← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 94

Sashe 23

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Juma ce ta Gabatar musu da Breakafast Saboda Ruma yasa Umma tasaka ta Shimfida Babbar Darduma Saboda in Tana Gida Bata son cin Abinci Saman Dining tafi son Ci kam Darduma a kasa,Nan aka Baje musu komai Rumana ta matsa Tace Tare da Juma da Goggo Jummai Zasu karya Umma bata Damu ba sanin Halin Rumanan Goggon jummai ce ke Baya Baya Juma dai ba Ruwanta Shirishirintanma ya Isheta Yan Garinsu Abbanta ne Daga Wamako Abba ya Dauko Goggo Jummai Domin ta Taimakama Umma Tun Tana da Karfinta Tazo Gidan Tun Ruma na karama akwai Shakuwa Sosai Tsskaninsu Kuma Ruman tana Daukanta kamar kakarta Ita ta sakaa mata ma sunan Goggo Jummai,Lokacin da karfinta ya kare ciwon kafa da Ciwon Baya sai Umma Dataji Dadin Zama da ita tace ta Dauko mata Daya Daga Cikin Jikokinta sai su Zauna Tare ita ta rika yin aiki,goggo Jummai Taji Dadin karamincin Su Umma Juma Jikarta ce Diyarta ta Fari ta Haifeta ta Rasu,ita Dauki yar Shekara 15 aduniya suna Zaune Tare Duk da Ciwon kafan Datake Fama Dashi Bata zama Haka batayi aiki ba komai na Bukatar Rayuwa Umma da Abba suna yi musu a yan"uwansu suka Daukesu ba masu aiki ba.

Tare Dukkansu suka karya Suna Hira suna Raha bayan sun gama Juma ta kwashe komai Zuwa Kitchen Goggo Jummai Tatafi Dakinta ta Dan kwanta ta huta suka bar Ruma da Umma anan Falon suna Hira Har wajen Azahar sai da aka Kira Sallar azahar kana kowacce Tayi Dakinta Ta gabatar da Salla,Rumana Barci ne a Idonta Sai kawai Tabi Lafiyan gado Ta kwanta Domin jiya Batayi barci ba kasawa tayi,Tana kwanciya Barci ya kwasheta Cike da Tunanin Mastur acikinsa.

Sai Bayan La"asar TaTashi Shima Sai da Umma ta Shigo ta Tasheta Tayi sallah Kana tatashi Tayi wanka ta Sauya kaya Zuwa Riga da wando na pakistan Daman yawancin kayanta kenan Bayan ta idar da Salla ne ta Bude akwatunanta Dama Daya na kayan sawanta ne Daya kuma na Littafan karatunta sai System dinta,System din ta Dauka Littafan kuma ta Xube su Kan gadonta Domin karatu Zatayi kamar Hauka irin karatun da masu wasa bane,Earphone dinta Ta Dauko ta Saka a wayarta Bayan ta saka Karatun alqur"ani ta Toshe kunnuwanta Ta Bude System dinta ta Fara Karatu bayan ta saka Sirrin Gilshinta mai kara Mata karfin gani Umma ta Lekota ganin tana Karatu yasa ta Kyaketa Ta yi Karatunta Rumana Bata Tashi Daga Karatunta ba sai da aka Kira Mangariba kana Tatashi ta Fada Tiolet ta Dauro alwala Tazo Tayi Sallah Ta Zauna Tana azkar Umma ta leko Tana gayamata Dawowar Abbanta Ko Hijabin Jikinta Bata Cire ba tabi Bayanta Tana Murna.

Afalon Sama ta gansa Rumgumeshi Tayi Tana Murnan ganinsa Shima Riketa yayi Cikin Farinciki,Yana Shafa kanta Gefensa ya Zaunar da ita yana Fadin"Rumana ya karatu..?

Shagwabe Fuska Tayi Tana Fadin"Ba Dadi Abba..Wlh Kamar zamu Haukace fa..Yanzu fa Bayan mun bar asibitin Cikin makaranta ne aka bamu Sati Biyu muyi Karatu kafin mu Fara Jarabawar Karshe.."Yana Shafa kanta yace"Masha Allah..I know my Dota..Zata iya da yardam Allah..Allah ya bada Sa"a Dr Rumana Muhammed wamako.."kanta yayi Girma da Kirarin Abban nata ta Washe Baki Tana Fadin"Nagode Abbana..Ina alfahari Dakai sosai kaida Umma.."Shima Mirmishin yayi mata yana Dafa kanta yace"Muma muna alfahari Dake Rumana.."Umma ce Dake jeramai abinci nan gabansa Take Mirmishi Nam Abba ya Sauko Da Rumana da Umma suka Hadu sukayi Dinner a sama Bayan sun gama Ruma ta kwashe komai Zuwa Falon kasa Juma ta karba Zuwa Kitchen Dakin Goggo Jummai ta Leka ta gaisheta,Ta isleta Tana kan Sallaya Tana Lazimi Bata wani Jima ba ta Koma Dakin Umman nata ta Zauna Gefensa suna Hiran su Sama sama Tana sska musu baki Cikin Farinciki yau gata ga iyayanta Masu Soyuwa Gareta.

Suna Cikin Hiran ne Wayar Abba ta Dauki kara Ya Dauko Ta Daga Cikin aljihunsa yana Ganin mai Kiran ya saki Mirmishi yana Fadin"D'anki Farida Mastur.."Umma ta Washe Baki Tana Fadin"AllH Sarki DCP zakace min Nima da Safe ya kirani ya gaisheni Yaron nan Wlh bantaba ganin mai Datttako irinsa ba Kamar wani Babba.."

Abba yace"Bari..Bari Farida..Yafada Lokaci Daya yana Daga Wayar Cikin Sallama Rumana Dake gefe Tayi Lambo ajikin Abba kamar bata jinsu nan kuwa Gabanta ne ke Fadi Kiran sunan Mastur kadai da Abba yayi yasa Jikinta ya saki Ta Tuna Ta Turamai sako ammh Bai Kirata ba Daman baya Kiranta sai in ita ta Kirashi baya Daga Kiranta zai bari ta yanke ya Biyo baya Tana ji suna mgana da Abba yana gayamai ta Dawo Gida Daganan aka Bama Umma suka gaisa sai kuma Sukayi sallama.

Umma ta kada kai Tana Fadin"Iyayensa sun yi Dacen D"a..Wlh Ina Sha"awarsa..Babu Ruwansa akwai Hankali da Tarbiyan gashi dai bashi da yawan mgana Ga shi ba wani Babba ba sai Halin Girma.."Abba ya Jinjina kai yana Fadin"Ai Alhaji Sunusi yace Sak Hallsyansa Ubansa ne..Haka Mahaifinsa yake Baba Habibu.."Umma tace"Ai har Mahaifiyar tasa..Hajja ai akwai kawaici da Halin Girma.."duka Hiran nasu na Yabon Mastur ne Tana Jinsu Batace komai ba Sai da Abban ya kalleta yana Fadin"Rumana kinyi Shiru baki ce komai ba..? Kina kiran yayan naki kuna gaisuwa kuwa..?

Kai ta gyada Tana Fadin"Eh Abba.."Mirmishi yayi yana Fadin"Allah yayi miki albarka..Babanki na Zaria nata Cigiyanki yaushe zaki mai Hutu ki kwana Biyu.."Rumana Ta muskuta Tana Fadin"Abba sai na Gama Exams na Dawo Gida kafin na Fara Intenship.'Umma tace"Yadai kamata kam Ruma..Hajiya Asiya ma Tagaji Da min Magiyan yaushe Ruman Zataje Suna Daga Kafa ne saboda Karatunta.."

Abba yace"Zataje Tayi Musu Hutu Insha Allahu Koma kije Chan Asibitin ABU Kiyi Intenship Dinki ko Service dinki.."Rumana ta Dago kanta Tana Fadin"Abba sai inda na Samu fa..Sai anyi Exam duka zan je nayi in na samu Shikenan.."Umma tace"Zama ki Samu..ko nan Sokoto ko Chan Zaria Duk inda kika samu duk Gidane..'Rumana bata kara mgana ba Abba ne yace"Kuna waya ko da yar"uwanki Diza..? Kinsan Ta Bude Wajen Makeup da Snaks,..?

Rumana Tace"Eh Abba...muna Taba Chart da ita sama sama..Ina kuma Following dinta Duka Social medianta Ina ganin posting din abubuwanta na Tayata Murna Abba sai dai Why Taki Karatu..?

Umma tace"Bata Ra"ayi ne Rumana..Ba gashi kuma Allah yasa ma Abun albarka Hajiya Asiya na gayamin irin Ficen da Dizan Tayi a Chan Zaria da kaduna.."Abba yace"Sosai ma..Kowa fa da hanyar Cin Abinsa baka ga Mansur ba Dan Wajen Shi Habibun Daya ke Riko .Kamar waasa Siyasa Ta zama Hanyar Cin Abincinsa.."Umma tayi Dariya Tana Fadin"Honourable kenam..Shi kuma ai dan Barkwanci ne ko Wasa da Dariyansa yaci a Zabesa...Abokin Diza kenan Tun na yarinta.."

Rumana Duk Tana jinsu Bata ce komai ba Ganin Ta gundura da yin Hiran yasa ta Tashi Tana Fadin"Umma Da Abba..Sai da Safe Zanje nayi karatu na kwanta.."Sukayi mata sai da Safe Kana ta Fice Zuwa Dakinta suka Bita da kallon Sha"awa.

Wanka ta sakeyi tayi Sallar Isha"i kana ta saka Kayan Barci Tazo ta Hau gado Duk yadda Taso Tayi Karatin ta kasa Saboda Tunaninsa,Shiyasa wani Lokacin bata so Tunaninsa yazo mata Sai ya Hanata Sukuni wani Lokaci sai ta maida kanta Kullum Cikin karatu Saboda kaucema Tunaninsa Sai dai yau yaci karfinta Kowa yabonsa yake..Kowa Sonsa yake saboda kyawawan Hallayansa Ture Littafan gabanta Tayi ta Jawo Wayarta Ta Lalubo Lambarsa Data sakama Emoji na Zuciya da makulli ta Dokamai kira.

******

Fitowarsa Daga wanka kenan Daure da Towel a kugunnsa Jikinsa Duk yana Digan Ruwa Daga kan gadon da wayoyinsa ke Zube yaga Babbar Tana Haske a Silent ya sakata kafin ya Shiga wanka.

Karisawa yayi kusa da wayar ganin Sunan Rumana yasa ya Dafe kansa bai Daga Kiran ba Sai da ta katse kana ya Dauko Wayar ya Shiga wajen Sako ya Fara Mata Rubutu.

*Me kike yi baki kwanta ba Har yanzu Rumana..? Akwai Exams agabanki..ya kamata by Now kin kwanta saboda kwalkwawarki ta zama Fressh Abunda kika Karanta ya zauna Miki..Kada ki Damu ki kwanta u Took in d Mrning Gud Night..*

Daga Haka ya Tura mata Lokaci Daya ya Maida wayar saman gado ya isa gaban Madubin Dake Dakin ya Fara shafa Lotion,sai da ya gama kana ya isa gaban wardrope din Dake Dakin Cikin Hanger ya Dauki Jallabiya ya saka yunwa yake ji Silafas dinsa ya Zura ya Fita Zuwa Kitchen ya manta bai yo Takeway ba kafin ya Shigo Gida kuma ya Kira Wani Sargent din Kamar Shiga Hakki ne.

Kitchen din Dake Cikin Apartmemt din da gwannati ta bashi yake zaune ya Shiga gas ya kunna ya Dora karamar Tunkunya ya saka Ruwan Zafi Yana Zafi ya kashe Gas dim ya Fito Falon Dayake Babba yaji kujerun alfarma wajen Dinning ya Nufa inda kayan Tea suke ya Hada nan ya Zauna yasha kadan bada yawa ba ya Ture kofin ya Mike Zuwa Falom kan Daya Daga Cikin Kujerin Falon ya Zauna ya Dauki Remot yana Sarrafa Tibin Dake kunne Tun Fitowarsa..

Tashar NTA Ya kamo yana kallon Labarai Cikin Harshem Turanci kansa ya maida Saman kujeran ya Jingina Lokaci Daya yana Dora kafa Daya kan Center Table din Dake Tsakiyar Falon ya Rage ma Idanuwansa Karfi Kamar mai jin Barci nan kuwa Duka Hankalinsa na kan Abunda yake kallo ne.

*Kuyu hakuri da jina Shuru da kuke yi..Wlh na Shiga wata Sabgace Biki gareni Dis week Shiyasa Posting din zai zama sai Lokaci bayan Lokaci ammh da Zarar an gama Biki Lafiya da yardan Allah zamu dawo mu Dora Insha Allahu,Sannan Zaku cigaba da Payment din kudin Karatun Sadaukarwar so Ina maraba daku Masoyana sai kunzo..Nagode..*

_Albishirunku Masoyana wannan karan na bude muku wani Shashi na musamman Saboda ku..Ina masu Bukatan Atalla musu Hajarsu Ko wani iri ne Domin samun costumer ta ko"ina..? Ku garzayo kakarku ta kusa yanke saka Zan Tallata muku Hajarku a Duka Shafukana Domin inganta Sana"arku da kuma Samun Cinikaya mai Tsabta da kuma kara Hada hada wajen Masi siye da Siyarwa mai Bukatar A tallata mata Hajjarta Zata iya min mgana kai Tsaye ta wannan Lambar Tawa 09069067488 domin karin Bayani...Sai kunzo Kunsan dai mai kasuwa Shi ke da Riba.._
Chapter 23 · 0% Book details