← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 82 OF 94

Sashe 82

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 3 min read

Tana Cikin wayar ne taji kamar kakarin Amai da gudu ta Jefa wayar nata kan kujera ta Rumtuma Zuwa Dakinta anan gefen gado yake Durkushe yana Kakarin Aman bai iya karisawa Tiolet ba,da Sauri ta karisa gareshi ta Rikeshi tamai sannu Makogwaronsa ya Tushe Numfashi ma Dakyar yake Fitarwa ga Tari Daya Sarkeshi Ya farayi ba kakkautawa Sai ga Jini yana Biyo dan Ruwan Tea din Dayasha Rumana ta Tsorata Cikin Firgita ta kurama Jinin Ido kafin tace"Mun shiga Uku..Jini fa..,?
Tafada Lokaci Daya Cikin wani irin Rudewa shi kanshi Mastur,ya Rude Daya ga Jini yana Fita Daman Likita ya Fadamai in Zuciyarsa takai wani mataki ko Tari yayi ssi jini ya Fita to ganin haka yasa yasan Abubuwa sunyi Nisa kuka Rumana ta Fashe dashi Tana kuka ta Taimakamai ya Tashi taRakashi Tiolet ta taimakamai yayi wanka Ta barshi ya karaasa wankan ta Fito ta gyara wajen Daya bata Tanayi Tana Sharan kwallah acikin Ranta Tana Fadin ya Zama Dole Tayi wani abu.
Ita takoma Cikin Tiolet din ta taimaka masa ya Fito yana Fitar da Numfashi Sama Sama,ita ta taimaka mai ta shafa mai mai ta kuma sakamai Saukakkun kaya ya saka Yana kallonta ta Saka Hijabin Sallarta Ta Dauki key din Motarta Yana kallonta Yafara Kokarin yi mata mgana Ganin haka yasa tace"Zan je na samo maka mganin Mtsalarka..Bazan bari ka Mutu saboda wata ba Ahalin ina da yadda Zanyi..!
Tafada Idanuwanta Taf da kwallah mamaki ya kamashi Cikin Sarkewar murya yace"Wata..?wata wa..?
Bata tsaya ma bashi amsa ba ta kada kai ta Fice Tana Fadin"Ka kula da kanka..yanzu zan dawo..!
Daga haka ta Fice tana Sharan kwallah Allah ne ya kawota Hanwa Lafiya a gidan Daddy ta Sauka Ta zuba Hon megadi ya Bude mata get ta sulala zuwa Ciki,ko parking din ma ba Daidai Tayi ba,Bata cikin Natsuwarta Tana Fitowa Tayi hamdala ganin Motar Daddy Gudu Gudu Sauri Sauri ta Nufi Cikin gida.
Afalon kasa Taci karo da Mama Fadime ita kanta Mama Fadime Ta tsorata da ganin yanayin Rumana Tana Daga Tsayen ko Zama ta kasa yi bayan sun gaisa tace tayi mata mgana da Mommy,ta amsa da Toh da Sauri ta Haura sama aranta Tana Fatan Allah yasa Lafiya.
Diza Dake Cikin Dakinta Taji kamar mgana afalon kasa Daman Hankalimta Tun Jiya ba"a kwance yake ba Tun Tafiya Mastur kuma Tayi ta kiran wayarsa bai Daga ba Mansur karami bayanan wajen mardiya ya kwana da Safen ta kawo mata shi yasha Nono ita ta wuce makaranta Ta bashi Nonon kadan yasha,daman Mardiya tayi mai wanka sai barci Tana Zaune ne tana Tufka tana warwara kamar taje Chan Lowcost tagani ko Lafiyasa yasa ta kasa Zama Waje Daya ko Sagir din Dayake ta Kiranta bata Daga ba jin mgana Sama sama afalo yasa ta tashi da Sauri ta Fito Daidai Lokacin da Mommy ta sauko kasa Tana Kallon Rumana cikin mamaki Tace"Ah Rumana lafiya dai ko...
Rumana najan majinan kuka tace"ba lafiya Mommy ina kwana..? Don Allah kimim mgana da Daddy ina son mgana dashi Cikin gaggawa..!
Mommy ta Rude Cikin Tashin Hankali tace"Rumana meyafaru..? Wani abu ne ya samu Mastur din ne..?
Kai ta girgiza ssi kuma ga Hawaye Diza dake tsaye Kofar Dakinta sai taji Zuciyarta ta Fara rawa,Mommy kuma Tashin Hankalinta ya karu taja Hannun Rumana Tana Fadin"Muje Sama..Daddy na chan..!
Tafada Lokaci Daya suna Haura Steps din Bene Diza Data Daskare a Tsaye ta kasa Daga kafafuwanta Ballatana Ta bi bayansu haka kurum take jin kasala ya Rufeta Dakyar ta samu Damar Ciran kafa tabi Umarnin Zuwanta wajen Bin bayansu Taji meke Faruwa..? Allah yasa ba wani Rashin zasu sake yi ba.
Chapter 82 · 0% Book details