← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 94

Sashe 7

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hatta Mastur Dake karami ji da Mansur yake haka zai zauna yayi ta kallonsa yana mai wasa Daukansa Kuwa in Hajara ta Hanashi kuka zai Tayi Dakyar yake yin Shuru Shi adole sai ya Daukesa kuma bazai iya ba Habibu ya yanke Shawaran Hajara Zata Shayar da Mansur kuma Daya Tuntube Hajara dasu Baba Jibo Tuni suka amince Domin Habibu yace bazai Taba Bama Sule Mansur ba ganin irin yadda Maryama ta Rayu agidansu baya Fata Mansur ma yayi irin wannan Rayuwar Dukkansu sun yi Na"am da wannan mganar ta Habibu.

Ranar da Maryama Tayi arba"in Ranar aka Raba komai Daga abunda Maryama ta bari na awakai ne na kiwonta Sai wasu yan kaya da aka Raba Sule ya samu nashi Sauran kuma na Mansur ne awajen ne Sule ya nuna yana son Karban Mansur wanda Goggo ce ta tada Bala"in sai ya karbosa Shi bashi da Ra"ayin Haka Tunda ya Rasa Maryama Yaji Duniyan Ta Juya mai Baya,nan take Habibu yace bazai Taba bashi Mansur ba Hajara Zata Shayar dashi Shi kuma zai zame mai Uba Har abada Mganar data kawo Hayaniya Yayyin Sule suka Shiga mganar kan sai sun karbi Mansur Shi kuma Habibu yace Wlh Ya Rantse bazai Taba basu Mansur ba Haka aka tashi Ranar Zuciyoyo ba Dadi Baba Jibo Shima wannan karon ya Goyi Bayan Habibu Domin bazai so ya Rasa Dan Maryama ba Akaro na Biyu ba kamar yadda ya Rasata ba Shi Sule yayi Shuru karfinsa akaci.

Wannan Dalilin yasa Goggo Mahaifiyarsa Sule tace suje su Rike Mansur ammh Gadon Mansur bazasu bada ba su Zasu Rike Habibu bai Damu ba Domin Basa gabansa Suka Tattara suka bar musu komai kayan Dakin Maryama ne kadai Ayya da Hajara suka je suka kwaso aka Saka Dakin Inna Hasiya Hajara kuma asibiti suka koma amtsayin wacce Zata Shayar da Mansur aka bata mgangunan da Zasu Kawo Ruwan Nono Tazo Gida Tana sha kuma Inna Hasiya na Hada mata da wasu gayyayyaki na gargajiya Cikin Sati Daya Nonuwa suka Shiga Taf Suka Fara Zuban Ruwa cikin Farimciki Hajara ta Fara Shayar da Mansur Wanda Daga ita Har Habibu Suke mai Son da basu son Meyasa ba ammh Suna Jinsa Aransu kamar Dansu Mastur Barin ma ita Dake Shayar Dashi..Wata kauna ce Daga Allah sai dai Mutuwar Maryama Har yau har Gobe ta saka barin Zukatansu barin ma Habibu Da koda yaushe sai yayi kukan Rashin Kanwarsa Dayafi so Fiye da kowa aduniya,Baya kwana Biyu bai Ziyarci kabarinta ba Har sai da Baba Jibo ya Dakatar dashi ganin Rashin Maryama din yana Neman Taba Habibun Sosai...!

Allah ya jikan Maryama da Rahma Allah yasa ta Huta..Allah ya karbi Shahadanta Ameen ya Allah..Tafiyar mai Nisan Zango ce yanzu muke kan Shimfida bamu isa Mafarin ba..

_Albishirunku Masoyana wannan karan na bude muku wani Shashi na musamman Saboda ku..Ina masu Bukatan Atalla musu Hajarsu Ko wani iri ne Domin samun costumer ta ko"ina..? Ku garzayo kakarku ta kusa yanke saka Zan Tallata muku Hajarku a Duka Shafukana Domin inganta Sana"arku da kuma Samun Cinikaya mai Tsabta da kuma kara Hada hada wajen Masi siye da Siyarwa mai Bukatar A tallata mata Hajjarta Zata iya min mgana kai Tsaye ta wannan Lambar Tawa 09069067488 domin karin Bayani...Sai kunzo Kunsan dai mai kasuwa Shi ke da Riba.._

*Domin zama Daya Daga cikin wadanda zasu karanta Labarin SADAUKARWAR SO..! Zaku Biya kudin karatunku kamar haka Masu amfani da Banki Zasu Tura â‚?300 ta wannan asusun banki 0552179550 Jamila umar gtb,Masu Katin waya kuma zasu Turo â‚?400, ta wannan lambar wayar 09069067488 Adauki Hoton katin sai aturo kai Tsaye mutanenmu na Niger kuma zasu Tuntubi wannan lambar kamar haka +22794775574 domin karin bayani,Insha Allahu mutum zai tsinci kansa a paid group ina maraba da ku masoyana Nagode*

*Shakira...*
1/1/22, 18:51 - Maryam Badmsi: *SADAUKARWAR SO..!!*
_(Labarin Yan"uwantaka,Soyayyah Tare da Sadaukarwa)_

*Wattpad:@Jamilaumar315*
*Mallakar:Jamilaumar(Janafty)*

*Page4️⃣*

*Bayan Shekaru Biyu..*

"Bayan Shekaru biyu da suka Gabata Da Rasuwar Maryama Da kuma Rikon Mansur Daya Dawo hannun Hajara.

Itace Madadin Uwa garesa Habibu kuma Uba ne garesa Mastur kuma ya kasance yaya garesa kuma Dan"uwansa Wanda yake Shekara ta bakwai Alokacin ya Fara girma an sakashi makarantan allo.

Girma da kuma Halin Rayuwa ya kara Kama Baba Jibo Ya Fadi a gona Sakamakon Jiri Daya kwasheshi yasa yake gida bai da Lafiya ciwon baya sai dai yakan Fita zuwa masallaci dake kusa baya Doguwar Tafi sai al'amuran suka koma Hannun Habibu Bayan kula da gonakin Mahaifinsa sai ya Fara Kiwo anan Cikin Gidan kama Daga awakai da Shanaye kuma Allah ya saka ma Abun albarka Dayake Inna Hasiya Tana Tsaye da Kafafunta Tana kula da komai.

Mansur Tun yana da wata Goma sha Biyar aduniya ya fara Tafiyansa ba inda baya zuwa Tun yana karaminsa yake kama da Mahaifiyarsa Shiyasa Lokaci Bayan Lokaci In suka kalli Mansur suke Tunawa da Maryama Saboda ba inda ya barta Hajara da Habibu sun fi Nuna Kaunar Zahiri Ga Mansur Fiye da Mastur wanda bai Damu ba Dayake Tun yana yaronsa Miskili ne mara Hayaniya da son mgana Sai dai Yana Bala"in son D'an goggonsa wanda Hajara Ta Fadamai Tun Mansur na Jariri ta gayamai Yaron da Maryama ta Haifa kafin ta Rasu Mansur kenan yaro, da rike abu ya rike komai acikinsa kansa Har yau har gobe bazai manta da Ranar da aka Fita da ita cikin wani Farin kyalle ba,Wanda Abun ya kasa bacemai acikin Kwakwalwarsa.

Tare suke Taruwa wajen kula da Mansur wanda Habibu kemai komai na Rayuwa Hajara kuma taci kashinsa Taci Fitsarinsa kuma Ta shayar dashi Shiyasa Take Jinsa ajikinta Kamar itace ta Haifesa,bangaran sule kuwa Koda yaushe yana Hanyan zuwa Ririwai ganin Mansur kuma ba laifi yana kawo Hidimansa a matsayinsa na uba da Farko har Habibu ya hana akarba sai Baba Jibo ya Dakatar Dashi yace Ya kyalesa ko bakomai Sule uba yake ga Mansur kuma Akwai Hakkinsa a Kansa Tunda yana Raye da wannan Dalilin Habibu yaja bakinsa ya Tsuke Ya zura ido Kawai Sai dai Bayan Sule Ba wanda ya kara Tako Kafarssa Daga Dangin Sule Harta kuwa da Goggo Mahaifiyarsa Suma basu wani Damu ba Shima kuma Sulen bai Taba Gigin cewa Zai Dauki Mansur ya Tafi Dashi Chan maruka ba Tunda yasan ba wani mai kaunar Abunda Maryama din ta bari,Duk da Mansur yaro ne ammh yawan zuwan Sule gidan yasa ya saba Dashi Sosai in ya gansa ya Fara Zillo kenan yana gaurancinsu na yara alamin yaga wanda ya sani ballatana Sulen baya zuwa Hannu Rabbana yan Minti da alawan yara yakan Riko musu shi da Mastur din wanda shi bai ma cika sha ba sai ya Tattara ma Mansur din shi da yake Sarkin Shan Zagi ne.

Haka Rayuwa ta Rika gangarawa Da Dadi ba Dadi Mansur nada Shekara Uku aduniya Wani Ifila"i da kaddaran Allah Daya baya wuce musulmi ya Fado musu Cikin Dare Gobara da ba"a san Daga Ina Take ba ko Daga ina ta Fara ba,Tatashi a Shashen su Inna Hasiya wanda Daga ita Har Baba Jibo sun kone aciki Koda aka Samu Nasaran Ceto su sun Riga sun Shaki Hayaki Sun Kone Daga wasu sassan na Jikinsu Allahu akbar Inna Hasiya da Baba Jibo sun amsa kiran Mahallacinsu alokaci Daya.

Wannan abunda ya Faru ya Girgiza Habibu Da Duka al"ummar Ririwai mutuwa Farar Daya kuma lokaci Daya,Hajara tayi kuka Mansur da Mastur su kansu sun san anyi Rashi Domin sun matukar sabawa da kakanin nasu barin ma Mastur Da ya fara Girma da wayau Habibu yasamu Jarabtan Mutuwan iyayansa alokaci Daya bai Nuna gazawa ba Yayi kukan Zucci ya Fauwala ma Allah komai ganin yana da Mata ga Ya"yansa Guda Biyu Daya kasance Shine garkuwansu Dole ya zama mai Juriya da kuma Jajircewa Domin inganta Rayuwar Mastur da Mansur.

Tun Rasuwar su Inna Hasiya garin Ririwai ya Fita kansa ya Fara Tunanin Sauya wata Rayuwar,Daman bayan Rasuwar su Inna Hasiya sai ya Dauko Ayya tana zama da Hajara Saboda ta Debe mata kewa Domin mutuwar ta Girgiza ta sosai Ta kasa Daina kukan Rashin su Inna gani take kamar kullum kwannan Duniya in ta Tashi Zata Iya Bude ido Ta gansu ta saka yardan ma kanta Cewa sun barsu acikin Duniyan su kuma sun Tafi Gidansu na gaskiya.

Batare da Habibu yayi Shawara da kowa ba ya Fara Shirinsa Gadonsa na Gonaki na wajen Baba Jibo da suka zama gadonsa Duk ya Hada ya Tattara ya Saida Tare da Duka Dabbobinsa Batare da yayi Shawara da kowa ba Shi kadai acikin Zuciyarsa ya yanke ma kansa Shawaran zai yi Nisa da garin kano Domin samun wani Waje da zai je ya gina wata Sabuwar Rayuwa Shi da Matarsa da ya"yansa Guda Biyu wadanda yake Fata da Muradin Da kuma Burin Inganta Rayuwarsu Ta zama wata aba mai ban Sha"awa anan gaba.

Su dai su Hajara sun ga dai an kwashe Dabobbi an Tafi Dasu kuma Habibu bai ce musu komai ba Ayya ce ma ta Tambaya Shine yace zai musu bayani Daga baya sai da yagama Hada Duka kudadensa Da Shawaran inda zasu koma kana ya samu Ayya da Hajara da mganar Sun yi kuka sosai na ganin Zasu bar Mahaifansu sai dai basu yi Gaddama da Habibu ba Tabbas yaga Rashi da maraici yana Bukatar Nesa da garin Doguwa Gabadaya nan dai suka Bashi Goyon baya kuma nan take yace su Fara shiri suyi sallama da Makota Nan da Sati Daya zasu Koma ZARIA..!

Kuma ya sanar dasu bazai Saida wannan Gidan ba Ko Domin gaba Watarana zasu iya zuwa Ko bayan Ransa ko su Mansur bazasu Rasa wajen sauka ba Sai da zai saka wasu Amintattun da zasu kula da Gidan ba sai sun Biya ko asin su ba Ayyah Tayi Na"am sosai da wannan mganar Nan da kuma suka Fara shiri Bayan sun gayama Makota da yan"uwa da abokan Arziki cewa Zasu bar garin Doguwa Gabadaya dama Jahar kano Kowa yaji sai yaji bai ji Dadi ba sai dai Kowa yasan a irin wannan Rashin da Habibu ya Fuskata bazai Taba iya zaman garin ba Nisa da garin Kila zai sa ya Rumgumi Duka Kaddaransa.
Chapter 7 · 0% Book details