← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 94

Sashe 44

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 7 min read

A Dove event Center,Dake kwangila aka Shirya Dinner din Tuni Motarsu Tayi gaba Sauran Motoacin suka Biyo baya wasu abokan su Mansur din duk suna Chan su Mus"ab ne suka Taho Dasu Basma da Sauran Mutane Saboda Dare yayi suna zuwa ba bata Lokaci suka Shiga Mansur ya Rike Hannun Diza da zasu shiga ammh Mastur ki yayi da Suka matsamai yace zai koma mota Dole suka barsa suka jera batare da sun rike Hannuwan juna ba Wajen ya Hadu soai Wajen Zamansu Daya ne Kowa da kujeran sa saboda ba Lokaci gabatarwa kawai Mc yayi aka Fara Gabatar da Tarihin Mastur wanda Saleem kumo ya bada,Sai Rumana wacce Basma ta bada Mansur kuma Sagir ya bada nashi Diza kuna Meena Daganan aka ci abinci sai aka Saka Kida akace Amare da angwayen su Fito Diza dai da Mansur suka Fito ammh Mastur yace baya Rawa ganin suna Lallabasa Dole suka kyaleshi Anyi Ruwan kudi da Diki Sosai yan Siyasa da yan jam"iyar su Mansur sun yi Halin Girma bayan nan Sun yanka Cake Mansur dai shi yake Tafiyar da komai Diza kuma Bata da yadda Zatayi Rumana kuwa Tun awajen Dinner ta Fara Sarewa na ganin nata angon kwatakwata baya mata Rawan Jiki Cake ma bai yanka ba yace bashi da Lafiya kuma gasiiya kansa kamar Zai Tsage 11:30pm Daddy ya kira yace su Dawo gida Za"a mika Amare Dakunansu Daman Mastur ya gaji da Zama su suka Fara yin gaba Shi da Saleem Sai dai aka Nemeshi aka rasa Rumana ma Mansur da Diza suka Dawo da ita Dole dai kanwar Naki Dare yayi akace abari sai Gobe akai Amaran Gidajensu.
Dukka Amaran A Dakin Mommy na sama suka kwana ammh Daki Dabam Dabam,Rumana ita da Basma suka kwana Anty Saratu suna Gidan Hajja chan suka kwana Rumana ta kwana Tunanin me ya Samu Mastur ne Taga kamar baya Farinciki kamar yadda Mansur yake ba Bata da mai bata amsa ba Dole Tayi Shuru.
Tun safe akaFara Shirin mika Amaran Dakunansu Daman Rumana Daga chan Sokoto matan kannen Umma sun zo da kayan gara Damota guda Snkas kuma Mommy Tayi musu ita da Diza wanda a Diza Catering dinta akayi komai,Biyu suka Raba kayan suka bama su Hajja Hakama na Bangaran Diza Baba Habibu nata Fada abu kamar Ba Gida Daya ba,Dukkansu Shigar Lifaya sukayi Da za"a kaisu Gidansu Daddy ya saka musu albarka Baba Habibu ma haka Baba Sule ma ya saka musu albarka Hajja da Ayya ma sun saka albarka Ayya dai tace kafarta kafar Amare sai ta Rakasu,Daman tuni su Wasu Mutanen suna cham Gidan karfe 10am na safe Aka tafi kai Amare Dakunansu Amotar Daddy aka Kaisu Inda Mus"ab ya Tukasu Mansur da Mastur suna Gida Mansur dai yana wajen Motocin Rakiyan Amaran suka Tashi,Ammh Mastur yana Ciki yana Warware gajiya ga Ciwon kai Duk bayajin Dadin Jikinsa.

Motoci Har cikin Haraban katom Gidan suka Shiga Diza itace karama sai da ta Fara Raka Rumana Shashenta wanda yaji Kayan alfarma kallon Sashenta Purple and White ne,Duka Daga Falo Har Bedroom Har sai da suka Danganta da kan gadonta na alfarma Kama suka Hadu suka Mika Diza Ita kuma nata Shashen blue and Ash ne Lokacin Da Diza Tajita Zaune kan gadon Auranta sai ta saka kuka Yi takeyi ba Saurarawa kowa ya Zata kukan Rabuwa da gida ne nan kuwa ba wanda ya sani Tana kukan Rasa Muradin Ranta ne na Har Abada.

Ranar anan akayi idasa Bikin Abinci ma da komai Duka Daga Gida Mommy ta aiko da komai,Sai Bayan La"asar akayi Walima a Haraban Gidan inda aka Gayyato Malama Safiya Muhammad Ba"are tayi Wa"azi ga amare wadanda sukayi Shigar Bakaken Jallabiya anyi Rabon abuwawan ci sosai Dama na Sha sai wajen 6pm aka tashi aka Fara Shirin barin Amare bayan Kowacce an gyara mata Shashenta yana Tashin kamshi Rumana tana Tare da Basma suna Sallama wacce Zata koma kaduna Gobe ammh Rumana tace kafin Tatsfi ta Biyo,Su Sagir ne suka zo da Motoci kwasan Mutane su maidasu Gida Bayan Dukkansu sunsha Nasihan Zaman lafiya da kuma Hakuri da juna duk da ba Mazajensu Daya ba ammh kuma Zasu zauna Waje Daya ba Abokin Mastur ko Daya Saleem ne kuma ya Wuce katsina Dazu Sargent Inuwa ne kadai ke kaida da kawo da Motan Yallaban.

Koda akayi mangariba Gidan ya Koma Tsit kowacce abarta ita kadai ashashen ta tana kuka Rumana Haka ta rike Anty Saratu Tana kuka Dakyar ta kwaci kanta Sai da Hajiya Adama ta tsawatar haka itama Diza Tayi ammh ita kukanta Harda Rashin Masoyinta.
Har yanzu gidajen Biyu acike suke Saboda Baki sai gobe kowa zai koma Gidansa Basma Tana Tare da Meena yar"uwa Diza nan Gidan Su Diza zasu kwana.

Bangaran angwaye kuwa Mansur Sai Zumudi yake yau zai Shiga Dakin Amarya yayin da Bangaran Mastur ji yake kamar Rayuwarsa ta Shiga Halin kila wa kala na har Abada kuma kenan.

*Shakira...*
1/1/22, 18:54 - Maryam Badmsi: *SS...21*

"Inda Mastur yasan Hanyar da zai Zillema auran da Haduwa da Rumana Amaryasa Da Tuni yayi sai dai ba mafita kuma ba Hanya,Dole yanaji yana gani ya Shirya cikin Sabuwar Shadda mai Ruwan Kasa,duk cikin wadanda Mansur din ya Dinkamai sai dai yau kowa kalan nashi ya saka Mansur Mai Ruwan Bula ya saka abunsa kowa ya gansa yasan yana Farinciki Sabanin Mastur kamar wani mara Lafiya mara kuzari mara karkashi mara Fara"a kamar wanda yake cikin wani Halin ni yasu kowa ya gansa sai yace baya fara"a kamar ango Duk da kowa yasan yanayinsa na lokacin ya bambamta da yadda Kowa ya saba ganinsa.

Mansur shi ya bama Sagir kudi yaje ya siyo kaji gasassu leda Biyu,Kowanne da Kilishi da Madaran Holladian mai Sanyi,sai Lokacin ya Sallami Sagir Mus"ab dai yana nan sai da Safe zai Hau jirgi ya koma,Da ace mastur yana da mafita kwanciyarsa zai yi a Dakinsa bayan ya kulle kansa ammh Ina bayaso yayi wani abun da za"a Tambayeshi meyasa yayi haka..?bai Shirya amsa wadanan Tambayoyin ba.

Kafin su wuce sai da suka Shiga Wajen Hajja da Ayya suka saka musu albarka Kana suka je wajen Baba Habibu da Mallan Sule Da Daddy da suke Tare a BQ,sukayi musu Nasiha suka sa Musu albarka,Daganan kowa ya Shiga Motarsa da Ledan kazansa Har zasu Tafi ma Mansur yaga Mastur zai Shiga Mota bai Dauki Jakar kayansa ba yasa ya Tunamai sai Lokacin ya Tuna ya koma Daki ya Dauko Jakarsa Gabadaya Mansur Mus"ab zai Rakasa Shi kuma Mastur shi kadai ya Shiga Motarsa Motar mansur ne ke gaba nashi na Binsu abaya Har Zuwa Hanwa Lowcost,sukayi Hon megadi yazo ya wangale musu get suka Sulala da Motocinsu ciki megadi na ganinsu ya Gane Zaratan Samarin Gidan ne Wanda Daddy ya Riga yayi mai Bayani.
Shi ya ruga yaje ya Bude ma Mastur Mota Mansur kuma da kansa ya Bude Daman ya kosa a kage yake ya kosa yagansa Dagashi Sai Diza hakan ne Kadai Burinsa da Farincikinsa.
Bayan sun Firfito Suka gaisa da Megadin,ba wani babba bane iyakarsa sa"ar Mastur da Mansur Gabadaya Mastur bai san ma ina ne Barayinsa ba Sai da Mansur ya nuna mai kansa kawai ya Dafe Ya Taka zai wuce Mansur ya Bisa da kallo yana Fadin"Yaya ina zaka kuma..?
Baka Dauki Ledan Kazan Anty tawa ba..Kuma baka Dauki Jakar kayanka ba..?
Sai Lokacin Mastur ya Tuna Da Sauri ya Dawo ya Bude Mota ya Dauki Jakar da ledan Mus"ab da mansur suka kalli juna Cikin mamaki Mastur kansa ya Dafe kafin yace"Na manta sam.."

Mansur ya kariso kusa dashi Yana Fadin"Ko mu Rakaka ne Yaya..? Da sauri yace"A"a ku barshi kawai kaima Amaryanka nachan na jiranka kada ka Damu.."Mansur ya kallesa sosai kafin yace"Meke damunka yaya..? Tunda aka Fara Sha'anin nan naganka ba yadda na sanka ba..?
Mastur ya Dago Idanuwansa yana kallon Mansur kafin yace"Wlh gajiya ce..Akwai gajiya Sosai ajikina.."Mansur ya Rausayar dakai yana Fadin"Ashiga a huta ya Mastur..Ina Tsausayama Anty Rumana yau duk zaka sauke gajiyanka akanta kenan.."Da Sauri Mastur ya waro ido yana kallonsa Dariya Mansur ya saka Sai da Mastur ya Daki Kafadansa yana Fadin"Kai yaron nan fa naga alaman ka Fara Lalacewa Tunda ka Shiga Siyasa.."yafada yana Turesa baya Mansur kuma na Dariya juyawa yayi kawai yana Fadin"Sai da safe.."Mus"ab ne dake gefe ya Daga murya yana Fadin"Allah Tashe mu Lafiya Ranka ya Dade.."Mastur yana jinsa sai ya waigo kawai ya Daga mai Hannu Suna kallo ya Kwankwansa Kofar Falon kadan kafin kuma ya Tura ya Shiga Ya maida kofar ya Rufe Sai da suka ga Shigarsa Kana Mansur ya wuce gaba Mus"ab yabi bayansa suka Nufi kofar da Sada Sadasu da bangaran Diza Amarya wacce ke chan Tana Rafzan kuka.
Chapter 44 · 0% Book details