← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 94

Sashe 5

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 7 min read

*Domin zama Daya Daga cikin wadanda zasu karanta Labarin SADAUKARWAR SO..! Zaku Biya kudin karatunku kamar haka Masu amfani da Banki Zasu Tura â‚?300 ta wannan asusun banki 0552179550 Jamila umar gtb,Masu Katin waya kuma zasu Turo â‚?400, ta wannan lambar wayar 09069067488 Adauki Hoton katin sai aturo kai Tsaye mutanenmu na Niger kuma zasu Tuntubi wannan lambar kamar haka +22794775574 domin karin bayani,Insha Allahu mutum zai tsinci kansa a paid group ina maraba da ku masoyana Nagode*

*Janafty...*
1/1/22, 18:51 - Maryam Badmsi: *SADAUKARWAR SO..!!*
_(Labarin Yan"uwantaka,Soyayyah Tare da Sadaukarwa)_

*Wattpad:@Jamilaumar315*
*Mallakar:Jamilaumar(Janafty)*

*Page3️⃣*

Mastur nada wata goma sha takwas Hajara ta yayeshi a kuma lokacin ne Habibu ya bayyana ma Iyayansa da ita kanta Hajara Alkawarin Daya Dauka na Mallakama Maryama Mastur har Abada.

Dukkansu sun Nuna amincewarsu Hajara kuma Daman ita mai Biyayyah ce ga Lamarin Habibu sai dai Inna Hasiya Ta ce baza"a bama Maryama Mastur yanzu ba yayi kankanta abari yakai ko Shekara Biyar ne ammh ayanzu akwai Cutarwa Araba uwa da D'anta a irin wannan Lokacin Jin haka yasa Baba Jibo ya mara mata baya Dole Habibu ya yarda da Shawaransu sai sukayi Shuru da bakinsu basu Gayana maryama din ba.

Sai dai Tana jin an yaye Mastur Ta Shiryo tazo kan zata Tafi Dashi Chan Maruka ta yayeshi Habibu ko Hajara ba wanda yayi mata gaddama Suka Hada mata kayan Mastur suka Dankamata Daman ya saba da ita ganin itace yasa bai ma yi Rigima ba Duk da Tun yana jaririnsa bai da yawan Rigima da yawan kuka Maryama Taji Dadi Harda kuka Sulaiman yazo ya Dauketa suka koma Goggo Dataga Maryama Tazo da Mastur Sai da Tadinga mgangunu Tana Fadin Sai dai Taga ana Haihuwa ita kam Juya ce Harta Zainabu ta gama Raina Maryama sai dai Saboda Sule yasa bata tankasu Ta Cigaba da Sabgarta na kula da Mastur Datake Jinsa kamar Dan Da tahaifa acikin cikinta.

Mastur bai dawo gida ba sai da ya Shafe wajen wata Biyu a wajen Maryama kana ta Dawo Dashi Wanda kamar kada ta Dawo Dashi Saboda yadda suka saba Da juna Harta Sule sai da yaji kewa komai ita kemai Bata Gajiya Watarana Har Hawaye Sule yake mata a Boye yana Fatan Allah ya bama Maryama Haihuwa itama Taga kwanta Aduniya Lokacin Data Dawo da Mastur ba Domin mganarsu Inna Hasiya ba, da Tuni ya ce Maryama ta koma da Mastur Ya bata Shi ta Rikeshi sai bazai iya ja da Abunda iyayansa suka ce ba, Shiyasa yayi Shuru da bakinsa ammh Tsausayin kanwarsa na nan Damkam aransa wanda Ko Barci baya Barinsa yanayi Cikakke.

Haka Rayuwa ta Cigaba da Tafiya da Dadi ba Dadi,Acikin Hakane Allah yayi ma Mahaifiyar Hajara Rasuwa Inno Sakamakon amai da gudawa Kafin Safe ta Cika Sosai Hajara da Habibu suka ji mutuwarta Inna Hasiya da ayya sunyi kuka sosai na Rashin Inno Baba Jibo Shi ya kasance kamar wani Shakiki Har akayi Sadakar bakwai aka waste Hajara ta koma Marainiya sai da Habibu bai barta ta kara kukan Maraici ba ya Tare mata Dukkan Gaban da Zataji yau Bata da iyaye.

Mastur Nada Shekara Hudu a Duniya Hajara ta kara Samun wani Cikin sai dai bai zauna ba Tayi Barinshi Haka Allah ya Tsara ammh Habibu yaji Ciwon Rasa Gudan Jininsa Sosai Fiye da Tunani Domin bai Dora ma kansa Kulafuncin Mastur ba Domin Maryama zai bama Shi Halak Malak.
Cikin Gudurin Allah Hajara ta kara samun wani Cikin Sai dai wannan karon Kusan Lokaci Daya Suka samu Ciki da Maryama Allahu akbar bawa Kada ya Cire rai da Rahamar Ubangiji..
Maryama Tayi kuka Kamar Zata Shide Saboda Murna Sule kam Kamar ya Zuba Ruwa akasa yasha Haka Habibu wanda ya bar Murnan Cikin Hajara ya koma Murnan Samuwar Gudan Jinin Maryamaa,Chan gidansu Sule kuwa Goggo da Zainabu kamar Bakinciki Zai kashesu Domin alokacin ma zainabu na Shayar da karamin Danta mai Suna Auwal Goggo Bata so Maryama ta Haihu ba Har Abada sai dai Kana naka ne Allah na nashi..Na Allah kuma Shine Daidai.

Sai kuma Tunda Maryama ta samu Cikin nan Lafiya yayi mata karanci Yau Lafiya Gobe Ciwo Cikin yana da Laulayi Sosai ta kwanta asibiti yafi Sau Uku Saboda Rashin karfin Jiki Bata samu Zaman lafiya ba sai da Cikinta yakai Wata 6 alokacin ne kuma Hajara Itama ta Sake Barin Cikinta wanda Tasha Wahala kamar bazatayi rai ba Saboda cikin ya zama Gudun Jini Dakyar ta Rayu Wanda Har su Habibu sun Fidda Rai da Hajara sai dai Rai mai alfarma sai gata tashi ammh fa an kashe kudi Tunda Har sai da aka Dangana da Asibitin General na Garin Doguwa,achan ne likitoci suke gaya musu Da wahala Hajara ta kara Haihuwa Saboda Mahaifiyarta Tana da Rauni ba Lalle bane in ta samu Ciki Ya zauna Har ta Haifeshi Saboda Raunin Mahaifan Dake Tare da ita wannan Labarin ya sanyayama su Inna Hasiya Jiki Suna ganin Tayaya Za"a Raba Hajara da Mastur alhalin kuma ba lalle bane ta kara Haihuwa sai dai jin Dadinsu Daya Cikin da Maryama ke Dauke Dashi Kila zai Tada wannan alkawarin da Habibu yayi Tsakaninsa da Ubangijinsa.

Lokacin da Hajara Taji Abunda Likitoci sukace bata Damu ba ta Fauwalama Allah Lamarinsa,Sai dai akasan Ranta Taji ba Dadi Ko bakomai Tana so Ta kara Haihuwa ko Saboda Habibu da Taga ya Damu Tun Lokacin Datayi barinta na Farko. ammh bata da yarda Zatayi Tunda Haka Allah ya Tasara mata Sai dai Tana yi ma Maryama Fatan Allah ya Sauketa Lafiya.

Tunda Maryama ta Shiga watan Haihuwanta sai Lafiya taki ta Kullum Cikin Ciwon kai da Jiri Ashe Tana da Hawan Jini iyayenta ko Habibu basu sani ba Daga ita sai Mijinta ganin Haka yasa Habibu yayi ma Sule mgana kan yana so Maryama ta Dawo gaban Inna Hasiya Saboda Ta samu mai kula da ita Tunda agidan sai dai Sule ya Taimaka mata ba dai Goggo Ko Zainabu Sule bai yi Gaddama ba ya Amince sai dai Goggo Taso Ta Hana Habibu bai tsayama Sauratanta ba Ya samu Tashar Mota sukaje har Gidan ya Dauko Maryama da Duka kayanta Dana Haihuwanta Data Tara Zuwa Gida sai dai su Inna Hasiya suka gansu kwatsam Hakika kuma Taji Dadi Domin Tana Tunanin yadda Maryama Zatayi Haihuwan Fari achan ba wani nata akusa Har Tana Tunani  Tayi ma Ayya mgana Taje Chan Maruka har Maryama din ta Haihu sai gashi ma Habibu ya gama mgana.

Nan Dakin Dake kusa da na su Habibu aka gyara ma Maryama Take Zaune Jiran Haihuwa kowa kula yake da ita ba Ba Baba jibo ba Inna Hasiya ba ba Ya Habibu ba ba Hajara ba Mastur kuwa murna ta kamashi Sai Tsalle yake Goggo Maryama ta Dawo Gidansu da Zama Tunda ta Dawo ya koma Dakinta da kwana ance yaro ma yasan mai Nuna masa kauna Shiyasa Tun yara yaronsa ya Shaida kaunar da Goggonsa kemasa.
Kullum Sule kafin ya Tafi Gida sai ya Biyo ya ga Maryama ya kawo mata tsire ko Nama bata ma wani ci Sai dai Mastur Da su Inna Hasiya Kwanan Maryama Goma agida Ranar Jumma"a da yammah ta Fara Naguda,Nagudan Data Dauketa Har Washegarin asabar bata Haihuwa ba,an kira anguwan zoman Gida sun kasa Kuma gashi ba wanda yasan Tana da Hawan Jini Habibu bai kwana agida ba agarin Doguwa ya kwana yaje siyar da Hatsi Daya Dawo ne yaga Halin Datake Ciki ya Fara Fada yana Ta ma Sule Fada tunda Tun da Maryama ta Fara Nagudan aka Kiraahi aka gayamai Inna Hasiya ne da Ayya keta Shiga da FitaHajara na waje Rumgume da Mastur Dake kuka ganin Halin da Maryama ke Ciki..

Habibu ko Hutawa bai yi ba ya je ya samo Mota suje asibiti kafin ya Dawo Maryama ta Haifi Danta Namiji sai dai kuma me Tuni Jini ya yanke Mata Sai kuma ta Fara Jijjiga Tana Datse Bakinta da Harshenta Cikin Tashin Hamkali Ayyah ta Fito Tana kuka Da Neman Taimako Gabadayansu suka Shiga Dakin Har da Baba Jibo da Hajara da Mastur da Sule ganin Halin da Maryama ke Ciki yasa sule ya Duka da Jinin da komai ya Rumgumeta yana Kiran sunanta Inna Hasiya ita ta Dauki Jaririn Dake kuka ta yanke mai Cibi Ta nadeshi Cikin wani Zani Tana Tsaye Tana kallon Maryaman ta kakkafewa kawai sai ta Juya baya Tana Sharan kwallah Hajarama kuka Take Mastur kuwa Duk da yana karami ne ammh ya Fahimci wani abu mara kyau na Faruwa Baba Jibo ne ya karisa kusa da ita yana Tofa mata addu"a yana Kiran sunanta.
Chapter 5 · 0% Book details