Sashe 64
Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ita kuwa Diza sai daga Baya kunya da Nadamar abunda ta aikata ya shigeta Tasani bata kyauta ba Uwa uba sai yau taga ta kure Hakurin zama da ita da Mansur yake Tunda take Dashi Bata Taba ganin Fushinsa ba Komai Tayi mai baya maida kansa Iyakata dai kawai yayi mata Mirmishi,Sai gashi yau ta batamai rai har yakai ga Marinta Bata san me ya Shiga kanta ba Kishi ne mai Zafi take ji akan Rumana Wanda bata iya Controling kanta Sai alokacin Taji kunyar abunda ta aikata Meyasa Har yanzu take son Mastur bayan kuma Tana auran Kaninsa..? Dame Mansur ya Rageta..? Babu tunda sukayi aure Shi yake Wahala da Dawainiya da ita Ita me ta sakamai..? babu sai mugun Hali da Rashin Tsausasawa ya kamata ta Mafarka Daga mafarkinta da bazai Taba Tabbata ba aure ya Haramta Tsakaninta Mastur ya kamata ta Fahumci Gaskiya ta Rumgumi Mijinta,yanzu bata da karfin gwiwan Fadama Mommy wani abu Ta Tabbata itace bata da Gaskiya.
Kukan datayi Shi ya kara Dawo mata da Zazzabin Jikinta mai Zafi,Ta na kwance Kan gadonta tana Rawan sanyi ahaka Mommy ta Shigo ta Tarar da ita sai Hankalinta ya tashi ta Kira Daddy ta gayamai Shi kuma yace Takai ta asibiti hankali a tashe Mommy ta tuka Diza zuwa asibitin da suke da Fayel Almadina Suna zuwa aka Karbeta saboda ta galabaita suna Hanya Tana ta Kwarara amai,Taimakon gaggawa aka bata Bayan an Dibi Jininta Domin gwaje gwaje sai aka Saka mata Drip,aka kawota Daki na Musamman Likita yayi ma Mommy Bayanin sai zuwa Gobe zasu koma gida Har sai an gama gwaje gwaje kana Lokacin ita Dizan ta Dawo Cikin Hayyacinta jin Haka yasa Mommy ta kira Mansur ta gayamai Halin da ake Ciki Lokacin yana Gida ne afalon Hajja Shi yake Fada musu ma Diza na asibiti.
Adaran ya Dauko Ayya da Hajja suka je suka Dubata Tana Barci Daga Gidan kuma Mama Fadime Tayi abinci Direba ya Daukota ya kawota suna asibitin Sai ga Daddy da Baba Habibu sun zo Har suka Tafi Diza bata Farka ba Tana ta Barci Mommy aka bari ta kwana da Diza,Su Rumana kuwa sai da safe Taji labari Domin sai Chan Dare Mansur ya Dawo Gidan Mardiya ta kwanta koda ya Dawo Rumana ma na Shashenta sai da safe bayan ya Shirya zai tafi asibitin yake gayama Mata ita ta Shiga Shashen Rumana ta gayamata ta Isketa ta Shirya Zata tafi Asibiti,Hankalinta ya tashi Mansur ya Rigasu yin gaba Rumana ita ta Dauki Mardiya suka Tafi asibitin Bayan ta kira Mommy ta gayamata asibitin da suke da Lambar Dakin.
Sanda sukaje Diza ta Farka Tun Cikin Dare kuma Alhamdulillah Jikin nata da Sauki sai duk tayi wani iri Tun Safe da Likita ya kawo Takardan gwajinta ya Tabbata Tana da Shigar Ciki na Tsawon Wata uku To meya Rage mata..? Ta riga ta zama na Mansur har Abada ya kamata ta Dawo Cikin Hayyacinta Lokacin da Mamsur yazo yaji Labari kamar zai suma saboda Dadi da Farincikin Tun alokacin Taji komai ya kwace mata Taji Duk wani Nauyin Zuciya ya saketa Tsananin Son Cikinta ya kamata Lokaci Daya da Burin Haihuwa da Mansur ko Allah zai bata D"a irin Mansur mai Hakuri da Dadin Zama,so take ta samu kebewa da Mijinta ta bashi Hakuri kuma Tamai alkawarin Zata bama Rumana Hakuri insha Allahu komai ya wuce.
Rumana Tayi mamakin yadda ta gaishe da Diza ta amsa Cikin Sakin Fuska kamar ba ita ba,Saboda ganin wannan Chanjin yass tace Mommy tabi Mama Fadime data kawo Abun karyawa ta koma Gida ita da Mardiya zasu zauna da Dizan har ta Dawo Shine ma Har Diza Ke fadin ba Asibiti zata tafi ba.? Rumana tace ta kira Aisha Bala Zataje tayi mata aikin ta na yau gobe itasai ta Rama mata,Sai Diza Tayi Shuru bata kara mgana ba Mommy tabi Mama Fadime ta koma Gida Mansur ya Tafi suna da Taro anan Sabongarin Zaria Shiyasa ya Tafi.
Rumana ita ta taimaka ma Diza tayi wanka atiolet din Dake Dakin ta Sauya kaya wanda Mansur ya Taho mata dashi ta Hada mata Tea tasha sosai da Buredi,Ta koma ta kwanta Har tana ma Rumana Godiya,Ita kuma sai dai Tayi Mirmishi batace komai ba,Dayake Mommy ta gayamusu Zencen Cikin Dizan Farinciki ya Cika Zukatansu,Ita ta kira Umma Daga chan Sokoto Ta Fadamata ita kuma ta kira Mommy Ta mata yamai Jiki da kuma Murnan karuwa da Diza ta samu suka Rabu Cikin Farinciki.
Su Rumana suna asibitin Har yammah kana Likita ya basu Sallama Lokacin Mommy na nan da Hajja,su suka Tarkato Diza da kayayyaki suka Taho gida Direct gidanta suka wuce da ita,Domin da Farko Mommy taso ta Wuce da ita gida Har ta kara jin Sauki ammh Diza taki tace a kaita Gidan ita taji Sauki Likita ma ya bata mgungunan karin Jini ne kawai sai Shawarwarin yadda Zata kula da Lafiyarta.
Mansur sai dai Mommy tamai waya suna gida Shiyasa daya tashi bai Je asibitin ba ya Dawo gida nan ya iske su Hajja da Mommy da balaraban kawu Usman sai Rumana da Mardiya Tunda suka Dawo Rumana bata Zauna ba ita da Mardiya su sukayi Girki,Diza tace Fate zata sha,Rumana Tayi mata shi Mai Hanta kuma taci sosai yaji Alaiyahu,ganin su yasa su Mommy suka koma gida suka bar Rumana ita da Mardiya itama bata koma Shashenta ba Har sai da Mansur ya Dawo Lokacin Diza ma tasha mgungunanta ta samu Barci Wajen 10pm na Dare Mardiya ta Rakata Shashenta.
Washegari kuma Diza da kanta tace mata Tatafi wajen aikinta Taji Sauki kuma ga Mardiya ba Mtsala Shiyasa Rumana tatafi Bayan Tafiyanta ne sai ga Yan maruka Ashe mardiya ta kirasu ta gayamusu Inna Zainaba da Mariya suka zo Duba Dizan,Kuma Mansur yaji Dadi sosai Domin ance Naka daman naka ne kwana Daya sukayi suka koma Tunda Jikin Diza yayi Sauki sai dan Abunda ba"a rasa ba na Laulayin masu Ciki.
Yan ma"aikatan Diza sun zo Duba Merry da Hauwa sune gaba gaba,Bata da mtsala Dasu su san aikinsu Ragamar komau yana Hannunsu koda bata da Lafiyan nan bata da Damuwa Tunda Kamar tana Wajen indai Merry da Hauwa suna tare da ita.
Mansur da kansa ya Kira Mastur ya gayamai Diza nada Ciki ya Tayasa Murna sosai har yana mai Tsiyan Allah yasa ya Girma yanzu Bayan sun gama Wayar Mastur Kamar zai yi kuka yana Jin Takaichi da Rugugun wani Daci acikin Zuciyarsa Na yadda ya kasa Cire Soyayyar Diza acikin Zuciyarsa Gashi har tana Dauke da Cikin kaninsa Shi kuwa wannan wani irin So ne..? Allah ya waddan wannan Soyayyar batamai amfani ba sam,Ranar bai iya barci ba kwana yayi yana Sallah Tare da addu'an Allah ya Cire mai Soyayyar Diza acikin Zuciyarsa Allah sakamai Soyayyar Rumana ko zai samu ya Sauke Nauyin Dake kansa nashi ya sani In ya Mutu a wannan Halin Allah sai ya Tambayeshi Hakkokin Rumana Daya Danne mata yana Rokon Allah ya bashi Iko da karfin Zuciyar da zai iya Sauke Nauyin Rumana Daya Rataya a Wuyansa.
*****
Bayan Sati Daya Da Kwantar da Diza a asibiti Alhamdulillah Ta samu Sauki Sosai sai dai Amai ne bai Saketa ba,Mardiya ta koma Gida wajen Hajja,Sai dai in Tana Bukatar wani abu ta kira Mommy ita kuma ta saka Direba Ya kawo mata,Rumana ma Tana iya Bakin Kokarinta akan Dizan Ballatana ganin yanzu ta saki Tunda Har yar Hira sunayi Tana Tambayanta wajen aikinta kuma In ta Dafa wani abun kwadayi na masu Ciki Tana kawo ma Dizan Ta karba Taci Tana Godiya Har acikin Ran Rumana taji Dadi sosai,Kuma abunda ya Faru dukkansu basu Furtama kowa ba Hatta shi Mansur din.
Yau din ta kama Lahadi ne Rumana na gida bata je asibiti ba tatashi da Kwadayin Cin Alalen Leda shi Tayi wanda ta Sakamai Kwai da Hanta,da alaiyahu da kanta ma Ta fita tayi Cefenan ta Dawo Shine ta shiga Wajen Diza ta isketw kwance kasala Duk ya Rufeta batayi komai ba Rumana bata koma Shashenta ba sai da ta gyara Ma Diza Dakunanta ta Hada mata Ruwan wanka Ta tasheta tace taje tayi,ta gyara gadon da Bedroom din gabadaya Bata tafi ba Har sai da Diza ta Fito Daga wanka ita kunyar Rumanan take ji kuma ta kara yardan ma kanta ba wai iyayinta bane ke saka ana Yabonta ba ta yardan ma kanta Rumana Tana da kyawun Hali.
Da zata tafi ne take gayamata Alele zatayi sai Diza tace Zataci Don Allah ta kawo mata Shine Dalilin Dayasa bayan Tagama Tayi wanka ta Dauki Kulan Alalen da Yajinta na Tafarnuwa wanda Balaraban Kawu Usman ta Daka mata itama bataci Alalen ba Tace sai taje Shashen Diza su ci Gabadaya.
Diza taji Dadin zuwanta Daman Tana zaune ita kadai ne sai kallo take yi Mansur Tun Safe ya Fita Sai kuma Dare ita sai yanzu take jin Haushin ma Siyasar tashi,Mutim ba Hutu ko Mganar data ke so suyi basu samu Dama ba to in ya Dawo tayi barci Saboda magungunar akwai mai saka Barci da Safe kuma bama takai ga Tashi zai Fice Shiyasa bata samu Lokacin da zasuyi mgana ba ammh yau ta kudiri Niyar yin mgana da Rumana ta bata Hakuri.
Kukan datayi Shi ya kara Dawo mata da Zazzabin Jikinta mai Zafi,Ta na kwance Kan gadonta tana Rawan sanyi ahaka Mommy ta Shigo ta Tarar da ita sai Hankalinta ya tashi ta Kira Daddy ta gayamai Shi kuma yace Takai ta asibiti hankali a tashe Mommy ta tuka Diza zuwa asibitin da suke da Fayel Almadina Suna zuwa aka Karbeta saboda ta galabaita suna Hanya Tana ta Kwarara amai,Taimakon gaggawa aka bata Bayan an Dibi Jininta Domin gwaje gwaje sai aka Saka mata Drip,aka kawota Daki na Musamman Likita yayi ma Mommy Bayanin sai zuwa Gobe zasu koma gida Har sai an gama gwaje gwaje kana Lokacin ita Dizan ta Dawo Cikin Hayyacinta jin Haka yasa Mommy ta kira Mansur ta gayamai Halin da ake Ciki Lokacin yana Gida ne afalon Hajja Shi yake Fada musu ma Diza na asibiti.
Adaran ya Dauko Ayya da Hajja suka je suka Dubata Tana Barci Daga Gidan kuma Mama Fadime Tayi abinci Direba ya Daukota ya kawota suna asibitin Sai ga Daddy da Baba Habibu sun zo Har suka Tafi Diza bata Farka ba Tana ta Barci Mommy aka bari ta kwana da Diza,Su Rumana kuwa sai da safe Taji labari Domin sai Chan Dare Mansur ya Dawo Gidan Mardiya ta kwanta koda ya Dawo Rumana ma na Shashenta sai da safe bayan ya Shirya zai tafi asibitin yake gayama Mata ita ta Shiga Shashen Rumana ta gayamata ta Isketa ta Shirya Zata tafi Asibiti,Hankalinta ya tashi Mansur ya Rigasu yin gaba Rumana ita ta Dauki Mardiya suka Tafi asibitin Bayan ta kira Mommy ta gayamata asibitin da suke da Lambar Dakin.
Sanda sukaje Diza ta Farka Tun Cikin Dare kuma Alhamdulillah Jikin nata da Sauki sai duk tayi wani iri Tun Safe da Likita ya kawo Takardan gwajinta ya Tabbata Tana da Shigar Ciki na Tsawon Wata uku To meya Rage mata..? Ta riga ta zama na Mansur har Abada ya kamata ta Dawo Cikin Hayyacinta Lokacin da Mamsur yazo yaji Labari kamar zai suma saboda Dadi da Farincikin Tun alokacin Taji komai ya kwace mata Taji Duk wani Nauyin Zuciya ya saketa Tsananin Son Cikinta ya kamata Lokaci Daya da Burin Haihuwa da Mansur ko Allah zai bata D"a irin Mansur mai Hakuri da Dadin Zama,so take ta samu kebewa da Mijinta ta bashi Hakuri kuma Tamai alkawarin Zata bama Rumana Hakuri insha Allahu komai ya wuce.
Rumana Tayi mamakin yadda ta gaishe da Diza ta amsa Cikin Sakin Fuska kamar ba ita ba,Saboda ganin wannan Chanjin yass tace Mommy tabi Mama Fadime data kawo Abun karyawa ta koma Gida ita da Mardiya zasu zauna da Dizan har ta Dawo Shine ma Har Diza Ke fadin ba Asibiti zata tafi ba.? Rumana tace ta kira Aisha Bala Zataje tayi mata aikin ta na yau gobe itasai ta Rama mata,Sai Diza Tayi Shuru bata kara mgana ba Mommy tabi Mama Fadime ta koma Gida Mansur ya Tafi suna da Taro anan Sabongarin Zaria Shiyasa ya Tafi.
Rumana ita ta taimaka ma Diza tayi wanka atiolet din Dake Dakin ta Sauya kaya wanda Mansur ya Taho mata dashi ta Hada mata Tea tasha sosai da Buredi,Ta koma ta kwanta Har tana ma Rumana Godiya,Ita kuma sai dai Tayi Mirmishi batace komai ba,Dayake Mommy ta gayamusu Zencen Cikin Dizan Farinciki ya Cika Zukatansu,Ita ta kira Umma Daga chan Sokoto Ta Fadamata ita kuma ta kira Mommy Ta mata yamai Jiki da kuma Murnan karuwa da Diza ta samu suka Rabu Cikin Farinciki.
Su Rumana suna asibitin Har yammah kana Likita ya basu Sallama Lokacin Mommy na nan da Hajja,su suka Tarkato Diza da kayayyaki suka Taho gida Direct gidanta suka wuce da ita,Domin da Farko Mommy taso ta Wuce da ita gida Har ta kara jin Sauki ammh Diza taki tace a kaita Gidan ita taji Sauki Likita ma ya bata mgungunan karin Jini ne kawai sai Shawarwarin yadda Zata kula da Lafiyarta.
Mansur sai dai Mommy tamai waya suna gida Shiyasa daya tashi bai Je asibitin ba ya Dawo gida nan ya iske su Hajja da Mommy da balaraban kawu Usman sai Rumana da Mardiya Tunda suka Dawo Rumana bata Zauna ba ita da Mardiya su sukayi Girki,Diza tace Fate zata sha,Rumana Tayi mata shi Mai Hanta kuma taci sosai yaji Alaiyahu,ganin su yasa su Mommy suka koma gida suka bar Rumana ita da Mardiya itama bata koma Shashenta ba Har sai da Mansur ya Dawo Lokacin Diza ma tasha mgungunanta ta samu Barci Wajen 10pm na Dare Mardiya ta Rakata Shashenta.
Washegari kuma Diza da kanta tace mata Tatafi wajen aikinta Taji Sauki kuma ga Mardiya ba Mtsala Shiyasa Rumana tatafi Bayan Tafiyanta ne sai ga Yan maruka Ashe mardiya ta kirasu ta gayamusu Inna Zainaba da Mariya suka zo Duba Dizan,Kuma Mansur yaji Dadi sosai Domin ance Naka daman naka ne kwana Daya sukayi suka koma Tunda Jikin Diza yayi Sauki sai dan Abunda ba"a rasa ba na Laulayin masu Ciki.
Yan ma"aikatan Diza sun zo Duba Merry da Hauwa sune gaba gaba,Bata da mtsala Dasu su san aikinsu Ragamar komau yana Hannunsu koda bata da Lafiyan nan bata da Damuwa Tunda Kamar tana Wajen indai Merry da Hauwa suna tare da ita.
Mansur da kansa ya Kira Mastur ya gayamai Diza nada Ciki ya Tayasa Murna sosai har yana mai Tsiyan Allah yasa ya Girma yanzu Bayan sun gama Wayar Mastur Kamar zai yi kuka yana Jin Takaichi da Rugugun wani Daci acikin Zuciyarsa Na yadda ya kasa Cire Soyayyar Diza acikin Zuciyarsa Gashi har tana Dauke da Cikin kaninsa Shi kuwa wannan wani irin So ne..? Allah ya waddan wannan Soyayyar batamai amfani ba sam,Ranar bai iya barci ba kwana yayi yana Sallah Tare da addu'an Allah ya Cire mai Soyayyar Diza acikin Zuciyarsa Allah sakamai Soyayyar Rumana ko zai samu ya Sauke Nauyin Dake kansa nashi ya sani In ya Mutu a wannan Halin Allah sai ya Tambayeshi Hakkokin Rumana Daya Danne mata yana Rokon Allah ya bashi Iko da karfin Zuciyar da zai iya Sauke Nauyin Rumana Daya Rataya a Wuyansa.
*****
Bayan Sati Daya Da Kwantar da Diza a asibiti Alhamdulillah Ta samu Sauki Sosai sai dai Amai ne bai Saketa ba,Mardiya ta koma Gida wajen Hajja,Sai dai in Tana Bukatar wani abu ta kira Mommy ita kuma ta saka Direba Ya kawo mata,Rumana ma Tana iya Bakin Kokarinta akan Dizan Ballatana ganin yanzu ta saki Tunda Har yar Hira sunayi Tana Tambayanta wajen aikinta kuma In ta Dafa wani abun kwadayi na masu Ciki Tana kawo ma Dizan Ta karba Taci Tana Godiya Har acikin Ran Rumana taji Dadi sosai,Kuma abunda ya Faru dukkansu basu Furtama kowa ba Hatta shi Mansur din.
Yau din ta kama Lahadi ne Rumana na gida bata je asibiti ba tatashi da Kwadayin Cin Alalen Leda shi Tayi wanda ta Sakamai Kwai da Hanta,da alaiyahu da kanta ma Ta fita tayi Cefenan ta Dawo Shine ta shiga Wajen Diza ta isketw kwance kasala Duk ya Rufeta batayi komai ba Rumana bata koma Shashenta ba sai da ta gyara Ma Diza Dakunanta ta Hada mata Ruwan wanka Ta tasheta tace taje tayi,ta gyara gadon da Bedroom din gabadaya Bata tafi ba Har sai da Diza ta Fito Daga wanka ita kunyar Rumanan take ji kuma ta kara yardan ma kanta ba wai iyayinta bane ke saka ana Yabonta ba ta yardan ma kanta Rumana Tana da kyawun Hali.
Da zata tafi ne take gayamata Alele zatayi sai Diza tace Zataci Don Allah ta kawo mata Shine Dalilin Dayasa bayan Tagama Tayi wanka ta Dauki Kulan Alalen da Yajinta na Tafarnuwa wanda Balaraban Kawu Usman ta Daka mata itama bataci Alalen ba Tace sai taje Shashen Diza su ci Gabadaya.
Diza taji Dadin zuwanta Daman Tana zaune ita kadai ne sai kallo take yi Mansur Tun Safe ya Fita Sai kuma Dare ita sai yanzu take jin Haushin ma Siyasar tashi,Mutim ba Hutu ko Mganar data ke so suyi basu samu Dama ba to in ya Dawo tayi barci Saboda magungunar akwai mai saka Barci da Safe kuma bama takai ga Tashi zai Fice Shiyasa bata samu Lokacin da zasuyi mgana ba ammh yau ta kudiri Niyar yin mgana da Rumana ta bata Hakuri.