← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 94

Sashe 3

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dakyar Maryama Ta ijiye Mastur Tabi Sule Zuwa Gida Har Waje Habibu ya Rakata Yana Ta Faman Allah ya Kiyaye Hanya da Sakon in sun isa gida Lafiya ta Kirashi a waya ta gayamai ta Hau Mashin din Mijinta Tana Fadin.

"Toh Yaya in mun isa zan Kira ka Insha Allahu.."

_Hmm...Salon na Musammanne..Tafiyar akwai Nisan Zango Yanzu muke Cikin Shimfidan Labarin bamu ma Shiga Cikin Mafarin ba.._

_Albishirunku Masoyana wannan karan na bude muku wani Shashi na musamman Saboda ku..Ina masu Bukatan Atalla musu Hajarsu Ko wani iri ne Domin samun costumer ta ko"ina..? Ku garzayo kakarku ta kusa yanke saka Zan Tallata muku Hajarku a Duka Shafukana Domin inganta Sana"arku da kuma Samun Cinikaya mai Tsabta da kuma kara Hada hada wajen Masi siye da Siyarwa mai Bukatar A tallata mata Hajjarta Zata iya min mgana kai Tsaye ta wannan Lambar Tawa 09069067488 domin karin Bayani...Sai kunzo Kunsan dai mai kasuwa Shi ke da Riba.._

*Domin zama Daya Daga cikin wadanda zasu karanta Labarin SADAUKARWAR SO..! Zaku Biya kudin karatunku kamar haka Masu amfani da Banki Zasu Tura â‚?300 ta wannan asusun banki 0552179550 Jamila umar gtb,Masu Katin waya kuma zasu Turo â‚?400, ta wannan lambar wayar 09069067488 Adauki Hoton katin sai aturo kai Tsaye mutanenmu na Niger kuma zasu Tuntubi wannan lambar kamar haka +22794775574 domin karin bayani,Insha Allahu mutum zai tsinci kansa a paid group ina maraba da ku masoyana nagode*

*Janafty..*
*Intelligent writer"s asso*
*01/10/2021*
1/1/22, 18:50 - Maryam Badmsi: *SADAUKARWAR SO..!!*
_(Labarin Yan"uwantaka,Soyayyah Tare da Sadaukarwa)_

*Wattpad:@Jamilaumar315*
*Mallakar:Jamilaumar(Janafty)*

*Page2️⃣*

Kullum Maryama Tana Hanyar Zuwa Ririwai ganin Mastur wanda Tuni Baba Jibo yayi mai Huduba da sunan da Maryama ta Zabamai kowa ya sani Zabin Maryama Shine Zabin Habibu.

Har sai da akayi suna kana Ta Zauna agida anyi Shagali Daidai Gwargwado na masu karamin Karfi an yankama Mastur katon Ragon Sunansa wanda Maryama ita ta Kiyawata Ragon a Chan Maruka Daman Tun Samuwar Cikin Hajarah Din Tace Ragon da akuyarta ta Haifa na Sunan Abunda Hajara ta Haifa ne kaunar Dake Tsakanin Habibu da Maryama Wata kaunace da Allah ne kadai yasan Yawanta.

Inna Hasiya ce ta Cigaba da kulawa da Hajara da Mastur,Ayya ma Sai dai ta Leko su Inno kuma Bata zo ba Tana yi ma Inna Hasiya kara da kuma Ayyah Kuma Alhamdulillah Hajara Tana samun Dukkan kula Bata komai Inna Hasiya Ke Duka ayyukan Gidan Hajara ko Tace Zatayi sai Ta Hanata Gefe Daya Habibu na Tsaye da Duka Kafafunsa na ganin ya Yalwata Ahalinsa Gabadaya Duk da Baba Jibo Karfinsa ya Fara karewa ammh Karfin Noman na nan Tare Dashi,Baya barin Habibu Ya Tafi Gona Shi kadai Koda bazai yi wani aiki ba sukan Tafi Tare Domin ya Taimakamai suna Noma koda ba Damuna ba sukan Noma Irin su Tumatir da Sauransu kafin Damina Ta zo.

Koda Hajara Tayi arba"in da Haihuwa sai wanda ya ganta tayi Kiba ita da Mastur kamar ba su ba sun samu kulawa Sosai kuma suna cin abinci mai Gina Jiki Sai kuma akayi Sa"a Nonon Hajara mai kyau ne Tuni Mastur sai Kiba yake Maryama kuwa Duk sati sai Tazo Garin kawai Domin Taga Mastur wanda Soyayyar Datake yi mai Tun yana Ciki ne Har yazo Gidan Duniya.

Sai Hajara Da kanta takai ma Inno Mastur Ta gansa ta Daukesa Ta sakamai albarka Tare da Fatan Rayuwa mai albarka Chan ta wuni Tare Dasu Suna ta ina suka saka da ita ita da Mastur irin Soyayyar da Kowa ke Nuna mata ita da Abunda ta Haifa na sakata kuka Habibu Kullim ya Dawo Haka Zai Dauki Mastur ya Dinga mai wasa Tun yaron baya ganewa Har ya Fara gane mai kula Dashi Sosai Wani Lokacin Hajara ita yar kallo ce Domin Daga Inna Hasiya Har Baba Jibo Suna Rawan Jiki wajen Daukan Mastur yaron ya Shiga Ran kowa Saboda Nasabarsa da Kyansa Tun yana Jaririnsa.

*TUSHE..*

"JIBRIL Baba Jibo da Inna Hasiya sune Asalin iyayen Habibu da Maryama su din Dukkansu Haifffun Garin Doguwa Local Goverment Dake garin kanon Dabo awata anguwa mai Suna Ririwai.

Tsakanin Inna Hasiya da Baba Jibo auran Zumunci ne Tunda Abokan wasa suke da Juna iyayansu Tun suna da rai suka Hadasu Zama waje Daya saboda ganin Dacewarsu,Tun iyaye da kakanin Sana"ar iyayen Su Baba Jibo Noma ce da Kiwo kuma ita suka gada Dayake alokacin Ilimin Zamanin nan bai wani yawaita ba Sai karatun allo Daka Sauke Zaka Fara Noma Domin itace Sana"a Lokacin Da kowa yasan iyayenmu Musamman ma na kauye Dashi.

Tun bayan Auran Baba Jibo da Inna Hasiya Allah ya Dauki Ran Iyayan Baba Jibo Daman Inna Hasiya Iyayan Baba Jibon suka Riketa Ta rasa nata iyayan Tun Tana karama sai ya zamanto sun Rumgumi Maraicin su Dagasu sai Daidai kun yan"uwa da suka Rage wasu duk sun Tsallake Zuwa wasu garuruwan Domin neman nakai kuma Tunda suka Tafi basu Dawo ba.

Inna Hasiya itama ta Dade bata samu Haihuwa ba Domin sai da suka Fitar da Ransu kana Allah ya basu Habibu wanda Haihuwarsu yazo musu da wani Budi a Shekarar Amfanin Gona yayi kyau Baba Jibo Da abokinsa Mallam Yahaya sun samu Alheri sosai Shiyasa Tun Lokaci Baba Jibo Ke Kiran Habibi Jarumi kuma Gwarzo.
Tun Haihuwansa suke matukar sonsa Haka Habibu ya Taso Cikin Gatan Duka iyayansa Gefe Daya kuma ga Aminin Mahaifinsa Baba Yahaya da Inno da Ayya suma ba"a barsu abaya ba wajen kula Dashi Dayake Zumunta ne na Makota ka wanda alokacin Bayan Makocinka Shine Babban Amininka kuma Dan"uwanka Abokin Shawaranka.

Habibu ya taso Shi kadai ne agaban Inna Hasiya kuma Shi mutum ne mai kulafuncin Yan"uwa sai dai Allah bai bashi ba Tun yana ma Inna Hasiya kukan ta sama mai kanwa Har ya Gaji Lokacin da aka Haifi Maryama Habibu nada Shekara Tara a Duniya ne Lokacin yana Makarantar Allo ya Hada karatunsa na Izifi Talatin,Alokacin ko su inna Hasiya sun Cire ransu da samun wani karuwa sai gashi Allah ya basu Maryama Farincikin da Habibu yayi ko Inna Hasiya da Baba Jibo basu yi shi ba Haihuwan ta kasance shi akayi mawa.

Domin Tun da Maryama Tazo Duniya alhakin kula da ita ya koma Wuyan Habibu MKarantar allo Kadai yake iya Tafiya yabar Maryama Bayanan kuwa Yana Gida Tare da ita Tun Tana Wata Hudu a Duniya Da Rigima da komai Yake sakawa Inna Hasiya na goyamai Maryama Da karfi da yaji ya koya mata zama Komai ya samu Baya iya Cinsa shi kadai Sai ya Rage ma Maryama Tun kafin Maryama ta isa Fara cin Abinci Habibu ya Fara bama Maryama kayan kwalama Batare da Sanin su Inna ba sai Dai kawai suka ga Maryama Bakinta ya Bude da Cin Abu komai aka bata.

Maryama da Habibu ta Fara Bude Ido a Duniya,Tun Tana Shekara Daya a Duniya Ta Fara Tafiya Ko"ina kuma Habibu Zai saka Kafa Bata yarda sai ta Bishi In ko yamata wayau ya Tafi makarantar Allo bata da ita ba In ta Fara kuka sai ya Dawo Taji Muryansa Ya Dauketa ya Lallasheta ya bata Sweet din Daya Siyo mata take yin Shuru Ko Inna Hasiya ko Baba Jibo Bata yarda da kowa sai Habibu Mutane suna mamaki da Jinjina ma Wannan kaunar Dake Tsakanin Maryama da Habibu.

Tun awannan Shekarun nata Habibu ke Daukanta yana Zuwa Allo da ita Saboda In bai je da ita ba Ta Rika kuka kenan akwai Ranar ma Data Fakaici Ido Tabi Bayansa sai dai Tsinto ta akayi Tabi Hanya Tunda Ranar Bai kara yarda ya Tafi ya barta ba Duk inda Zashi da ita yake Tafiya Tun Alarammah na Fada har ya Daina Saboda Maryama Bata yarda da kowa sai Yayanta Habibu Kaunace Daga Allah data kuma Fara Tun Tasowarsu.

Haka Rayuwarsu Ta Cigaba da Gudana Cikin kaunar Juna Har Habibu ya Sauke alqurani aka yayeshi sai ya zamana Maryama kadai ke zuwa makaranta Shima ssi da aka sha Daga Domin Da Farko tace bazata kara zuwa makarantar ba sai da yayanta Habibu Shi kuma Lokacin ya Fara Bin Baba Jibo Gona sai yamma suke Dawowa Maryama wuni take kuka Kamar Wata wacce Za"a yanka In Ta Dawo Daga allo Bata ga Yayanta ba Inna Hasiya tagaji da Lallashi ta Fita Batunta Sai ya Dawo ya Lallasheta Take yin shiru Dole ta Hakura Tunda Inna Hasiya tacr Tana mace baza ta Rika Bin su Gona ba ta zauna agida.

Haka Rayuwarsu ta Cigaba da Tafiya Cikin Soyayya da kaunar Juna Daya baya son bacin Ran Daya musamman ma Habibu Da baya kaunar bacin ran maryama ko kukanta itama Haka Sai dai kuma Duk da wannan Kaunar Dake Tsakaninsu Bai Hana Maryama ta Girmama Habibu a mtsayinshi na yayanta Datake matukar Ji dashi.

Tana da Shekara 14 aduniya ta Sauke Qur"ani Akayi Walimar Saukarsu a makarantar allonsu Wanda Habibu yayi mata rawan Gani Sosai wajen Walimar Saukarta Wanda ya saka Maryama farinciki sosai Zuwa Lokacin kuma sai Manema Daga Ko"ina suka yi ma Maryama chaa Tunda alokacin Yara mata basa wuce Sa"anninta ake Aurar dasu Tunda ba karatun Boko suke yi ba.
Duk cikin manemanta Mutum Daya ta yarda Take kulawa Sule wanda yake Mutumin Maruka ne Shagon kayan Kwalliyan mata gareshi anan cikin kasuwar Ririwai,Maraya ne Mahaifinsa ya Rasu sai dai Yayyinsa Maza Suna Saune a Famiy House dinsu ne gidan Gado Shi da Mahaifiyarsu Da suke Kira Goggo Sule Shine karaminsu yana da Yayyi mata Da Maza Dukkansu su Biyar ne wajen Goggo Mata Biyu Maza uku.

Ganin Maryama Ta fi Son Sule yasa Baba Jibo da Mallam yahaya suka yi Bincike akansa kuma suka samesa da Nagarta Hallaye nan da nan suka bashi Izinin Turo mgabatansa Lokaci Habibu nada shekara 24 aduniya ya zama Matashin Saurayi,Cikin Lokaci Kadan Sule ya Turo mgabatansa aka Gudanar da Neman aure aka Saka Rana Har acikin Ran Habibu bai so Maryama Tayi Aure Nesa Dasu ba yaso Kusa da Gida Saboda ya Shaku da ita Zai ji ba Dadi in Tayi mai Nisa Sai Dai kuma bashi da tacewa ganin Maryama na kaunar Sulen kuma ya Tabbata in ya Furta Baya son ta aureshi Ko Maryama na Mutuwar son Sule ya Tabbata Saboda Farimcikinsa Zata Fasa Shi kuma Bazai so ya zama Sanadin Ruguza Farincikin Yar"uwansa ba kuma Tilon kanwarsa ba.
Chapter 3 · 0% Book details