← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 66 OF 94

Sashe 66

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 6 min read

Wannan Dalilin Shi yasa ya Dade agida bai koma ba Har sai da Baba Habibu yayi sati Daya a asibitin aka sallameshi,suka Dawo Gida zuwa Lokacin Hatta yam Maruka sun so gaisheshi Baba Sule da yan"uwansa Umma da Abba ma Daga Sokoto sun Taho sun Dubashi Inna karime ma Tazo ita da Mijinta Mommy da Daddy kuma Koda yaushe suna asibiti Tare dashi Diza ma Haka Rumana kuma Daman anan take aiki Haka abokan aikinta keta zuwa gaishe shi Domin ta sanar dasu Baban Mijinta ne sai alokacin wasu suka ga Mijin Rumana Mastur,Shima Din alokacin ne yaje Har bangaran Datake aiki yagani Abunda yabama Rumana mamaki Batayi mamaki ba sai Taga in ya Dawo gida yayi wanka Da Safe saboda Achan yake kwana Tare da Baba Habibu,Mansur yayi nacin ya Dinga kwana ya Hanashi In Tana gida bata Fita ba sai yace ta Jirasa su koma tare in sun koma yammah Tayi zata koma gida sai ya Dauketa ya maidata watarana kuma Mansur ya maida su Gida ita da Diza haka sukayi tayi Har yaji Sauki ya koma gida Hajja da su kansu suna kara Kula dashi.

Abunda ya kara bama Mastur Tsoro da mamaki Abu Daya ne zuwa Biyu,alokacin da Baba Habibu ke asibiti Rumana bata zuwa Hannu Rabbana sai tayi abinci Tazo dashi haka bayan ya koma gida ma haka bata zuwa Hakanan abunda ya bashi Tsoro bai Taba ganin alert din ta Cire ko Naira Biyar Daga cikin kudinsa ba,To da wani kudi take amfani..? Yaji Tsoro ya Shigesa kada fa yazo ya mutu ya shiga Wuta saboda Hakkin Rumana Dake kansa sai ya yanke Shawaran yi mata mgana.

Aranar tare suka Dawo Daga Gidan su Hajja dukkansu,Ita taje wajen aiki sai da ta Dawo ta Biyo,ta iske ma su Inna Zainaba sunzo da Maryamu da Mariya Harda Sakina,Diza kuma Daman anan ta isketa,nan aka Hadu ana ta Hira anan ne ma take jin Maryama ta samu Miji Zatayi aure acikin garin Kano kowa ya Tayata Murna sosai,Har anyi mgana an sska Ranar auran nan da wata Biyu,ita kuma Mardiya Daman an Biya mata Jarabawan Da Jamb saboda Achan maruka tayi karatu har matakin Jss3,Shiyasa bayan tazo nan din Mastur yace sai dai Tayi Tsallake zuwa gaba saboda ta girma Shiyasa ya saka Mansur ya samar mata lesson Teacher Shiyasa abun yazo da sauki.

Achan suka kai Dare sai Wajajen 10pm kana suka koma Gida Dukkansu Diza Tana Motar Mijinta ita kuma Rumana Da Motarta taje asibiti sai ta barta nan Gidan Hajja Mastur ya Dauketa a nashi Zuwa Gida suna zuwa Kowa ya nufi Bangaransa Hakance ta Faru da Rumana Domin Dakinta ta Shige Shima Mastur ya Shiga Dakinsa sai da yayi wanka ya Sauya kaya zuwa na Barci Riga da wando masu Ruwan Toka,kai Tsaye Bayan ya Fito Daga Dakinsa ya Nufi Dakin Rumana jin bai ji Motsinta ba Bayajin yunwa Domin Dukkansu sunci Abincin da Hajja ta Dafa musu.

Tana Tsaka da Karatu Domin Tana da wata Seminar gobe din Sanye take da Riga Doguwa mai Budadiyar gaba wacce keda madaurin Gaba Bata saka Dankwali ba Sai dai ta Tufke gashinta,Fuskarta Sanye da Siririn gilashinta mai kara mata karfin gani System ne agabanta akan gado Tana karatu Taji Sallamarsa da Shigowarsa Dakin Da mamaki ta Dago Tana kallonsa kamar yadda Shima yake kallonta Ganin bata bsshi Izinin karisowa ba yasa ya Coge Daga Kofar dakin Hannunsa Saman Kirjinsa yace"Baki bani Izinin Shigowa ba Madam..?
Mamakin kalamansa Taji Da Sauri ta muskuta kunya Take ji Saboda Rigar jikinta Gaban Nonuwanta suna Bude ne shi bai ma lura da Kirjin nata ba Dayake ba Kodayaushe yake kula da irin wadanan Abubuwan ba Tunda ya Rasa Diza.
Da sauri tace"Ah Haba..Har sai na baka izinin zama kaima ai Dakin ka ne..!

Karisowa yayi har gefen gado kana ya zauna yana kallon System din gabanta kafin yace"Kina wani aiki ne..! ? Rumana tace"A"a karatu nake..Cikin wannsn satin zan gama Seminar ta.."Kai ya Rausaya kafin yace"Allah ya bada sa"a..!
Ta amsa da Ameen a kasan Ranta sun Kara Daukan tsawon Lokaci kafin ya kalleta yana Fadin"Duk iya Tsawon wannan Lokacin meyasa baki Taba taba ko Sisi Cikin Katin Bankin da na baki ba..?
Daga sama Taji Tambayar shiyaasa ta Dago Tana kallonsa acikin Ranta Tana Ayyana Daman yana Sane da bata taba Taba ko Biyar dinsa ba"Kinyi Shuru..?
Ya katse mata Tunani da Sauri ta Sauke Numfashi kafin tace"Ina da kudi a Hannuna ne..Abba yana Turomin kudi duk wata kuma akwai Kudin da gwannati Take Biyana duk wata na Intenship din da muke yi Shiyasa kaga ban Taba amfani da kudin Daka barmin ba..!
Yana kallonta Har ta gama Bayaninta sai yaji ssm bai kyauta ba Shiyasa ya kara Tausasa Murya yana Fadin"Duk na sani..Ai ba Abba ke da iko akan ki ba..ni ke da alhakin Baki komai na Rayuwar nan Rumana Duk da auranmu ba yadda mukayi Tsammani bane ammh ai Aure sunansa aure kuma Hakkin kowannenmu yana Rataye ne a Wuyanmu Ko bakomai ki bani Damar sauke wannan Nauyin naki Don Allah.."Har yagama Jawabinsa kanta na kasa Bata Dago kanta mamakinsa ya Cikata Daman wai yasan da ita Matarsace ko kuwa yau kawai Dadin Bakin su Maza ne ya Motsa..?
Jin tayi Shuru yasa ya mike tsaye yana Goye da Hannayensa kan Kirjinsa yace"Kada ki kara amfani da wani kudi in ba Cikin Katin Bankin da na baki ba Kinji ko..? Bata da Zabi illah ta Dagamai kai Cikin Gamsuwa kai ya gyada kafin yace"Gud..Kuma Komai kike Bukata ki kirani ki Fadamin Plz.."Cikin mamakinsa tace"Insha Allahu.."Daga haka yayi mata sallama ya Fice Ta Bishi da kallon mamakinsa Bata iya Dora wannan al'amarin nashi a komai ba sai a Dadin bakin Namiji kawai.
Haka kuwa akayi Domin Kafin ya Tsfi sai da ya Dauketa suka Shiga kasuwa yayi Cefene kuma suka Shiga Shop ya siya mata abubuwan amfani sosai su pad ne,da kayan kwalama Duk dai yaji ya Sauke Nauyin Dake kansa Ba Laifi Rumana taji Dadi Sosai ko Bakomai Zakaji Dadi yau wanda bai Damu da Damuwarka ba ya Damu dakai koda Sau Daya ne.
Bai tafi ba sai da yaga Jikin Baba Habibu ya samu kana ya koma Bayan ya tura ma Baba Sule kudi kan Hidiman Bikin Maryama ita ma Maryama din ya bata kudi yace ta Siya abubuwan da Zata kara Koda Mansur yaje chan maruka ya iske komai ya kamallah daga Taimakon Dan"uwansa kuma Yayansa haka Baba Sule keta kwararamai addu"a Shi kanshi Mansur yana alfahari da samun Dan"uwa kamar Mastur Domin Dayane shi acikin Dubu abunda ya kara musu kadan ne Domin Yayan nashi ya gama yin komai.

Ba Laifi Mastur yayi kokarin gyara Zamantakewarsa da Rumana yana kiranta Bayan kwana Biyu zuwa uku yaji Lafiyanta da kuma Tambayanta in akwai wata Damuwa,Hakan ba karamin Farantama Rumana rai yayi Shiyasa itama takan Kirashi kafin ya kirata in taji Shuru,Saboda kada yaga kamar Bataji mganarsa ba yasa taje ta Cire 30k acikin kudinsa Ta Siyama mardiya kaya su Atamfa da leshi Da Sauran kayan amfani Saboda ita babu abunda bata dashi Ta Taba kudin ne saboda ya samu Sukuni acikin Ransa kuma Yaji Dadin haka sai yaji kamar Rumana ta Sauke mai wani Nauyi ne.
Chapter 66 · 0% Book details