Sashe 45
Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 7 min read
Suna Shiga Falon Mus"ab ya zauna kan Daya Daga Cikin kujerun Falon Shi kuma Mansur ya Taka ya Shiga Bedroom din Daya Hangi Haske domin akwai Wutan lantarki Haske ya gama gauraye ko"ina,yana Tura Kofar yaga ta Bude ya Tura kai ya Shiga Da Sallama asaman Bakinsa.
Cak ya Tsaya ganin Diza zaune kan gado ta hada kai da gwiwa Tana ta Rafzan kuka kamar wacce akace uwarta ta Mutu Da Sauri ya Karisa kan gadon yana Fadin"Subhanallah...My Firstlady ya da kuka haka..? Yafada Lokaci daya yana Cire Takalmin kafarsa ya Haye kan gadon lokaci Daya ya Tarairayota Zuwa jikinsa cikin Tashin Hankali,Dago kanta yayi da Fuskarta ta gama Damewa da majina da Hawaye Cikin Matsancin Tashin hankali ya Tallabo Habanta yana Fadin"Meya Faru ne..? Meyasa kike kuka..? Baga ni ba..? Kin manta i promise u indai ina Raye sai kin fi matar gwanna jin Dadi da Rayuwa mai yanci.."Yake Fada yana Share mata Hawaye da Hannuwansa Diza sai taji jikinta yayi sanyi Meza tace..? Tunda aka Fara mganar auran nan Mansur bai taba Bata ransa ba..Koda tace bata sonsa yayansa take so ba ta ga ya Sauya mata ba Kullim Sai dai ya Farantamata Koda bazata Godemai ba Tun suna yara Mansur mai Hidima gareta ne Balle yanzu da ta kasance matarsa Tana Matukar Tsausayamai Rayuwarsa Cikin Sauki da salama ko abokin Fada bai dashi bata Taba ganin Fushin Mansur ba Mutum ne nagari mai Hakuri da kawaici Wanda take kuka Domin sa bai san Tanayi ba da bakinsa yace baya sonta Yana chan da matarsa,Meyasa Zata zo Tana kuka Domin ta bata ma wanda ke matukar sonta rai..? Da wannan Tunanin Tayi Saurin Saka Hannu ta riko Hannuwansa Tana Fadin"Ina kukan Rabuwa da Mommy ne da Daddy..'Mirmishi yayi yana kallonta Cikin Begen so da kauna yace"in wannan ne baki da Damuwa..in kullum kike son Zuwa Kiga Mommy da Daddy nayi miki alkawarin bazan gajiya ba.."yafada Lokaci Daya ya Sakarmata Idanuwansa Cikin kallon Sha"awa da muradi mai girma Diza da taji kamar ta Suma Saboda kukan Dake cin Ranta kawai ta Fada jikinsa ta kamkameshi ta Fashe da kukan Takaichin Zuciyarta da bata son wannan bawan nata sai Damuwa da wanda bai Damu da ita ba.
Yana jinta Tana kuka ya kara Rumgumeta yana lallashimta Cikin Dadaddan kalamansa Har ya samu Tayi Shuru Tana ajiyar Zuciya,Dagota daga jikinsa yayi ta kara makalewa Dariya yayi yana Jin karan wayarsa Dake Cikin aljihunsa yace"Mus"ab na Falo yana jirana fa My Firstlady..."Dago Jajayen idanuwanta tayi Tana Fadin'Tare kuka zo..? Yana shafa Bayanta yace"Eh Da Yaya Mastur kinsan ba abokai ne dashi ba..Ya wuce Shashensa ni kuma Mus'ab ya Rakoni Sagir ma yayi gida.."Tunda ya ambaci Mastur Tayu Dif da ita sai taja jikinta ta koma Gefe Ta kwanta Tana Sauke Numfashi mikewa yayi yana Gyara Rigarsa data Fara Yamutse yace"Zaki samu Fita ku gaisa ko sai gobe..?
Kai kawai ta gyada mai kafon tace"Nagaji..Banma son Tashi."Tafada Cikin Sanyin murya bai Damu ba ya juya yana Fadin"Bari naje na sallameshi.."Daga haka ya Fice ta Rakashi da ido Cikin Taruwan Hawaye.
Mansur na Fita Mus"ab ya balbeleshi da masifa wai ya Shanyashi Shi dai Hakuri kawai yake bashi yana Dariya Sallama sukayi bayan ya gayamai Dizan bazata samu Damar Fitowa ba Karamin Tsaki Mus"ab yaja kawai ya wuce Mansur ya bashi key din Motarsa ya koma da ita Saboda Dare har Haraban Gidan ya Rakasa saida yaga Ficewarsa Daga gidan kana ya koma Ciki.
Shi kanshi a gajiye yake barci yske son yayi ya Huta Domin yafi Sati baya samun wani Ishashen Barci,Dakyar ya Lallashi Diza ta shiga Tayi wanka yaje Kitchen ya Dauko Filet da kofuna sai fork,Yazo ya Saka Kazan a Filet ya bita dashi Har kan gado yana bata tana amsa Dakyar,Ya matsa mata taci ne saboda yasan tana jin yunwa Kadan taci ya bata madaran Tasha ta koma ta kwanta,Shi ya karishe sauran kazan ya Danna da madara Sauran kuma ya kai kitchen ya saka Cikin Fridge ya Dawo Falo ya Dauki Jakar kayansa ya Shiga Ciki ya Samu Diza kwance acikin Bargo Idanuwanta a lumshe bai mata mgana ba ya Fada Tiolet yayi wanka Koda ya Fito Barcin gajiya ya kwashe Diza Bata sani ba,Mirmishi kawai yayi ya Bude Jakarsa ya Dauki kayan barcinsa Riga da wando ya saka ya Fesa Turare ya Shinfida Darduma yayi Shafa"i dawuturi Dakyar kamar ya Kifa Falo ya Fita ya RarrageHasken wajen kana ya Dawo Ciki ya Rage Hasken Bedroom din ya kunna Dumlight,Kan gadon ya Hau Lokaci Daya yana Jawo Diza jikinsa wacce ke sanye da Daguwar Rigar barci mai Taushi,Daman barcin ya kwasheta da Fargaba ne,Tana jinta ajikinsa Tayi Saurin Zabura Riketa yayi yana fadin"Relex..Babu abundaa Zan yi miki kwanta kiyi barcinki..Nima gajiya bazata barni na iya Moranki Dakyau ba.."Yafada yana Raban Wuyanta wani yamm taji acikin Jikinta ammh Ta kasa Motsi Tama jinsa ya kara Rumgumeta Bisa Kirjinsa yaja Bargo ya Rufesu yana Sauke Numfashi Lamo Diza Tayi Tana Shakam Kamshin Turaransa Tunani na neman Shigo mata Yasa Tayi Saurin Kiran sunan Allah Saboda yadda suke agajiye yasa basu wani jima ba Barci ya kwashe su Dukkansu.
Bangaran Mastur Rumana dai ba haka Tagani Domin Har Mastur ya Shigo Gidan nan bata sani ba,ba Dakinta ya Fara Shiga ba Dakin kusa da nata ya Bude ya Shiga shima agyare yake Tsab nan ya Sauke kayansa Domin bai yi Tunanin Fara Rayuwa da wata a Daki Daya ba Sai da ya Shiga yayi wanka ya Saka Wata Jallabiya mai Ruwan Madara Shafa"i da Wuturi yayi Ya Dade Zaune yana Tufka yana Warwara kafin ya Mike Cikin Sanyin Jiki ya Fita Zuwa Falon Lokaci Daya yana karema Falon kallon aransa yake fadin Nice Ledan kazan Daya ijiyeta nan Saman Dinning ya Dauka ya Nufi Dakin Rumana yana Addu"a da Fatan Allah yasa Tayi barci sai addu"ansa bata ci ba yana Taba Kofar ta Bude Daman an Dan Sakayata ne sai ga Rumana Zaune kan Tsakiyar gadonta Taci kuka ta Koshi Har ta Dago Fuskarta Tana kallon Kofa Sai gashi sun Hada Ido Hudu da Mastur Dake Tsaye da Leda ahannunsa,Mamaki ya kamata Bayan ta Sauke Numfashi Ita nata angon da Shigar Jallabiya zai Shigo mata..! Da alama ma ba yanzu ya Shigo Gidan ba.
Shi kuwa Mastur saurin Karisowa Cikin Tsakiyar Dakin yayi yana kaucema Idanuwan Rumana Gefen gadon ya Zauna kamar wani mara gaskiya ya Dora mata ledan kazan kan gadon agabanta Cikin mamaki Tabi ledan da kallo kafin ta Sadda kanta kasa Tana kara jan mayafinta Shuru shuru yana Zaune bai ce mata komai ba Ganin haka yaasa ta Muskuta Tana Fadin"Ina wuni..!"
Dakyar ya iya Bude baki ya amsa mata Cikin wani irin kasala,Dif kuma yayi ya kasa mgana Domin bai sam ta ina Zai Fara ba itama sai tayi Shuru gabanta na Faduwa Wajen kimamin minti goma Sha Biyar ya mike tsaye yana Fadin"Kici kafin ki kwanta..Sai da Safe."Daga haka bai jira cewarta ba ya juya yana Tafiya kamar zaiFadi Rumana ta bishi da kallo,baki Bude har ya Fice Saboda mamaki,Daidai Karar Rufo Kofar da yayi daidai Zubar kwallarta Sai yanzu ta kara yarda Mastur baya sonta..Domin Angon adaran Farko Doki da Zumudin Amaryansa yake ammh ita ba wani kulawa ba Tattali ba mgana mai Dadi,yadda take karantawa a Littafan Hausa da Turanci Daran Farko Kazan amarcin ma Ango ke lallashin Amaryansa Tana ci kauda kai Tana bata rai yana bata abaki ammh ita anata barayin ba Haka yake ba Dakyar ma angon nata ya Shigo wajenta ya Tura mata Ledan kaza yace taci Kafin ta kwanta Daganan ya Fice abunsa ya barta Bayan yayi mata Sallama kemsn Ita kadai Zata kwana Adaran Farkonta Angonta ya Raba makwanci da ita wannan wani irin Rana ce Gareta,Sai kuka Haka Rumana ke kuka Kamar ranta zai Fita Tagaji ne ta Mike ta Rarrafa Ta Shiga Tiolet tayi alwala ko wanka Bata iya yiba ta zo Tayi Sallar Isha"i da batayi ba Tana jin yunwa kwarai Domin Rabonta da wani abincin Kirki Tun Breakfast din da sukayi agidan Daddy ammh bazata iya cin komai ba Saboda bakinciki Ture ledan kazan Tayi kasa ta Kudundune akan gadoTana Cigaba da kukanta ko kayan Jikinta bata cire ba,Ta kwanta Bata san iya adadin Lokacin Data Shafe Tana Kuka ba da Tsausayama Rayuwarta Bata san Lokacin da barci ya kwasheta ba.
******
Washegari Bangaran Diza da Mansur sun tashi Cikin Farimciki Domin Diza Tana ganin Soyayyah da Tattali wajen Mansur wanda yayi Sanadiyar goge Duka kukanta,Sai dai kawai ta Rika Binsa da ido Tana addu"an Allah ya Dora mata kaunarsa ya Cire mata son wanda baya sonta.
Daga gidan Daddy aka aiko musu da Breakfast,Kwando Biyu Mansur Daya Mastur Daya,Dukkansu mazajen su suka Fita suka amsa Bayan Mommy ta kirasu ta sanar dasu ga abun karyawa nan zata aiko Dashi,Mansur shi yayi komai ya Lallaba Diza yayi mata wanka ya Sauya mata kaya shima yayi wanka ya sauya kaya,suka Fito Falo ya Zuba musu abun karyawn Tana kan Cinyarsa yana bata abaki Tana kauda kai yana Lallashinta Har taci ta koshi kana shima ya samu yaci ya koshi Daganan ya Dauketa suka Koma Cikin Bedroom suka kara Nannadeawa suka koma Barcin gajiya.
Cak ya Tsaya ganin Diza zaune kan gado ta hada kai da gwiwa Tana ta Rafzan kuka kamar wacce akace uwarta ta Mutu Da Sauri ya Karisa kan gadon yana Fadin"Subhanallah...My Firstlady ya da kuka haka..? Yafada Lokaci daya yana Cire Takalmin kafarsa ya Haye kan gadon lokaci Daya ya Tarairayota Zuwa jikinsa cikin Tashin Hankali,Dago kanta yayi da Fuskarta ta gama Damewa da majina da Hawaye Cikin Matsancin Tashin hankali ya Tallabo Habanta yana Fadin"Meya Faru ne..? Meyasa kike kuka..? Baga ni ba..? Kin manta i promise u indai ina Raye sai kin fi matar gwanna jin Dadi da Rayuwa mai yanci.."Yake Fada yana Share mata Hawaye da Hannuwansa Diza sai taji jikinta yayi sanyi Meza tace..? Tunda aka Fara mganar auran nan Mansur bai taba Bata ransa ba..Koda tace bata sonsa yayansa take so ba ta ga ya Sauya mata ba Kullim Sai dai ya Farantamata Koda bazata Godemai ba Tun suna yara Mansur mai Hidima gareta ne Balle yanzu da ta kasance matarsa Tana Matukar Tsausayamai Rayuwarsa Cikin Sauki da salama ko abokin Fada bai dashi bata Taba ganin Fushin Mansur ba Mutum ne nagari mai Hakuri da kawaici Wanda take kuka Domin sa bai san Tanayi ba da bakinsa yace baya sonta Yana chan da matarsa,Meyasa Zata zo Tana kuka Domin ta bata ma wanda ke matukar sonta rai..? Da wannan Tunanin Tayi Saurin Saka Hannu ta riko Hannuwansa Tana Fadin"Ina kukan Rabuwa da Mommy ne da Daddy..'Mirmishi yayi yana kallonta Cikin Begen so da kauna yace"in wannan ne baki da Damuwa..in kullum kike son Zuwa Kiga Mommy da Daddy nayi miki alkawarin bazan gajiya ba.."yafada Lokaci Daya ya Sakarmata Idanuwansa Cikin kallon Sha"awa da muradi mai girma Diza da taji kamar ta Suma Saboda kukan Dake cin Ranta kawai ta Fada jikinsa ta kamkameshi ta Fashe da kukan Takaichin Zuciyarta da bata son wannan bawan nata sai Damuwa da wanda bai Damu da ita ba.
Yana jinta Tana kuka ya kara Rumgumeta yana lallashimta Cikin Dadaddan kalamansa Har ya samu Tayi Shuru Tana ajiyar Zuciya,Dagota daga jikinsa yayi ta kara makalewa Dariya yayi yana Jin karan wayarsa Dake Cikin aljihunsa yace"Mus"ab na Falo yana jirana fa My Firstlady..."Dago Jajayen idanuwanta tayi Tana Fadin'Tare kuka zo..? Yana shafa Bayanta yace"Eh Da Yaya Mastur kinsan ba abokai ne dashi ba..Ya wuce Shashensa ni kuma Mus'ab ya Rakoni Sagir ma yayi gida.."Tunda ya ambaci Mastur Tayu Dif da ita sai taja jikinta ta koma Gefe Ta kwanta Tana Sauke Numfashi mikewa yayi yana Gyara Rigarsa data Fara Yamutse yace"Zaki samu Fita ku gaisa ko sai gobe..?
Kai kawai ta gyada mai kafon tace"Nagaji..Banma son Tashi."Tafada Cikin Sanyin murya bai Damu ba ya juya yana Fadin"Bari naje na sallameshi.."Daga haka ya Fice ta Rakashi da ido Cikin Taruwan Hawaye.
Mansur na Fita Mus"ab ya balbeleshi da masifa wai ya Shanyashi Shi dai Hakuri kawai yake bashi yana Dariya Sallama sukayi bayan ya gayamai Dizan bazata samu Damar Fitowa ba Karamin Tsaki Mus"ab yaja kawai ya wuce Mansur ya bashi key din Motarsa ya koma da ita Saboda Dare har Haraban Gidan ya Rakasa saida yaga Ficewarsa Daga gidan kana ya koma Ciki.
Shi kanshi a gajiye yake barci yske son yayi ya Huta Domin yafi Sati baya samun wani Ishashen Barci,Dakyar ya Lallashi Diza ta shiga Tayi wanka yaje Kitchen ya Dauko Filet da kofuna sai fork,Yazo ya Saka Kazan a Filet ya bita dashi Har kan gado yana bata tana amsa Dakyar,Ya matsa mata taci ne saboda yasan tana jin yunwa Kadan taci ya bata madaran Tasha ta koma ta kwanta,Shi ya karishe sauran kazan ya Danna da madara Sauran kuma ya kai kitchen ya saka Cikin Fridge ya Dawo Falo ya Dauki Jakar kayansa ya Shiga Ciki ya Samu Diza kwance acikin Bargo Idanuwanta a lumshe bai mata mgana ba ya Fada Tiolet yayi wanka Koda ya Fito Barcin gajiya ya kwashe Diza Bata sani ba,Mirmishi kawai yayi ya Bude Jakarsa ya Dauki kayan barcinsa Riga da wando ya saka ya Fesa Turare ya Shinfida Darduma yayi Shafa"i dawuturi Dakyar kamar ya Kifa Falo ya Fita ya RarrageHasken wajen kana ya Dawo Ciki ya Rage Hasken Bedroom din ya kunna Dumlight,Kan gadon ya Hau Lokaci Daya yana Jawo Diza jikinsa wacce ke sanye da Daguwar Rigar barci mai Taushi,Daman barcin ya kwasheta da Fargaba ne,Tana jinta ajikinsa Tayi Saurin Zabura Riketa yayi yana fadin"Relex..Babu abundaa Zan yi miki kwanta kiyi barcinki..Nima gajiya bazata barni na iya Moranki Dakyau ba.."Yafada yana Raban Wuyanta wani yamm taji acikin Jikinta ammh Ta kasa Motsi Tama jinsa ya kara Rumgumeta Bisa Kirjinsa yaja Bargo ya Rufesu yana Sauke Numfashi Lamo Diza Tayi Tana Shakam Kamshin Turaransa Tunani na neman Shigo mata Yasa Tayi Saurin Kiran sunan Allah Saboda yadda suke agajiye yasa basu wani jima ba Barci ya kwashe su Dukkansu.
Bangaran Mastur Rumana dai ba haka Tagani Domin Har Mastur ya Shigo Gidan nan bata sani ba,ba Dakinta ya Fara Shiga ba Dakin kusa da nata ya Bude ya Shiga shima agyare yake Tsab nan ya Sauke kayansa Domin bai yi Tunanin Fara Rayuwa da wata a Daki Daya ba Sai da ya Shiga yayi wanka ya Saka Wata Jallabiya mai Ruwan Madara Shafa"i da Wuturi yayi Ya Dade Zaune yana Tufka yana Warwara kafin ya Mike Cikin Sanyin Jiki ya Fita Zuwa Falon Lokaci Daya yana karema Falon kallon aransa yake fadin Nice Ledan kazan Daya ijiyeta nan Saman Dinning ya Dauka ya Nufi Dakin Rumana yana Addu"a da Fatan Allah yasa Tayi barci sai addu"ansa bata ci ba yana Taba Kofar ta Bude Daman an Dan Sakayata ne sai ga Rumana Zaune kan Tsakiyar gadonta Taci kuka ta Koshi Har ta Dago Fuskarta Tana kallon Kofa Sai gashi sun Hada Ido Hudu da Mastur Dake Tsaye da Leda ahannunsa,Mamaki ya kamata Bayan ta Sauke Numfashi Ita nata angon da Shigar Jallabiya zai Shigo mata..! Da alama ma ba yanzu ya Shigo Gidan ba.
Shi kuwa Mastur saurin Karisowa Cikin Tsakiyar Dakin yayi yana kaucema Idanuwan Rumana Gefen gadon ya Zauna kamar wani mara gaskiya ya Dora mata ledan kazan kan gadon agabanta Cikin mamaki Tabi ledan da kallo kafin ta Sadda kanta kasa Tana kara jan mayafinta Shuru shuru yana Zaune bai ce mata komai ba Ganin haka yaasa ta Muskuta Tana Fadin"Ina wuni..!"
Dakyar ya iya Bude baki ya amsa mata Cikin wani irin kasala,Dif kuma yayi ya kasa mgana Domin bai sam ta ina Zai Fara ba itama sai tayi Shuru gabanta na Faduwa Wajen kimamin minti goma Sha Biyar ya mike tsaye yana Fadin"Kici kafin ki kwanta..Sai da Safe."Daga haka bai jira cewarta ba ya juya yana Tafiya kamar zaiFadi Rumana ta bishi da kallo,baki Bude har ya Fice Saboda mamaki,Daidai Karar Rufo Kofar da yayi daidai Zubar kwallarta Sai yanzu ta kara yarda Mastur baya sonta..Domin Angon adaran Farko Doki da Zumudin Amaryansa yake ammh ita ba wani kulawa ba Tattali ba mgana mai Dadi,yadda take karantawa a Littafan Hausa da Turanci Daran Farko Kazan amarcin ma Ango ke lallashin Amaryansa Tana ci kauda kai Tana bata rai yana bata abaki ammh ita anata barayin ba Haka yake ba Dakyar ma angon nata ya Shigo wajenta ya Tura mata Ledan kaza yace taci Kafin ta kwanta Daganan ya Fice abunsa ya barta Bayan yayi mata Sallama kemsn Ita kadai Zata kwana Adaran Farkonta Angonta ya Raba makwanci da ita wannan wani irin Rana ce Gareta,Sai kuka Haka Rumana ke kuka Kamar ranta zai Fita Tagaji ne ta Mike ta Rarrafa Ta Shiga Tiolet tayi alwala ko wanka Bata iya yiba ta zo Tayi Sallar Isha"i da batayi ba Tana jin yunwa kwarai Domin Rabonta da wani abincin Kirki Tun Breakfast din da sukayi agidan Daddy ammh bazata iya cin komai ba Saboda bakinciki Ture ledan kazan Tayi kasa ta Kudundune akan gadoTana Cigaba da kukanta ko kayan Jikinta bata cire ba,Ta kwanta Bata san iya adadin Lokacin Data Shafe Tana Kuka ba da Tsausayama Rayuwarta Bata san Lokacin da barci ya kwasheta ba.
******
Washegari Bangaran Diza da Mansur sun tashi Cikin Farimciki Domin Diza Tana ganin Soyayyah da Tattali wajen Mansur wanda yayi Sanadiyar goge Duka kukanta,Sai dai kawai ta Rika Binsa da ido Tana addu"an Allah ya Dora mata kaunarsa ya Cire mata son wanda baya sonta.
Daga gidan Daddy aka aiko musu da Breakfast,Kwando Biyu Mansur Daya Mastur Daya,Dukkansu mazajen su suka Fita suka amsa Bayan Mommy ta kirasu ta sanar dasu ga abun karyawa nan zata aiko Dashi,Mansur shi yayi komai ya Lallaba Diza yayi mata wanka ya Sauya mata kaya shima yayi wanka ya sauya kaya,suka Fito Falo ya Zuba musu abun karyawn Tana kan Cinyarsa yana bata abaki Tana kauda kai yana Lallashinta Har taci ta koshi kana shima ya samu yaci ya koshi Daganan ya Dauketa suka Koma Cikin Bedroom suka kara Nannadeawa suka koma Barcin gajiya.