← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 94

Sashe 13

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ganin yayi mganan ba wasa yasa Mansur din ya Mike yana kallon Diza yace"kawo Yar bebin nakai Dakin Hajja..In mun Yi sallah sai mu Cigaba da wasan.."Make abunta Tayi taki basa ganin haka yasa yace Mata"kina son ya Mastur ya Dake ki..? Sai ta girgiza kai Kamar Zatayi kuka Da Sauri yace"Toh kaima Aiya ta ijiye Miki Kizo muyi alwala."Ba musu Tatafi ta kaima Aiya Datagama Alwala Zata Shiga Ta karba Tana Fadin"Maza kiyo alwala Kizo muyi sallah kawata.."Baki ta washe mata ta amsa da Toh Tatafi ta koma Wajen Mansur Lokacin Har Mastur ya idar da alwalansa Sai Mansur ya mika mata wata karamar Buta Shima ya Dauki Nashi Suka Fara alwala In Tayi Kuskure sai ya gyara Mata Har suka Idar Mastur na Gefe yana Kallonsu suna Idarwa Hajja na Fitowa Daga Madafa Mastur yace"Hajja ki kaita Tayi sallah zamu tafi masallaci. ".
Daga Haka yaja Hannun Mansur suka Fice wanda ke tta waiwayanta Har yana mata Bye Bye.

Hajja Ta kaita Dakin Aiya ta Bata wani karamin Gyale ta yafa mata Sukayi sallah Tare da Aiya suna idarwa Ta zauna tana Motsi da baki ganin Aiya na Addu"a itama Sai ta Fara Motsi da baki Aiya na kallonta yarinya sai ta Burgenta Sunanan Su Mansur suka Dawo Daga masallacin saboda Sauri Baya yabar Mastur ya Rugo Zuwa Gida ya Fada Dakin Aiya yana Kiran Diza Tana ganinsa ta Mike Tana Murna Aiya ta Dauko Musu Bebin suka Cigaba da wasansu,Mastur kuwa yana Dawowa ya koma Daki ya Cigabq da Karatunsa.

Har Hajja ta tuka Tuwo taje Tayi Salla ta Dawo ta kwashe ta saka Ruwan Zafi na wanka Tazo ta Zubama Aiya nata ta sakama Diza nata Duk da bata da Tabbacin Zataci,Sai Mansur yace ta Hada musu sai ta sakama Mastur nashi Dabam Kamar yadda suka saba Ta Shinfida katuwar Tabarma suka Zauna Abunda ya bama Aiya da Hajja mamaki yadda Diza taci Tuwo Harda kari ita da Mansur Suna gama cin Tuwon kenan aka Kira salla wannan karon ma Mastur ya tasa Mansur suka Tafi masallaci itama Dizan sukayi sallah Tare da Aiya Sun idar kenan sun Fito su Mansur suka Dawo suka kara Murna Diza da Mansur Har Hajja da Aiya na mamaki koda yake wasa ne ya Hadu da wasa ne.

Mallam Habibu ya Dawo ya iske Diza yarinyan Sam bata da Bakunta ta saki Jikinta Ya siyi ma Mansur Sweet sai aka Raba Musu Aiya ce ke koramai Bayanin Shigowar Hajiya Asiya da Abunda ya wakana Cikin Fara"a yace"Allah sarki..Mutanen Kirki ne Allah ya bar Zumunci.."Yana cikin Cin Tuwo Sai ga Wata yar Matashiyar yarinya Wacce bata Wuce Shekaru 30 ba ta Shigo da sallama bayan sun gaisa dasu Hajja tace sunanta Fadime yar aikin Gidan Hajiya Asiya an ce Tazo Tatafi da Diza Dizan na ganinta ma ta Fara Kiran sunata alamun sani Data Fahimci Tafiya da ita za"ayi sai ta Fara kuka Dakyar da Lallashi Ta yarda tabi Fadime Mansur din kansa Kamar zai yi kuka Ranar da Wuri yayi barci haka itama Dizan Daga bangaranta..

Washegari Karfe 9am Sai ga Fadime ta kawo Diza sai dai Su Mansur suna makaranta Fadime take Fadin tun Safe Take kukan sai an kawota Wajen Mansur Hajja ta karbeta tace sun Tafi makaranta ammh sun kusa Dawowa zata zauna..? Diza tace eh sai Fadime tatabi ta barta Wajem Hajja Aiya ta Fito Tajata Daki Suna ta Hira kamar Wata babba Duk da yarinya ce ta Fahimci yar gatace Diza ta gaba da baya.

_Albishirunku Masoyana wannan karan na bude muku wani Shashi na musamman Saboda ku..Ina masu Bukatan Atalla musu Hajarsu Ko wani iri ne Domin samun costumer ta ko"ina..? Ku garzayo kakarku ta kusa yanke saka Zan Tallata muku Hajarku a Duka Shafukana Domin inganta Sana"arku da kuma Samun Cinikaya mai Tsabta da kuma kara Hada hada wajen Masi siye da Siyarwa mai Bukatar A tallata mata Hajjarta Zata iya min mgana kai Tsaye ta wannan Lambar Tawa 09069067488 domin karin Bayani...Sai kunzo Kunsan dai mai kasuwa Shi ke da Riba.._

*Domin zama Daya Daga cikin wadanda zasu karanta Labarin SADAUKARWAR SO..! Zaku Biya kudin karatunku kamar haka Masu amfani da Banki Zasu Tura â‚?300 ta wannan asusun banki 0552179550 Jamila umar gtb,Masu Katin waya kuma zasu Turo â‚?400, ta wannan lambar wayar 09069067488 Adauki Hoton katin sai aturo kai Tsaye mutanenmu na Niger kuma zasu Tuntubi wannan lambar kamar haka +22794775574 domin karin bayani,Insha Allahu mutum zai tsinci kansa a paid group ina maraba da ku masoyana Nagode*

*Shakira...*
1/1/22, 18:52 - Maryam Badmsi: *SADAUKARWAR SO..!!*
_(Labarin Yan"uwantaka,Soyayyah Tare da Sadaukarwa)_

*Wattpad:@Jamilaumar315*
*Mallakar:Jamilaumar(Janafty)*

*Page7️⃣*

"Wannan Dalilin shine zan iya cewa Mafarin Zumunci mai karfi da ya koma Tamkar yan"uwantaka ko Jini Daya Tsakanin Iyalan Alhaji Sunusi Tureta da kuma iyalan Mallam Habibu.

Domin Wata Shakuwa ce mai Girma ta Shiga Tsakanin Mansur da Diza kamar wasu yan"uwana na Jini kullum Kwanan Duniya Tana Gidansu nan take wuni suna wasa Tun ana Maidata Gida Tana kuka Har Alhaji Sunusi yace a kyaleta ta Rika kwana abun kamar wasa sai karamar mgana ta zama Baba Ya zamana Ko Dizan bata zo ba Da sun dawo makaranta Mansur ko abinci baya Tsayawa yaci zai shiga Gidansu Diza megadi baya Hanashi Saboda ya Riga ya sansa Kuma Alhaji ya bada Umarnin kada ataba Hana Iyalan Gidan Mallan Habibu Shiga Gidansa Duk sanda suke so.

Tun iyayansu na mamakin irin Shakuwar Da ke tsakaninsu Har suka Dawo suka Daina ganin Haduwar jini ce da Allah ya Hada sannan uwa uba Halayyansu yazo Daya son Surutu da kuma son wasa,Mastur ya kasance babu Ruwansa baya shiga harkansu sai dai yakan tsawatar musu suyi karatu ko sallah da Sauransu ya zamana kamar wani Babban yaya garesu Diza Tana Jin Tsoron Mastur ko mgana Yayi yanzu Zata Shiga Taitayinta ganin baya mgana kuma Baya Dariya,Bata san Haka Hallitansa take ba Balle ma Da Mansur ke Tsorata da Fadin In bata jin mgana Mastur din yana Duka ita kuma bata son Duka Shiyasa da taji mganarsa Take shiga Taitayinta sai dai baya musu da wasa Duk Jin Dadin wasan da suke da an kira sallah zasu Tashi Mastur ya Dake ma wannan Tarbiyan nasu wanda Hatta da Hajiya Asiya ta Shaida haka Domin Ko Sallah aka Kira bata Tashi ba Tana Zaune in Diza na wajen yanzu Zata kama Hannunta Tana Janta Lokaci Daya tana Fadin Tatashi Tayi sallah Kada Ya Mastur ya mata Bulala wannan abun Farinciki ne Sosai Diza bata wasa da sallah balle karatu wanda da karfi da yaji Ta shiga islamiyansu Mansur Domin in zasu Tafi sai ta Fasa kuka Tun suna barinta agida Har watarana Mastur yace Ta saka Hijabi su Tafi Tare,Jin haka yasa sai dai Suka ji an saka Diza a makarantan Islamiya Mallam Habibu ya sakata kuma Mastur yace Baba ya Dinka mata Hijabai Ta Daina yawo ba Hijabi ko Hula Diza kuma ta Rike wannan Ko Barci bata yarda Tayi saida Hula akanta ko Zamewa yayi sai tace Mommy Ya Mastur yace in ina Barin kaina abude Shedan zai Min Fitsari akaina Hajiya Asiya ssi dai Tayi Dariyan Domin ko itace Diza Ta ganta ba Dankwali Haka take ce mata Har gida Taje tayi ma su Hajja Godiya da Mastur wanda Haka kurum Natsuwarsa Take Burgeta ko Baya son mgana Haka Zatayi ta Jansa Da Hira sai dai ya kalleta ya gyada mata kai ko ya Girgiza mata kai bata Damuwa da Hakan ita dai Haka kurum Mastur din ya Shiga Ranta.

Kusan kullum Hajiya Asiya na Shigowa Gidan Su Hajja kuwa sai Jefi Jefi sun kanshiga su gaisa Mansur kuma ai ya zama Dan Gida Mastur ne ya Taba Shiga Sau Daya shima Lokacin islamiya ne yayi kuma Diza taja Mansur zuwa Gidanasu sai ya Shiga ya Kirasu wannan ne Shigansa na Farko Daga Ranar kuma bai kara Shiga ba Saboda Shi mutum ne mara son Hayaniya da kuma Yawan mgana Tun Farko.

Makaranta kuwa Diza kuka ta saka ma Alhaji Sunusi kan sai an sakata makarantan da Mansur yake zuwa Tunda lokacin Mastur sun zana Jarabawan Fita Daga primary suna Jiran sakamako,Sai Mansur ne kadai ke zuwa Daman achan kaduna an sakata makaranta Tana Nursing2 Dawowarsu nan ne karatun ya Tsaya wannan Dalilin yasa Hajiya Asiyata bada Shawaran ya Sauya ma Mansur din makaranta sai ya sakasu tare da Diza haka kuwa akayi Saidai Hajiya Asiya tazo Tatafi Dashi Batare da tayi wata mgana ba taDai ce Zasu anguwa Mastur kuma baya Zaman gidan Mallam Habibu yake bi kasuwa kafin sakamakon Jarabawan nasu ya fito.

Zaria Acadamy aka kaisu akayi musu yan Tambayoyi,Tare da Sauran abubuwa Cikin Lokaci Daya akayi komai aka gama Tunda akwai kudi Diza Primary 1 aka sakata Shi kuma Mansur Primary 4 uniform da komai Da Littafai Duka makarantan ta basu Ranar chan ma suka barsu sai da suka Dawo ne Hajiya Asiya ke Fada musu Mansur suna makaranta Hajja da Aiya suka rasa bakin mgana Sai Godiya sai 4pm na yammah Ranar suka dawo Kuma Audu Sabon Direban da Alhaji Sunusi ya Dauka yaje ya Daukosu Bakin Mansur da Diza kamar Zai Tsage saboda Farinciki Mallam Habibu sai dai ya Dawo yaji Labari mai Dadi Har gida yaje ya Kara ma Alhaji Sunusi Godiya yace kada ya Damu ai sun Saba Daya yanzu.

*******

Alhaji Sunusi Tureta Mutumin Jahar Sokoto ne A wata Karamar hukuma mai suna Tureta Bashi da iyaye tun yana Gabar samartaka Allah ya yi musu Rasuwa Alhaji Sunusi yayi gwagwarmaya sosai Kafin yayi Karatu sai da ya Saida Duka Gonakin da iyayensa suka Rasu suka barmai ya samu Gurbin Shiga jami"ar Usmanu Dan Fodiyo inda yayi Digree dinsu kan kasuwanci anan ne ya Hadu da Amininsa wanda ya Zama kamar Dan"uwan garesa Alhaji Muhammed Wamako Wanda Shima Dan Wamako ne Shima Karatu ya kawosa suka Hadu nan kuma sai ya zamana abu Daya suke Karanta,Tare suka yi Digree dinsu suka kuma yi Mastes dinsu Lokacin nr suka Fara Tunanin Gudanar da waata Sana"ar Alhaji Muhammed wamako shi ya Fara kawo Shawaran su Fara Sana"ar Shigo da Motoci ba Laifi Suna yan kudade a Hannunsu Tunda bayan gama Digree dinsu sun Fara aiki a wani karamin kamfani suna samun albashinsu suna Tarawa Domin Tsayawa a kan kafafunsu.
Chapter 13 · 0% Book details