← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 94

Sashe 47

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 7 min read

9pm Daidai ya Shiga Gidan wani barcin kuma aidonsa kamar yasha kayan maye Wayoyinsa ya Dauka da System dinsa Dake Cikin Motan ya nufi Barayinsu Yana Shiga Falon yaga wani kwadon Abinci wanda baya Raba Daya Biyu Mommy ce ta kara aikowa Dashi Dakin Rumana ya kallah yaga da Haske kuma bata Tura kofan Duka ba bai yi Tunanin Shiga ba ya Saka makulli ya Bude Dakinsa ya Shiga ya maida Kofa ya Rufe.
Rumana Dake Cikin Dakinta ta Saki Numfashi Bayan taga Shigowarsa Hankalinta ya tashi Tana cikin Zullumin ganin Tun Dazu Taji Shigowar mansur ammh Shuru bata gansa ba Tayi Tunanin kiransa sau ba adadi Sai ta kasa kiran Wayar Umma ya Dauke mata Hankali basu Dade da gama waya ba ya Shigo.
Wayar ta ijiye saman gadon ta Bude kofar tiolet ta Shiga wanka take so Tayi ta kwanta yau bata Cuci kanta ba Mommy na kara aiko musu da abinci Taci ta koshi na Safe kuma ta bama Dirban ya maida shi Domin ta Lura Daga ita Har shi basu Taba komai Daga cikin abincin ba Har gwarama Dazu Basma Taci Soyayyan Dankalin Dazu kafin su Tafi.

*Ki biya ki karanta cikin Salama Mace mai aji mallakan komai nata take yi bata jiran Abun Sata 09069067488*

*Janafty...*
1/1/22, 18:54 - Maryam Badmsi: *SS...22*

"Har ta gama abubuwan da Zatayi ta kwanta bata kara jin Motsin mastur ba sai da Safe Wajen misalin 10am lokacin Taji Knooking din kofa Tayi Zaton Baya gidan ne ta Fito da Niyar taje ta Bude domin tasan Sakon Mommy ne na Breakfast dinsu sai kuma sukayi karo ya Fito Daga Dakinsa Saurin ja da Baya tayi tana gaisheshi ya amsa kamar mai ciwon baki Kitchen ta Shiga ta Dauko mai Kwandon Jiya Domin ta bama Direban ya maida ma Mommy sai ta iske har Mastur ya ijiye kwandon nan Falo ya Shige Ciki Har Haraban Gidan ta leke Daidai Lokacin da Motar Direban ke Fita Daga Haraban Gidan Baki ta Ciza kafin ta Dawo Falon,Kitchen ta maida Duka Kwamdunan Abincin Ta samu Filet ta Dibi Soyayyan Dankali da kwai sai ta Samu wani Mug ta Diba Ruwan Lipton Ta Fito Falo Saman Dining ta Zauna inda taga an jera kayan Tea ta hada komai ta fara sha Zuciyarta na wani Tunani Kofar Dakin nashi ta Kura ma ido kamar Tana ganinshi Lokaci Daya Tana auna wasu Tunane acikin Ranta Kenan haka zasu Gudanar da nasu Zaman auran..? Abunda ke bata mamaki baya taba komai na abincin da Mommy ke aikowa Dashi sai dai ita taci kadan kuma ta Tabbata Mommy Tana Fahimtar basa cin abincinta Tunda in aka kawo wani Tana maida wanda aka kawo kada Ta barsa ya Lalace tunda ita ba ci Zatayi ba kuma Uban gayyar Shi bata son ina ya saka gaba ba Tana Tsoron kada Mommy ta kula da hakan har takai ga Tayi mgana.

Haka ta gama karyawanta Tana ta Tunanenta,nan ta bar komai Saman Dinning din ta Kariso cikin Falon ta Zauna kan Daya Daga Cikin kujerun Falon Tana Sauke gajiyan cin Abinci,Zaman Shuru Duk ya isheta yasa ta mike Tana kokarin Hada Kayan kallon Dake falon,ammh ta kasa sai kawai ta barshi bata kara zama afalon ba ta koma Cikin Dakinta Bata son ta zauna haka Tunani zai mata yawa sai ta Dauki Wayarta ta kira Abba bai Daga ba sai da ta katse kana ya Kirata suka gaisa,Yana Tambayanta Mastur tace yana Lafiya Basu Dade suna waya ba sukayi sallama bayan ya kara mata Nasihan Zaman hakuri da Zama lafiya ya ba Umma sun gaisa Sama sama Daganan sukayi Sallama.

Wardrope dinta ta Bude ta Dauko Trolley dinta Wanda aka Sako mata Takardunta da Sauran muhimman kayanta Daga gida Kan tsakiyar gadon ta Zazzage komai Tana gani Tarkadunta na makaranta ta Hadasu waje Daya Taji Dadi Dataga Har da System dinta zai Debe mata kewa sai Sauran abubuwanta masu muhimmanci Duk ta Dauka Tana adanasu Inda suka Dace Musamman Takardan da suka bata a Uduth wanda Zata je dashi ABU chika ta nuna Ranar Monday,Aikin shi ya Dauke mata Hankali Bayan ta gama ta Koma Kan gado ta Zauna Ta tankwashe kafa,Bayan ta saka Gilashinta Ta Bude Syatem din Ta kunna,Daman Rumana akwai son karatu bata Bata Lokaci ba ta Fara Karatun Abunda ya Shafi Abunda ta karanta Domin Tana da Burin Bayan ta gama Service dinta Zata Dora Karatunta Wato Resendency,Tana so ta samu kwarewa kan Abunda ya shafi yara Hakan yasa Hankalimta ya Dauke Daga Tunani ko Motsin Mastur Daya shige Daki kamar baya gidan.

Har ya Fito Falon yaje Kitchen ya Dauko Mug ya Dibi Ruwan Zafi yahada Tea din yasha Bata sani ba Tadai ji Rufowar kofar Dakinsa Sai Lokacin ta Fahimci Ya Fito kenan,Ranar haka suka wuni acikin Gidan Tana da Tabbacin bai fita ba ko kofar Gida Direban gidan su Mommy sai Dare ya kawo musu kwandon Abinci Lokacin Tana Falo ita ta Fita ta karba bayan sun gaisa tace mai ya tsaya ta koma Kitchen ta Dauko mai kwanduna Biyun na jiya dana yau da Safe ta bashi ya Juya ya tafi Bata wani jin yunwa Domin Ta kara cin Ferfesun Kayan cikin sosai kuma ya cika mata Ciki.
Wannan karon Tuwon Shinkafa ne Miyar Agon,Da yaji Nama da Kifi,Rumana nasan Tuwon Bata tsaya wasa ba takai komai Kitchen tasamu Filet ta Dibi Tuwon Leda Daya taci Ta Hada da Ruwa,Abunda yake kara bata mamaki da Mastur kamar ya manta da akwai Mutum acikin Gidan ko Motsin shi bataji kuma ta Tattabata yana Cikin Gidan kuma bata ga Fitarsa ba,Bata ji wani Dadi ba anan Falon ba ana kiran Sallar Isha"i ta Shige Ciki abunta yau ko Motsin Mansur da Diza bata ji ba Tana Tunanin Kila suma Daga Barayinsu yau basu Fita ba.

Haka suka kwana Washegari ma Haka suka sake kwana bata Sauya zani ba Hana Rantsuwa Da Rana tana Falo ya Fito Daga Cikin Dakin yana Sanye Da Jallabiya Ruwa ya fito Dauka Kishi ya Fito Dashi,Sai alokacin Suka gaisa bayan sun kwana sun Wuni basu ga juna ba,Gaishe tayi ya amsa Batare Daya kalleshi ta ba,Ya shiga Kitchen bai Dade ba ya Dawo daGoran Ruwa mai Sanyi ya Shige Ciki ta bisa da kallon mamaki Domin ita dai bata ga yana cin Abinci ba sai dai Ruwa ko Lemo ko kuma da Safe yasha Tea da Daddare kuma yasha Ruwan lipton kuma bata ga wani alaman yunwa ko Damuwa a tare dashi ba Tagumi Tayi aranta Tana Janjanta ma kanta irin Mijinta Data aura kenam...?gashi Tun ranar Litini Da Safe da yan Sokoto suka zo musu sallama ba wanda ya kara Lekosu daga su sai Halinsu Diza ma da Mansur bata kara,jin Duriyarsu ba sai Ranar alhamis da Sassafe Lokacin Tana ma kam Darduma bayan ta idar da Sallar Tana azkar Taji karan Bude kofar dakin Mastur Dayake Dakin na kusa da nata In dai zai Fito ya Taba Kofar Dakin Tanaji Ita dai tana Zaune Bata motsa ba Tunaninta ko Kitchen zai shiga neman wani abu Tunda ko Masallaci basa zuwa acikin Gida suke yi Dayake ba wani masallaci kusa dasu da Nisa gaskiya ita kamta Lokaci takan Duba awayarta Take gane Lokutan sallah.

Ta na nan Zaune batasan me ya Faru ba sai taji Muryan Mansur acikin Falon suna mgana da Mastur,Da sauri tatashi Tana Tunanin Lafiya Kamar ta Fita sai kuma ta fasa ta koma ta Zauna Mastur Dake chan Falo Shi da Mansur Cikin Yamutsan Fuska ya kalli Mansur da Duk ya Firgice yana Fadin"Lafiya na ganka haka..?

Yafada yana kara kallonsa ganinsa kamar baya cikin Natsuwansa,Mansur na Shafa kai yace"Yaya Mastur aron Anty Rumana nazo ka bani..Diza ce ba Lafiya don Allah muje ta Dan Taimaka mata."Ya karishe Fada yana Sosa kai Daga yanayin mganarsa Mastur ya Fahimci Abunda ya Faru wani irin Dam yaji akan Kirjinsa,Da sauri ya Juya yana Fuzgar Numfashinsa bai ce ma Mansur din komai ba ya isa ga Kofar dakin Rumana ya kwankwasa mata Daman Tana Zaune ne kunnenta na Falon da Hanzari ta Mike Tana gyara Zaman Hijabin jikinta ta isa ga Kofar ta Bude,Taci karo da Mastur tsaye akofar Dakin Da Sauri ta rankwafa Tana gaisheshi kallo Daya yayi mata ya amsa da "Lafiya lau..Kije Mansur na neman ki..!

Daga haka ya juya Hannuwansa na Cikin alijuhun bakin Wando  Dake Jikinsa kawai ya Tura kofar Dakinsa ya Shige ya Rufo kofa ya barsu nan suna Binsa da kallo Mansur bai Damu ba yafi kowa sanin Halin Mastur hankalinsa Baya jikinta Ya bar Diza Tana ta kuka Ya riga yayi aika aika Dole ta kwana tana kuka kuma yaji mata Rauni Domin jiya ya amshi Budurci Diza
Chapter 47 · 0% Book details