← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 94

Sashe 19

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kai ya gyadaa mata yana Fadin"Ok..Bari na shiga na Fito.."Yafada yana wucewa Ciki ita kuma sai ta sauke idonta kan Karamin Frime din Dake kan Tv Stand din dake Falon Hoton Mastur ne da Mansur Mastur da Uniforms dinsa ajikinsa Ranar da aka bashi Rank din Zama Dcp ne,Abuja Mansur din yaje mai shine Sukayi Hoton Sun yi Bala'in kyau Mastur yana Rike da Kafadan Mansur Dukkansu Suna Dariya,Fararan Hakoransu a waje in ga gansu Zaka Fahimci Tsantsan kaunar juna atsakaninsu.

Hoton ta kurama Ido ko Kiftawa batayi Gabadaya Hankalinta ya tafi kan Mastur shi take kallo Lokaci Daya Tana Sakin Mirmishi Wani Shauki da muradi mai girma yana kara Shiga Zuciyarta Bata ma san Mansur ya Fito ba sai da Taji mganarsa sama sama yana cewa Tatashi su tafi Kasalance ta Mike tana gyara Mayafin kanta Kallonta yayi kafin ya Dan Dakata yana Fadin"Kash..Nayi mantuwa.."

Kallonsa Tayi Tana Fadin"Ai daman baka Rabo da mantuwa..me kuma ka manta..? Wayarsa yake Dannawa Loksci Daya yana Fadin"Ban kira Ya Mastur ba Diza..Kuma Duk Safiya Bayan su Baba dashi nake Fara mgana kafin na Fita.."Komawa Tayi ta zauna Ranta na mata Fari yau zataji muryansa Data kwana Tana Marari ba wata Shakuwa Tsakaninsu Shiyasa Take jin kunyar kiransa ammh Lokaci Bayan Lokaci suna Waya Dashi ta wayar Mansur,Abunda ke bata mamaki Kusan kullum sai ya Kira Daddy ko Mommy ta Ammh Ita bai Taba kiranta ba Ko Da sau Daya itama Bata Kiransa ba Saboda Bata san Tana ina Zata Fara ba.

Mansur ta kura ma Ido ganin ya kara bata rai Ido ta waro mai Tana Fadin"Ya ya dai..? Yana zama gefenta yace"Bai Daga kiran ba.."Ta rausayar dakai Tana Fadin"Kila yana Aiki ne..Kasan fa baya Hada aikinsa da komai Gwamna na ."

Bai samu Zarafin mgana ba Dayar wayarsa Kiran Samsung wacce Mastur ya siya musu iri Daya, ta fara Tsuwwa Ya Daga yana mgana Yan Siyasansu ne ya Dade yana mgama kafin ya katse Kiran Daidai Lokacin da Dayan wayar tasa Ta Dauki Neman agaji Tare da Shi Da Diza suka kai kallonsu kan Wayar sunan wanda suka gani ne ya saka kowannensu Sauke Boyayyiyar ajiyar Zuciya
Ya Mastur ne Baro baro yake Kiran Wayar Mansur da Sauri ya Dauki wayan ya Daga Cikin Shagwaba kamar karamin yaro yace"Nayi fushi ya Mastur..Ban kiraka ba kuma baka kirani ba Tun Safe..Na kuma kiraka baka Dauki kirana ba Mansur ne fa Mansur dinka Wanda baka da kamarsa.."

Yafada yana Tura baki,Diza kallonsa kawai take Tana yar Dariya sanin Halin Mansur Shi Haka yake Rayuwarsa mai Sauki ce,Hulan kansa Zanna Bukar ya Tura gefe Lokaci Daya ya saka wayar Speaker Daidai Lokacin da Mastur yayi Mirmishi Cikin Kayattaciyar Muryansa yace"Honourable Mansur Sulaiman Doguwa..Am Sorry Sir.."

Yanayin yadda yayi mganar sai da ta saka Diza Taji bugun Zuciya Mansur kuwa Baki ya washe yana Fadin"Kai ne Sir ai Yaya..Ya aikin..? Ka tashi lafiya..?kaci abinci..?kana wajen aiki ne..? Mirmishi kawai yayi Lokaci Daya yana Sagala wayar a kunnuwansa da Hannu Daya Dayan Hannun kuma yana Danna System dinsa Sargent Inuwa na Tsaye agefensa yana Jiran Umarni.
Cikin Sanyin sa yace"Oh..Wata Tambaya zan Fara amsaka Daga Ciki. ?

Mansur yace"Duka yaya Nidai.."Yafada yana Dariya yana kallon Diza Datayi Kasake Tana Sauraran Muryan da Bata gajiya da Sauraranta ko Jinta Mastur kuma Dagachan Bangaran Bai yi Dariya ba sai dai ya saki Fuskansa Cikin Dakiya yace"Komai Lafiya..Mansur Fatan kaima haka..? Yafada Kamar an sashi Dole Sargent Inuwa na Gefe aransa yana ayyana Duk Duniya banda wannan Dan"uwan yallabai bai mai sakashi mgana takai Goma Arana Ko da su bai taba gani ba ammh yasha jin wayarsu Yanajin yadda Mansur din ke yawan saka Ogan nasu mgana ko bai so ba

Mansur kuwa Daga Chan Bangaran ya tsike da Zuba yana gayamai Taron da zasu yi da Irin kayan da ya saka ya Karishe da Fadin"Yaya Mastur Shaddan fa Dana Tura maka Hotonta nasakafa..Diza tace nayi kyau Sosaifa ko nayi maka Hoto ne kagani..? Zamu yi Vidoe callne..?

Kansa ya Dafe kawai yana Dan Jizan Lebensa jingina yayi da Jikin Kujeran Dayake kai bayan ya Ture Computer din gabansa Da Hannu ya Nuna ma Sargent Inuwa Fayel din gabansa Har ya gane me yake Nufi da Sauri ya kame mai Lokaci Daya ya Dauki Fayel din ya Fice sai Lokacin Mastur yayi mgana yana Jan Numfashi saboda kiran Sunan Diza da Mansur yayi sai da Zuciyarsa ta amsa.

Cikin Sanyin Murya yace"A"a ina aiki ne Mansur..ammh nasan kanina mai kyau ne..Kowani kaya ya saka suna mai kyau.."Yafada yana Dan Mirmishi Mansur yace"Daz my Yaya ni kadai..Yaya when zaka zo ne..? Wlh muna kewarka Hajja Baba Aiya Mommy,Daddy Har da Diza Gata agefena.."

Mastur yaji gabansa ya Fadi Cikin Taushin Murya yace"Ok..Tare zaku Tafi Taron kenan..? Mansur ka Daina Zuwa da yarinyar nan cikin Taron maza fa Ita macece ka kiyaye Abunda nake gayamaka.."Ya karishe Kamar Kamar Zuciyarsa Zata Fito Saboda Takaichi da Kishi Sanin Halin Mansur din Da Diza yawo kamar sun ci kafar kare Last Month yaje Zaria bai kwana ba ko da yaje basa nan wai Suna Catering din Dizan Tun Safe Dagachan Mansur din zai je Taron su na Siyasa Zata Rakashi Saboda Takaichi ko Jiransu bai yi ba shi da Tawagarsa suka Dauki Hanyar Porthercourt Daman Abuja suka zo Sunyi Meeting da IGP na kasa.

Mansur ya kalli Diza itama Ta kallesa Tana Tura baki Abunda na Cimata Tuwo a kwarya Intaga yadda Mastur bai Damu da ita ba Ballatana Lamarinta Sai dai bai Chanza ba yana nan da Fadansa da Tsare Gidansa Data Sanshi Dashi Tuntuni.

Mansur yace"Ni ba Tare zamu ba..Catering dinta zata tafi Tana da aiki...Gata ma ku gaisa.."Yafada yana Tura mata Wayar gabanta Mastur yayi Saurin Bude idanuaansa jin Sallamar Diza Cikin Siririyar Muryanta Bai amsa mata Sai da ya Fara Kokuwa da Numfashinsa kafin yace"Kina lafiya..?

Daman ai gaisuwansa bata wuce haka tace"Lafiyata kalau ya aiki..? Kamar baya som mganar yace"Alhamdulillah.'Daga nan bai kara mgana ba sai Kokuwa yake da Numfashinsa itama sai ta kasa mgana Karban Wayar Mansur yayi yana Fadin"Wai Yaya Mastur Ita har yau Diza Bata Saki Jiki Dakai ba..Tsoronka Take ji Tun Lokacin ina ce mata kana Duka.."Yafada yana Dariya Mastur bai biye masa ba yace"Ka tashi ka tafi kada ka makara..Ka tuna ka girma yanzu kai ba yaro bane..Mansur din Baya Bashi bane na yanzu Honourable ne wanda Hakkin Jama"a Dadama ke kansa.."

Cikim kwamciyar Hankali yake mganar wanda duk wanda yaji Sai Muryan ta sakamai Natsuwa Mansur yace'Insha Allahu Yayana.."Mastur yace"Ina aiki ne..U took Later..Kada ka manta ka Kira Baba Sule ka gaishesa bana son in kara maka mgana Mansur ok..?
Da sauri yace"Allah zankirasa yaya.."Gud..yace Lokaci Daya yana katse Kiran.

Diza Datayi wani Sanyi da ita ya kallah yana Fadin"Bari na Kira Baba Sule kamar yadda yaya yace..kije ganin nan zuwa.."Bata yi musu ba ta mike Dauke da wayarta Sanin Da Tayi bazaiTaba waya da Mahaifinsa agabanta ba Bata san meyasa Mansur ba wata Jituwa ko Shakuwa Tsakaninsa da Yan"uwansa ta Bangaran Uba ba Duk ko da yadda Baba Sule ke yawan zuwa abaya ganin mansur din Yanzu ne ma ya Rage zuwa Saboda Shekarin sun ja,iyalai sun kara yawa da wasu matsalolin Rayuwa Har Mastur da Ba D'ansa ba yana Kiransa aka kai suna gaisawa,Shi haka yake kowa sai dai kaji yana yabonsa Haka Abba da Umma na Sokoto Suna ji da Mastur kamar Dan su na Cikinsu Kullun sai ya Kirasu sungaisa Yana da Kyawawan Hallayan Ga ita ne kadai bashi da kyawawan mu"amala.

Tana Fita ya Kira Baba Sulen suka gaisa Bashi da lafiya ne Typiod bai ma sani ba Mastur din ya Kirashi ya gayamai Baba Sule yace ma Mansur yaushe zaizo yace sai ya samu Lokaci nan yake gayamai Bikin kanwarsa Sakina ya taso..Kuma Auran Yayarsa Maryama ya kare Tana Gida Mansur yace sai ya samu Lokaci zai zo Insha Allahu Daganan suka Rabu ba wata Shakuwa Ballatana Fahimtar juna Baba sule Koda yaushe in ya Tuna sai yayi Hawaye Ba kowa bane Silan komai sai goggo Da yau Mansur a wajensa ya tashi Daya Tabbata Ya Fahimci acikin ya"yansa shi na Dabam ne.

Chan Shashen Su Hajja ya iske Diza Baba Habibu ya Fito,Daman sungaisa Tun Safe Zaman karyawa sukayi Dukkansu Aiya sai Tsokanarsa Take yana Ramawa ko Hajja Ta Tare mai Baba Dai na jinsu yana Dariya Yana gama karyawa yayi musu Sallama ya Fice Zuwa kasuwa Mansur ma bai jima ba ya Fita Domin Samarin anguwan da matasa sun Cika kofar Gidan Suna Jiransa Dakyar ya samu ya Fitar da Motarsa Saida ya sallamesu kana suka Raka Motarsa da sai kayi Gwamna Honourable Mansur Har Bakin Titi.

Diza kuwa Nan ta kai Har 12 suna Hira dasu Hajja kana ta baro Gidan Zuwa gidansu ta iske Daddy ya Fita sai Mommy Da Tayi bakuwa kawarta Hajiya Baraka wacce suke Business Tare,suna Zaune ne afalon Mommy na sama chan ta shiga suka gaisa kana taSauko ta Fada Dakinta wanka Tayi ta Shirya Cikin Doguwar Jallabiya ta yane kanta da Vail din Rigar Daman ita Duk kayanta Jallabiya ne Saboda Tana sonsu sosai,Takalminta ta saka ta Dauko karamar Jakarta ta Fito Ta Shiga Kitchen ta samu Mama Fadime na Girki tayi mata sallama Tace Zata wajen aiki,Daganan ta Haura sama Tayi ma Mommy Sallama ta kuma Karbi key din Motarta tace yau da ita Zata Fita.

Daga Gidan Direct Dogarawa ta wuce Tanayi Tana Duba agogon Fatan Dake Hannunta Bata so Tayi african Time koda ta ta samu Mutum Biyu na Jiranta,Rigar aikinta kawai ta Dora a saman Kayanta ta Fara aiki Daman sunyi mgana da Hauwa Ta wuce,So take tagama Ta Leka Cikin Catering Taga Abubuwan Dake wakana anan wajen.

_Albishirunku Masoyana wannan karan na bude muku wani Shashi na musamman Saboda ku..Ina masu Bukatan Atalla musu Hajarsu Ko wani iri ne Domin samun costumer ta ko"ina..? Ku garzayo kakarku ta kusa yanke saka Zan Tallata muku Hajarku a Duka Shafukana Domin inganta Sana"arku da kuma Samun Cinikaya mai Tsabta da kuma kara Hada hada wajen Masi siye da Siyarwa mai Bukatar A tallata mata Hajjarta Zata iya min mgana kai Tsaye ta wannan Lambar Tawa 09069067488 domin karin Bayani...Sai kunzo Kunsan dai mai kasuwa Shi ke da Riba.._
Chapter 19 · 0% Book details