← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 86 OF 94

Sashe 86

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ana saura kwana Biyu Tariyan Anty Hadiza ta iso ita da Umma Tafiyan Jirgi sukayi Daga kaduna suka Hawo Motar Haya suka kariso Zaria Umma tazo ma da Rumana Kayan gyaran Da kuma Turaruka Harda Diza Gabadayansu,Koda suka iso Rumana na asibiti sai dai Data Dawo nan Ta sauka,sai Dare Mastur ya dauketa suka koma Gida Washegari kuma Umma da Anty Hadiza da Inna Zainaba da Balaraban Usman suka zo suka gyara Shashen Diza suka Share suka gyara ko"ina Cikin Kitchen suka Tsaftace suka Fitar da abunda ya Lalace Daddy ya bada kudi Aka yo Cefene aka Cika su a Fridge komai da yaji Diza kuma Ranar taje ta amso dinkunanta Daga Online ta siya kayanta nata dana Mansur karami Nata takai Dinki kwana Biyu har an Dinka mata Masu kyau dataje ne ma Taga Dinkunan Rumanan telan nata yake Fadamata kayan Rumana ne tare suka kawo da Mastur sai gashi Diza taji Haushi Saboda Tun Ranar daya kaita Catering dinta bata kara ganinsa ba Sai Jiya Shima sanda ya Shigo Gaida su Umma da kiran Rumana Lokacin ta gansa Daga Nesa Abun na Damunta ammh sai ta Nuna komai ba komai bane bata so Shedan ya Fara Tasiri akanta Tasan Tana da Kishi sosai ammh Bata so Ta kara Nunashi kan Rumanan.
Washegarin aka tashi da Tariyan Dizan ba wani Taro akayi ba ita kanta Dizan bata gayyaci kuwa ba sai yar"uwarta Meenal ko kwalliya hana Hauwa zuwa Zatayi Tadai saka kaya masu kyau Tana shiga Tana Fita Rumana nan gidan ta Dawo itama akayi Sha"anin da ita,itama ta Shiga ta Fita ita da Mansur karami Diza ma bata sakamai kayan Data siyamai Rumana ce ta Sakamai nata wanda ta siyamai haka Mommy da Hajja da Umma wanda Rumana ta siya musu suka saka.
Bangaran kayan gyaran da Umma tazo musu dashi Diza Tasha nata,Harda wadanda Anty Hadizan tazo mata dashi Rumana tana shan nata ammh a hamkali sanin Diza zata karbi Ragamar Miji Tukunna Rumana tayi gayyah Aisha Bala tazo mata sai yammah Tatafi,Ango Mastur kuwa yana Chan sai aranar ya kira Acp Saleem kumo ya gayamai Halin da ake Ciki ya Dinga zaginsa yana Cemai bai da kirki Mastur dai ya bashi Hakuri Daga karshe suka Rabu kan sai sunzo Shi da Madam bayan yayi mai Fatan alheri,wuni yayi acikin Gida yana kewar Dan"uwansa Yayi kuka sosai Lokaci Daya yayi mai addu"an Rahmar Allah Gashi Rumana taki zama Tatafi ta barsa da kewa abinci kadai tayi mai kafin ta Fita saboda kada ya Zauna da yunwa.

Karfe 6pm na Rana da Daddy da kansa ya kawo Diza Dakinta a karo na Biyu,Tare da Rakiyar Umma da Anty Hadixa sai Rumana data Taho a Motarta ita Dauko Meenal da Inna Zainaba da Mardiya ssi Balaraba,Har shashen suka shiga bayan Daddy yayi ma Diza da Rumana addu"an zaman lafiya kana ya Fita ya barsu anan su kansu su Umma nasu Nasihan suka Dora Duk da sunyi Daga Gida Diza kuka Rumana kuka Ba wanda yasan Dalilim kukansu Rumana Tana kukam Wani Nauyi ne Daya Tokare mata Kirji Na yau Zata bar ma Diza Mijinta ita kuma Dizan Tana kukan jin wani iri da kuka Rashin Mansur,Sai kuma Nauyin Rumana Tana Fatan Kada Allah ya Kara Doramata Kishin Rumana,Tun ada ma da basu Hada Miji ba Ballatana yanzu da Zasu Zauna karkashin Ihuwa Daya.
Kafin Isha"i duka sun watse Fita sukayi bakin Titi suka samu Motar Haya,suka Hau zuwa Hanwa Tunda daddy ya koma Mastur kuma yana Shashen Rumana bai Fito ba yadai ji Shigowarsu,Ya kira Rumana yace tazo tace ba yanzu ba,Zata Shigo ba sai Baki sun Tafi,Mansur karami yana Hannun Mommy ba"a zo dashi ba Sai da suka Tafi kana Rumana Tayi ma Diza Sallama tace Zataje ta Shirya angon nata Zata Rako mata shi yanzu..Diza Mirmishi kawai Tayi Tana Danne Abunda ke Cikin Ranta.

Koda Rumana ta koma Shashenta cikin Bedroom dinta ta iske Mastur Lullube Cikin bargo Data shigo kin kulata yayi wai yayi Fushi sai da tayi ta Lallashi Ta Lura Rigima yake ji Domin Haka ya Tarota ta Fado gadon ya Turmusheta yana Fadin"Ni ko.?ni kekiranki kina jamin aji ko Rumata..?
Mirmishi ta saki Tana kokarin Daidaita kanta take Fadin"Taya zn iya barin su Umma na taho wajenka? Tab salon ace bani da kunya kuma Diza bazata ji Dadi ba yau Tana Amarya nazo na Rike mata ango..!
Kura mata ido yayi itama Idon ta Kuramai Kafin tayi Saurin Janyen Idanuwamta Tana kokarin maida kwallarta ya Shagala da kallonta ta Shammacesa ta Kwace kanta ta Diro Daga kan gadon Tana Fadin"Tashi ka Shiga wanka..Kafin ka Fito na Fito maka da kayan da zaka saka yau ni da kaina zan Shiryaka na Rakaka Har Dakin Amarya Diza Harta Kazan amarci baka da Damuwa na Tanadar maka kaidai kawai Biyayyarka nake nema..!
Yana kallonta Cikin wani Shauki ya Mike tsaye Cikin kasala ya sara mata yana Fadin"Yes Mah..ammh da Sharadin ke Zakimin wankan ko..? Yafada yana Daga mata Gira Dariya Tayi kafin tace"Ok Sir..As you wish.."Kama Hannunsa Tayi ta Turasa Cikin Tiolet yana kokarin Juyiwa ta saki hannunta ta Juya ta Fice da gudu tana Rufomai kofa da Mirmishi ya bita yana Fadin"Zan kamaki ne..!
Tana Fitowa ta Bide Wardrope dinta ta Dauko Sabuwar Farar Shaddan Data Dinkamai Riga da wando da Babban Riga Gezner ce mai kyau dubu 100 ta siyeta,Ta kuma bada aka Dinkamai Batare Daya sani ba ta Siyamai Sabon Agogon na Kamfanin Rado Takalminsa Rufaffae na Fatar Damisa da Hula zanna Bukar,sai Boxers da Singlet sai Turaren da zai Fesa Duka ta ijiyemai ta Fita Zuwa Kitchen ta Dauko kazan ta Dake Cikin Frigde wacce ta Tafasa tun safe ta Gama Hadata Tun Safe Cikin Oven ta sakata ta Fara gasawa Ta Fito da Babban Lemon Holladian mai sanyi Guda Biyu da Kilishin Data Bama Aisha kudi ta Siyo mata Yanzu data Dawo ta Shigo Dashi.
Sai datagama gasa kasan Tsab ta Nannadeta Cikin Poul Paper,Ta Hada Harda Kilishin,ta samu wani kyakyawan kwando ta Sakamai ta jera Harda Lemukan kana ta koma Cikin Bedroom din
Ta iske shi Tsaye yana Duban kayan bai saka ba Yana Sanye da Towel a kugunsa..
Tsayawa Tayi rike da kugu Tana Fadin"Me kake jira baka Shirya ba?lokaci na Tafiya..?
Kallonta yayi kafin yace"Wadanan Kayan fa is for Who..?
Karisowa Tayi Tana Daga kayan Lokaci Daya Tana Fadin"Is Urs..Gudummuwata kenan bazaka je Dakin kanwata da Tsoffin kaya ba..Oya maza Daga hannu ka saka Singlent bana son gaddama Lokaci na Tafiya..!
Shidai kallonta yake yi bai iya ngana ba da Taimakonta ya gama Shiryawa Sai gashi ya Fito Ras ango,Ta jashi gaban madubi ta Fesheshi da Turare Tana Kallonsa kafin ta juya tana Fadin"Kayi kyau ango Diza..!
Rumgumeta yayi Lokaci Daya yana Fadin"Kuma Mijin Rumana ba.."Mirmishi ta saki kafin Tayi mgana yace"Kiyo alwala muyi Sallar Isha"i Tukunnah..!
Batayi gaddama ba Daman Tana neman Hanyar Guduwa kai ta Gyada Kafin ta Sabulr Jikinta ta Shige Tiolet tana Sharan kwallah.
Tana wanka tana kuka Ta Dade kafin ta Fito koda ta Fito ta ganshi Xaune yana jiranta Mirmishi ta sskarmai Kamar yadda Tayi mishi shi ya Taimaka mata ta Shirya itama cikin Shadda Doguwar riga ya jata gaban madubi ya Daura mata Kallabi Lokaci Daya ya Rumgumeta yana Fadin"Thanks So much..Allah ya saka Miki..Allah yayi miki albarka..!
Da ameen take amsawa Tana kokarin saita kanta.
Sallar Isha"i yajasu Jam"i sukayi Suna Idarwa Tara Tayi Rumana ta Mike da Hijabin Jikinta tace"Ka taso na rakaka..Dare yayi kada Diza Tajimu shuru..!
Mikewa yayi ita kuma ta Riko Hannunsa suka Fito Falon tace ya Jirata ta Shiga Kitchen ta Dauko kwamdon ta Fito ta kama Hannunsa Dayake Binta da kallo Zuciyarsa ta kasa Fassara wani mtsayi Rumana gareta acikin Zuciyarsa.

Bata Dire Hannunsa ba sai da ta Rafka sallama Bedroom din Diza Bayan ta Sadashi da Gefen Diza Dake Zaune kan gadon Cikin mayafinta Bata Dago ba sai da ta amsa Sallamansu.
Rumana ta zauna gefen gado Tana Fadin"Amaryanmu..Kiyi Hakuri na Dauki Lokaci..Na Tsaya Shirya angon naki ne kamar yadda nayi miki alkwari Gashi kuma na cika ga angonki nan na kawo Miki Sai ki Rikemin shi Amana .Allah ya baku zaman lafiya da Zuru"a Dayyiba..!
Diza ta amsa da Ameen Mastur ma aransa ya amsan kwamdon ta ijiye gefen gadon Tana nuna ma Mastur da ido kafin ta mike tana Fadin"Asha Amarci Lafiya..Sai da Safe..!
Tafada tana kokarin juyewa jin Hawaye suna kawo mata da Sauri Mastur ya mike ya Rikota Cikin Jikinsa Sai kawai ta Rumgumeshi tana Fidda Numfashi Zuciyarta na Zafin Kishi kamar yadda na Diza ke yi Data Hangensu ta cikin mayafinta kamar Zuciyar ta Zatayi Tsalle ta Fito waje haka take ji saboda Kishi.
Rumana ce ta Fara Zare Jikinta Tuna inda suke ta Ja kumatunsa Tana Fadin"Ka kula da Diza..!
Shima kumatunta ya shafa yana Fadin"Kema ki kular min da kanki..Matata..,!
Kai ta jinjinamai kafin ta Daga kafa Zata wuce yana Kokarin Binta ta Dakatar dashi.."Ka koma wajenta..Zan iya komawa da kaina..!
Daga haka bata tsaya jiransa ba ta Fice da Sauri jin hawayenta suna neman zubowa.
Allah ne yakaita Shashenta Lafiya bata Zube ba saboda Kukan Daya kwace mata Dakyar ta kai kamta Bedroom ta kwanta Tana ta Rusa kuka Lokaci Daya tanaji kamar Zuciyarta Zata Faso waje Innalillahi kawai take maimaitawa acikin Ranta.

*Shakira..*
1/1/22, 18:55 - Maryam Badmsi: *SS....39*

*Kibiya ki karanta cikin Salama Mace mai aji mallakan komai nata take yi bata jiran abun Sata 09069067488*
Chapter 86 · 0% Book details