IGP Nakasa Gabadaya Shekaru Biyu da suka Gabata,Suka Tattaro suka Dawo nan Abuja da Zama,Cikin katon Gidansu da Mastur ya mallaka mai Dauke da Shashi masu Girma da tsari,
Mastur ya cika Burin marigayi Mansur yakai Duka iyayansu Makka,Daddy mommy,Hajja Baba Habibu da Baba sule da Inna Zainaba sai Kawu Usman da Inna Balaraba wadanda Mastur ya sa aka gyara musu Gidansu ya koma na Zamani.
Sai bayan sun dawo ne Shima Dashi da Iyalansa Gabadaya sukaje sukayi Hajja,Daganan suka wuce India sukayi sati Biyu suka Dawo gida saboda Yara da karatunsu.
Lokacin kafin su koma Abuja yawanci Diza tafi zaman porthercourt,ita kuma Rumana tana Zaria saboda Karatunta sai ya zamana sai ta samu Hutu take zuwa ma Mastur,Yawanci yaran Diza duk ita ta Reno su ita dasu Hajja Diza dai ta kan Haifa Ta barma Rumana Shiyasa ko taki ko taso Rumana mace ce mai Girma da Daraja acikin Idanuwan kowa.
Gabadaya Mastur ya inganta Rayuwar iyayansa ya Dawo da Baba Sule da iyalansa nan Zaria agidansu,da suka bari Rayuwa tayi Dadi Mardiya tayi aure a kaduna har ta Haiyayyafa haka su Maryama da su Sakina kowacce ta zama uwa sosai,Basma kawar Rumana tayi aure anan zaria ta auri Sagir Allah yace shine mijinta yaransu Biyu,Haka ma Aisha bala tayi aure a lagos Ashekarar Data gabata itama Dayake ta tsaya Cigaban karatunta bangaran mata wato Gyneacologist
Rayuwa tayi Dadi sai son Barka Mastur ya Riga ya Dauke Dukkan Nauyin Dake kansa wanda abaya Dashi da Mansur suke Daukesa Albarka iyaye da yan"uwa bazata bar Zagaye dash ba.
Mansur Karami Dayake amsa sunan Mansur S.Mansur Doguwa yana Bording school anan Abujan sai sun samu Hutu yake zuwa Sauran yaran kuma suna Day ne anan garin Abujan Direba kai kaisu ko Diza ta kai su ta Dawo dasu Ita ta zama Hajiya yanzu manya Cateing gareta Har Abuja Da kaduna,Mastur ya Tallafa mata sosai ta Bunkasa aikinta da kasuwancinta yanzu bama Nageria ba Harta Kashashen waje sun san Labarin Diza Catering and Makeup da Diza Beuty Saloon.
Yanzu da suka Dawo waje Daya Diza ce ke kula da yaran duk da Rumana ta Dauko Juma jikar Goggo Jumai sun taho da ita nan Abuja Tana Taimaka musu,Ita daman Tun Safe take Fita sai yammah ita da Ogan da kansa Sai Diza agida in ba an kirata ta Fita yin wani bane wajen Catering dinta Tana gida Tana Hutawa.
*****
Rumana Tana tsaka da Duba patient Misalin karfe 6pm na yammah Sauri take ta tashi bata son Tukin Dare kuma Yallabai Mastur sam bayaso Fada yake mata,Tana Haraman Tashi ne kiran Diza ya Shigo wayarta ta Daga Tana Fadin"Ga ni nan a Hanya..Yanzu na Tashi Mamin yara..!
Haka take cemata Tunda haka yaran ke kiranta ayayinta ita kuma suke Cemata Mama Diza Dagachan Bangaran Tace'Mamansu Gida fa yau ba kowa..Duka yara basa nan..!
Rumana cikin mamaki tace"Bangane ba? basu Dawo Daga School bane..!
Diza tace"Sun dawo kin mata yau suka samu Hutu..suna Dawowa suka Iske Direban Daddy yazo suka Hau Shiri sai sun Bishi na Kira Yallabai na gayamai yace na Tattarasu duka ya kaisu Wajen su Hajja.."
Rumana Tayi Dariya Tana Fadin"Daman ance wannan karon Zaria za"aje Tunda wanchan Hutun Umma akayi ma shi.."Diza tace"Aikuwa su Mommy nachan na Murna yanzu muka gama waya da ita Har sun isa .Ban kira ki bane sanin kina aiki..!
Rumana tace"Yayi kyau muma ma Huta ina..Megidana..!
Diza tace"Dashi aka tafi..!
Rumana ta waro ido Tana Fadin"Na shiga uku..Yaron nan ya Cika Rigima mamin yara..!
Diza tace"Kuka ya Dinga yi Dayaga zasu tafi..Yallabai najin haka yace a hadamai kayansa a kaima Hajja Babban Mutum dinta..!
Rumana tace"Shikenan sai na kariso..!
Daga haka suka yanke kiran Lapcot dinta ta Dauka da wayarta sai Jakarta ta Fito Tana Amsa gaisuwan Likitoci da Nurse din Dake kai da kawo Tana Fita Haraban asibitin ta Shiga Motarta Kirar Prado ta Fice Daga asibiti.
Anguwan Maitama suke da zama nan ta Nufa ana Bude mata Wagegen get din ta Sulala ciki ne nan Motar IGP Mastur Habib Doguwa ta sawo kai Shima yana Daga Baya Direba na jansa,Kusan Lokaci Daya suka Shigo Gidan.
Rumana Data Fito sai da ta jira Mastur wanda Direba ya Budemai ya Fito Dan kimamin Shekaru 50 da wani abu Duniya ammh jin Dadi da Hutu sun Boye haka sanye yake da Uniform dinsa Domin Daga Villa yake sunyi ganawar Sirri da Shugaban kasa Tunda ga nesa suke sakin ma Juna Mirmishi kafin su Fara taku zuwa ga junansu.
Rumgume juna sukayi Cikin Shauki Mastur na Fadin"Dr na..!Rumana na..!
Itama Rumanan din Cikin farinciki take fadin"Yallabaina..Mastur dina..!
Dariya suka saka Gabadayansu Kafin su Nufi kofar da zata sadasu da Babban Falon gidan
Wani Dan Sanda na Binsu da wayoyin Yallabai.
Suna Shiga Falon da Sallama Kamshin ya Dakesu a tare suka Lumshe ido Lokaci Daya suka Furta.."Mamin yara..!
Suka Fada Lokaci Daya suna kallon juna Shi dai Dan sandan nan shiga yayi ya zube Wayoyin saman Wani Tamgamemin Glass Dake Tsakiyar falon ya sara kafin ya Fice.
Sun Fara takawa zuwa Tsakiyar Falon hannunsu Rike da juna Juma ta Fito Daga Kitchen Tana yi musu maraba da sauri ta koma Kirchen ta Hado Abun sha da Lemi ta kawo musu Lokacin har sum samu matsugunni a kan Daya Daga cikin kujerin Falon Rumana ta Tsiyaya Ruwa a glass cup Cup ta mikama Mastur itama ta Zuba Tana sha Tana mamakin ina Diza taShiga Juma ta kwalama kira Bayan tazo tace mata Ina Diza kafin ma ta bata amsa sai ga Diza tana Fitowa Daga Kitchen Tana Turo wani Katon tubur na glass Dauke da wani katon Cake taci kwalliya sosai da ka ganta kaga Dizan Mansur Dizan Mastur sai dai ta kara Girma da cikar Haihuwa data Hutu da jin Dadi.
Baki sake suke kallonta Tana Karisowa gabansu ta ja ta tsaya Tana Fadin"Happy 15 years Marrige Annivesery...Dr.Rumana muhammad wamako and ur Lovely Husband IGP Mastur Sulaiman Doguwa..!
Tafada Lokaci Daya wasu Fulawars na Zubowa ta saman kansu Cikin Sha"awa ta juya tana Dagama juma Hannu alamun jinjina itama ta Dagamata Domin tare suka Shirya komai.
Bakinsu yaki Rufuwa saboda Murna Gabadaya sun ma manta,Yau ne suke cika Shekaru goma Sha Biyar da aure Matakin Rayuwa kala kala sun taka da Farinciki.
Rumana sai Hawaye ya Ciko Idanuwanta Ta Rumgume Diza Tana mata godiya Dukkansu Mastur ya Hada ya Rumgume,Tuni Juma ta kawo Wukan yankar Cake karama Rumana da Mastur suka Rike hannu zasu yanka Cake Rumana ta Jawo hannun Diza ta Dora saman nasu ta Dagamata kai suka yanka gabadaya,Mastur shi ya Fara basu Dukkansu abaki kafin kowacce ta bama Yar'uwanta Lokaci Daya suka Tarovsuka Turama Mastur Cake abaki kamar zai yi amai yana Haki yace"Kai kai..Ku mugaye ne ko..?
Suna jin haka Diza da Rumana suka kalli juna kafin su Lakuti Cake din suka Laftamai a Fuska ya Kwabe Fuska yana kallonsu kafin yace'Lala..Mamansu da maminsu sai fa na Rama nima..!
Fadar haka yasa shima ya lakuti Cake din ya Dumfaresu da gudu suka Dare suna Darewa suka Fara Zagayen Falon Shi kuma yana Binsu yana Fadin"Mugaye sai na Rama..!
Juma Dake Kitchen Tana kallonsu ta Girgiza kai Tana Fadin"Ya Allah ka Cigaba da Dauwamar da Farinciki a wannan gidan da Zuru"arsu gabadaya..!
Ammh har gaban Abada bazasu Taba mantawa da Rashin da sukayi ba Rashin Mansur Sulaiman Doguwa wani Rashi ne daHar Abada wanda wannan ahalin bazasu mantashi ba,kaf yaran ba wanda baisan labarin Marigayi Baba Mansur ba Daga bakin Daddynsu ba haka kuma Office dinsa da Dakin barcinsa makale da Hotunan Mansur din da suke Dauka Lokacin suna raye.
Mansur karami ya san ba Mastur ne ya Haifesa ba ammh kuma Bashi da maraicin wani bango
Rumana ce uwarsa har gobe Mastur Ubansu Diza kuma Anty take awajensa..!
*Tammat Bihamdullahi*
*Alhamdulillah nan na kawo karshen wannan Labarin nawa..Abunda na Rubuta Daidai Allah ya bani ladansa Kuskuran Dake ciki kuma Allah ya yafemin ina Godiya Masoya da kuka Nunamin kauna wajen Siyan Littafaina Allah ya saka muku da alheri Sai mun hadu a Sabuwar Shekara Cikin wata Tafiyar..!*
*Shakira*
*Janafty*
*Intelligent writer"s asso*
*23/12/2021*