← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 71 OF 94

Sashe 71

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 7 min read

Cikin kasala dayake jin ya sameshi Lokaci Daya ya Jawo Wayoyin ya Bude su,sai da suka gama Daidaita Network kana personal Phone dinsa tayi alamun Shigowar Sako ya Dagata yana Dubawa Jerin mutanen da suka Nemeshi ne, saboda wayarsa irin mai nuna mai Duk wanda ya Nemeahi bai samu bane,Abunda ya Bashi mamaki Shine ganin Abba ya nemeshi,Baba Habibu,Daddy,Baba Sule,Ruma,sai yaji Jikinsa bai Bashi ba ganin bai ga kiran Mansur ba Alhalin da Asuban nan ma sai da sukayi mgana yace zai kirashi da Safe su karisa mgana kan yadda Zasu kai iyayansa Sauke Farali wannan Shekaran
Bai gama mamaki ba yaji Shigowar Sako daga Rumana Jikinsa na rawa ya Shiga ya Bude Abunda ya gani ne yasa ya mike da Sauri bai Shirya Lokaci Daya yaji Zuciyarsa na Duka da karfi da karfi.
Bai tsaya ba ya kwashi Wayoyinsa ya Fice daga Office din,yana Fitowa ya Hadu da Sargen Inuwa Cikin bada Umarni yace"Sargent Dauko Mota ka kaini Filin Jirgi..Zaria Zani Now.!
Sargent inuwa yayi mamakin wannan Gaggawa sai dai ba"ayi ma oga Gardama

Da Uniform din Dake jikinsa da wayoyinsa,gidan Dayake Zaune kadai ya shiga ya Dauko Atm dinsa da Walet dinsa Daya manta da Safe bai dauka ba ya Fito ya Shiga Mota sai Filin Jirgi Abunga ga Masu fada aji kuma abu in aka ce maka akwai Naira nan da nan komai ya kamallah ko Awa Daya Mastur bai yi a Filin Jirgi ba Jirgunsu ya Daga Zuwa Kaduna da Misalin karfe 11:30am Hankalinsa kwata kwata ba"a kwance yake ba Shiyasa bai yi Tunanin kiran wani ba suna Shiga Jirgi ma kuma ya Kashe Duka Wayoyinsa sai dai kuma Tuni Zuciyarsa ta Daina Bugawa Daidai yana ji ajikinsa Tabbas wani Abu na Faruwa mara dadi a Zaria.

*Shakira..*
1/1/22, 18:55 - Maryam Badmsi: *SS....33*

*Ki biya ki karanta cikin Aminci da Salama 09069067488*

"Yadda suka ga Rana haka suka ga Dare,Mastur bai Runtsa ba Duk Tsawon Dare hakama su Baba Habibu su Diza kuwa Daga cikin gida ba mgana Barci sai dai Barawo ya iya sace Daidai ku Daga Cikinsu,Domin zukata Tuni sun gama raunana,Kuka ya bar Fito musu sai Jiki da Zuciya ke ta Faman Turiri da Zafi Dacin Rashin da sukayi mai Girma atare dasu.

Washegari ma haka ma Mutane basu yanke ba sai zuwa suke kamar ba gobe Mastur bai yi mamakin ganin Abokan aikinsa sun zo mai gaisuwa basanin Kaninsa Sananne kuma Mutuwar ta Zaga Duniya Harta da Headquater su na Porthercourt sun zo mai gaisuwa sai ga Abokinsa Acp Saleem kumo da Matarsa Hajiya Malika sun zo ma Mastur gaisuwa ba Shakka yaji Dadi sosai nan da nan akayi ma Malika iso Cikin gida wajen su Diza,Duk Ba wanda yasan ta a ido ammh Suna jin Labarin Saleem kumo abokin Mastur abakinsa.
Malika ta Tsausayama Diza sosai da Rumana Duk sun Fita Hayyacinta Dayake daga ita sai Saleem din sukazo ta bar su Hajiya wajen Ummi suna Abuja Tayi amfani da Iliminta ta Rika Lallashin Diza da Rumana da kalamai na kwantar da Hankali Tana musu misali da Ranar data Rasa Mahaifinta da irin Tashin Hankalin Data shiga sai gashi Dalilin gwarzom Mijinta gashi yanzu bata Cikin wani Rashi Da Damuwa ssi ma Godiya Allah Datake yi.
Rumana ce kadai ta Fahimceta banda Diza da take kallon kasa kawai batare data Motsa ba Tun Jiya bayan an kai Mansur gidansa na Gaskiya Diza bata kara mgana sai dai ta kan amsa gaisuwa in anyi mata Kowa yazo ya ganta sai ya Tsausayamata Da kuma Addu"an Allah ya Sauketa Lafiya.
Sai washegari Saleem kumo da Matarsa Malika suka koma Cike da Tsausayin Mastur da Ahalinsa.
Tunda akayi Rasuwan Gidajen Biyu suke Cike da Jama"a wasu na Zuwa wasy na Tafiya Lalle ya Tabbata Mansur mai Jama"a ne kuma mai Mutane,Sun ga Zahiri Lokacin da kasa ta Rufe idanuwansa kuma Duk wanda yazo Alherinsa yake Fada ba wanda ya Taba ganin Abokin Fadansa Mus"ab ma yazo Shi da Iyayansa Yayi kuka sosai kamar Ransa zai Fita yaje har kabarin Mansur yayi mai addu"a sai Ranar da akayi uku suka koma Sauran Bakin maruka da yan Ririwai da sukazo kuwa wasu Ranar Shida wasu kuma sai da akayi addu"an bakwai wasu kuma Sai Washegari kamar sun kannen Mansur Sakina da maryama da mariya masu Auran sai Inna Zainaba da Matan yayyin Baba Sule dashi kanshi da Sauran yan"uwansa Duk aranar suka Koma,Sun yi kuka kamar Ransu zai fita sai Mutuwar ta Dawo Tamkar Sabuwa aranar Washegari Ranar takwas Umma da Abba suka koma Dayake duk yan uwansu na Tureta dana wamako duk sunxo gaisuwa Mota Guda da yan Gidansu Mommy Tun Ranar da akayi uku suka zo suka koma
Har Inna karime da iyalanta Ranar ta koma gida duk ya watse Daga Rumana sai Diza sai Mardiya dasu Hajja Mommy ma ta koma Gida sai dai nan take Wuni Waje kuma Daddy ne kadai ke karban gaisuwa Dayake Mutane na Zuwa Jefi Jefi.
Zuwa Lokacin Mutuwar ta Gama shiga Jikinsu Sun Riga sun Tabbatar da Mansur ya Tafi ya barsu har Abada kowa kagani ya Rame yayi Dan wuya Barin ma Mastur da Diza tamkar basu Taba Fuskantan wani Farincikin acikim Rayuwarsu ba gwara Mastur yakan sha Ruwan Lipton arana ita kuwa Diza sai anyi Daga da ita da Mommy najan Ido kama take yarda ta saka wani Abu acikinta bata Damu da Wani Hali Abunda ke Cikinta Zai Shiga ba kawai taji aranta Tafi kaunar itama ta Mutu tabi Mansur Chan da Zamanta a wannan Duniyan.

Ranar da Mansur yayi kwana Goma da Rasuwa duka Kafafuwa suka Dauke Baki da Nesa Dana kusa sun gama komawa Gidajensu Lafiya da Fatan Allah ya Jikan Mansur yayi mai Rahma Akuma Ranar ne Dadaddre bayan Sallar Isha"i Dukkansu suka Zauna afalon Hajja,Daddy ne ya Bude Taron da addu"a Bayan Doguwar addu"an da sukayi ma Mansur da Fatan Dacewa kana Daddy ya gangaro kan makasudin zaman nasu Nasiha kan yarda da Kaddara da kuma Tunatarwa cewa Allah Dayane kuma Mutuwa Zahiri ne inda Mansur yaje chan Zasu je suma Yayi Nasiha sosai Hakama Baba Habibu ya Dora da nashi,Diza Hawaye kawai take Zubarwa hakama Rumana da Mardiya Ayya kuwa Daman ta koma Shuru Shiru Mutuwar ta Tabata sosai Mastur na Gefe Yana Nazarin Diza gabadaya yaji Duk Duniya ba abun Tsausayi irin Diza Ko Shekara basu yi da aure ba Mansur ya Tafi ya barta da Cikinsa Shi kuwa yayi alkawarin Sai inda karfinsa ya kare wajen ganin ya Inganta Rayuwar Diza da Abunda Zata Haifa Bazai Taba bari Tayi kuka ba.
Hajja ma na gefe Tana Sharan kwallah Ita Uwa ce..Kuma Shakikiya wajen Mansur ta Shaku Dashi Kamar Danta Tunda ta Shayar dashi da Cikinta,Dole tayi kukan Rashin Shalelen Danta wanda bata da Kamarsa,Kafin a tashi wannan zaman anyi mganan Kan A ina Dixa zata zauna Har ta Haihu..?Cikin Sauri
Mommy ta Nemi da Zata Tafi Diza ta zauna wajenta ta kula da ita Har ta Haihu,Ba wanda yayi gaddama kowa yayi Na"am Sanin Halin da Dizan take Ciki Uwa ce kadai Zata iya Juriyan Da ita da kuma Kula da ita Daga karshe Daddy ya Umarci Mastur ya Dauki Matarsa Rumana su koma Gidansa yau din Ba yadda ya iya Illa Bin Umarinsu a Koda yaushe rumana ta Rumgume Diza tana kuka sai da Mommy ta Rabasu,sai da ta raka Diza da Mommy Gida Har Dakin Dizan kana ta Dawo suka Tafi gida ita da Mastur Cike da Tsausayi da Wani Acikin Zuciyarta na Tsausayin Diza da Mastur suna Zuwa gida Megadi ya Fara musu gaisuwa Mastur kadai ya amsa Rumana kuwa Haraban gidan Take kallo Tana ganin Motocin Mansur dake wajen guda 3,gata Diza itama Guda uku ta juya ta Kalli Shashensu sai kuka ai da Gudu ta Shige bata ma Jira Mastur din ba,Shima a wannan Lokaci Wani kafada yake nema inda Zai yada kansa yayi kukan Rashin Dan"uwanasa,ammh bai Samu ba.
Shima cikin gidan ya Rufa mata Baya kai Tsaye Dakinsa ya wuce,Yayi wanka ya Sauya kaya ya koma ya kwanta yana ganin kamar abun mafarki ne yau wai ba Mansur ya Tafi ya barsu Tafiya na Har Abada
Yafara Tunanin Rayuwa ba abakin komai bawa yake ba yau kana Raye gobe baka Ya Tuna yadda suka Turbune Mansur acikin kasa Dagashi sai Halinsa sai Allah,Me zai ce ma Allah in ya Mutu yau..? Wani amsa Zai bama Allah in ya Tuhumeshi da Rashin Sauke Nauyin Rumana Dake kansa..! Bashi da wani Uzuri Ballatana wani abun cewa ya kamata yaji Tsoron Allah ya gyara Lahirarsa kafin Shima yau ace ya bar Gidan Duniya.
Wannan Tunanin yasa ya Tashi Zumbur ya Fada Tiolet ya Dauro Alwala,yazo ya sauya Jallabiyan Jikinsa zuwa wata Mai ruwan Madara bata da Tsawo sosai Turare ya Fesa kai Tsaye ya Nufu Dakin Rumana da yakini da Niyyar gyara komai Shi kansa bai san meyasa Zuciyarsa keJansa ba sai dai kawai ya san Shi din Abun Tsausayi ne
Chapter 71 · 0% Book details