← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 94

Sashe 32

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan Bayanai Daga malamai,Masu Ruwa da Tsaki magabata da Masu Makarantar sai aka Fara kiran Daliban Daya Bayan Daya Rukuni Rukuni Domin karban licence da Rantsuwa Wanda prof da kanshi Zai basu,Rumana Tana Daga Farko Farko Lokacin da aka Damkamata Licence dinta Sai ga Hawayen Farinciki Haka ta Dagashi Sama su Umma suna gani Diza da Mansur kuma sai Video suke,Umma Hawayen Farinciki take suka Rumgume da Mommy Suna Murna,bayan angama basu Rantsuwa sai aka koma Kiran Dalibai da suka Fita da Firstcallas,sai ga sunan Rumana Muhammad Wamako a mtsayin wacce ta Fita da Firstcallupper,Murna Farinciki kamar ta suma Bata Taba Zata ba ammh Sauran abikom karatunta sun san ta Chanchanta Domin akwai ta Da kokari Hazaka guruwa ce ta karshe Rumana Har kan Step ta Taka aka karramata kuma aka Bata Waje Tayi jawabin Godiya ga Iyayanta kana aka Gayyaci Alhaji Muhammed Mahaifin Rumana shima ya isa kan step dim yayi jawabin Godiya Cikin Alhafari.

Farinciki ya cika Zuciyar Umma da Abba yau din Rana ta Musamman ce Rumana Tana kuka Tana Rike da kambon karramarta da licent dinta,Murnan Burinta na Farko ya Cika Saura na Biyu cikin Shaukin Farinciki ta Fito da Wayarta Ta Tura ma Mastur Text.

_Salam Alhaamdulillah..Yau na Cika Burina na Farko..Na zama Likita..Saura Dayan Burin nawa Wanda ba wanda ya sanshi Sai Allah..I LOVE U Ya Mastur..And i Mean it.._Daga haka ta Turamai Tana jinkamar ta sauke wani Nauyi Daya Dade acikin Zuciyarta.

Shikuwa Mastur yana Cikin Office dinsa yana aiki yaji Shigowar Sakon Rumana Zuciyarsa sai da ta Buga Daya ga Sakobta Daman yasan Za"a Rina Ya dade yana Tunanin hakan sai dai bai taba Zaton shi nan kusa ba,kansa ya Dafe kawai yana jin wani irin Faduwar gaba,Tun bayan Daya Fahimci Mansur na Son Diza ya gama Tsara Rayuwarsa na cewa bashi ba wani jin Dadi ballatana wani abu na Farinciki ba aikinsa kadai zai sakama gaba bai kawo ma zai iya auran wata mace ba Domin zai Cutar da ita ne ya zauna da ita baya sonta Hakan kamar karuwa ce Zai zauna haka koda bazai Dorar da wani Farinciki ko Jin Dadi game da Rayuwarsa ba Ammh Zai ji sukuni da jin Dadi in har Mansur ya auri Diza ya kasance Cikin Farinciki.

Yana ganin Sakon yayi sauri ya goge bai maida mata da amsa ba Sai ma Tsausayi da ta bashi ta Fada son wanda bai Dace da ita ba Bai taba mata kallon so ba Kallon kanwa yake mata Tunda yake mace Daya ya mallakama Zuciyarsa kuma Ita Din ya Riga yayi alkawarin Sadaukar da ita ga kaninsa Bashi da wani Gurbi da zai iya sakata,Shiyasa ya nuna kamar bai ga Sakonta ba ya koma ya Jingina da kujera yana Fama da Sukan Zuciya ayadda yake kwana baya Barci ga Nauyin kai da Saranwan kai ya Tabbata da yana zuwa asibiti aka auna sa Za"a ga Ya kamu da Hawan Jini Gashi mgungunansa sun kare kuma bai koma baya son yaje a Bayyanamai Wata gazawar Tashi ne Shiyasa kokarinsa Da sai ya Nuna bakomai bai sani ba Hatta Ma"aikatan Dake karkashinsa Sun Fahimci Yallabai baya Cikin kwanciyar Hankali Jarumin Namiji mai cikar Zati da Haiba Duk ya Susuce ya koma wani iri Dashi Rashin son Hayaniya da rashin son mganarsa sai ya karu Yawan kadaicin Dayake samar ma kansa yana kara Hadasamai Abubuwa Dadama bai sani ba.

Achan Lagos kuwa Taro ya Tashi Lafiya su Rumana bayan sun gama Hotuna da Mate dinsu da malamansu ta Nufo inda iyayanta suke ita da Wata kawarta yar Kaduna Basma Lawal ita iyayanta na London Mamarta ta raka Babanta adubashi yana Fama da Mtsalan koda Sai yayanta ne da kanwar Mamanta suka zo mata ita kadai ce kawarta Basma Duk Fadin Jami"an saboda bata da Sakin Jiki da mutane.

Ta gabatar da Basma gasu Umma Suka gaisa cikin Fara"a suna Tayasu Murna nan ta kira yayan nata da Anty ta suka gaisa da su Umma Duk da Abaki suka san Labarin Rumanan sai yau suka ganta,Rumana bakinta Har kunni suka Sarke Hannu da Diza Suna gaisawa yau da sun Hadu bayan sun kwashe Shekaru Rabonsu da ganin juna Sai dai ta Waya ganin Hotunan juna,Diza ta sakar mata kayattacen Mirmishi Tana Fadin"Congratulation Sister..Allah yasa albarka.."

Rumana Cikin Muryanta mai Cike da Natsuwa Ta amsa mata Tana Fadin"Ameen ya Allah..Nagode.."Diza ta kada kai Tana Fadin"Sunana Khadija Sunusi Tureta(Diza).."Rumana tayi Karamar Dariya Tana Fadin"Haba Diza ke din ce bangane ba..?umma kinji Diza Tana Zaton ban ganeta ba..?Umma tace"Ai ku kuka sani. in baku gane juna ba..Kunyi Sakaci da Zumunci Alhalin kuna yara Baku da aiki sai akaini Wajen Diza akaini Wajen Ruma.."Gabadaya aka saka Dariya koda ganin yadda Umma Tayi mganar Rumana Har kasa ta Duka ta gaida Daddy da Alhaji Yusuf suna ta saka mata albarka cikin Sha"awa Daddy yana ji aransa yau Dama Diza Tayi karatu ita da ta sakashi alfahari,Haka ta duka ta gaida Mommy da Hajja da Aiya Sai Matar Alhaji Yusuf Hajiya Laure,Suka Rumgume da Goggo Jummai Juma kuma an samu nayi sai Faman saki baki akeyi ana kallo,Suma Uncles dinta haka ta bisu Daya bayan Daya ta gaishesu suka amsa cikin Alfahari da ita Umma ita ta kalli Rumana Tana nuna Hajja Tace"Kin ko gane Hajja Mahaifiyar Mastur.?

Rumana ta Sunne kai Tana Fadin"Umma naga kamar su ai.."Mommy Tayi Dariya Tace"Kai Dota har kin ga kamarsu..Ai Mastur ma yafi kama Sosai da Baba Habibu.."Rumana tace"Shi nasanshi ai suna Zuwa Da Daddy.."Umma tarike Baki Tace"Kaji ja"ira sau daya ne fa..Lokacin da sukazo Daurin Auran kanina Salisu Asiya Lokacin ita kuma Ta Dawo Hutu.."Mommy tace"Anyi haka Tare kuwa suka zo..Yar nawa akwai kwalkwalwa gashi mun ga Ranarsa yau..'Hajja dai na Gefe Batace komai ba sai Mirmishi Take Aiya ce ta gyara Tsayuwa Tana Fadin"Wai ni baza"a nemi wajen Zama bane..Mufa ba iyalan Megidana bane Yan Sanda da suke kwana atsaye basu gaji ba..Wlh nagaji.."Tafada Tana yamutsa Fuska Umma Tayi Dariya Tana Fadin"Yi hakuri Aiya..Mu karisa Wajem Inuwar Chan a Shinfida Manyan Darduma sai mu Zauna mu Huta muci abinci..Ruma Taho muje kayan ki na Mota.."Rumana tace Toh Har zata Bisu sai ta waiga Tana kallon Diza wacce ke jan gefe Tare da Mansur da Mas"ud suna Hira Basma kuma Daman Tatafi ita da Anty da yayanta inda sukayi parking dim Motarsu itama Jama"a sai Binta suke Juniors dinsu Domin ita ta Kirasu Zata basu kayan Rabon duk su Raba kamar zata Bi bayan su Umma sai ta Fasa Domin ta gane Fuskar Mansur Ta Taba ganinsa yazo Gidansu Wajen Mastur Lokacin Ta Fara Uduth kafin ta samu Addmission ta koma Lagos da karatunta.

Sallama Tayi musu Lokaci Daya Tana gyara Zaman gown din Rigarta Gabadayansu suka waigo Suna kallonta Diza ce tace"Yauwa Taho muyi Hoto.."Jin haka yasa ta karisa kusa da ita Diza ta kalli Mansur Tana Fadin"Dauke mu da wayarka.."Tun kafin ma ta gama mgana ya Fara Daukansu Mas"ud na Gefe Shima yana ta Daukansu Rumana kawai yake kallo yana mata Mirmishi Domin kallon Farko Da yayi mata ta Shiga Ransa a kasar Waje yayi karatunsa yanzu Haka Shine Manaja a kamfanin Sarrafa Biscuit Warrper,Yana ganin Rumana kawai yaji ya samu Matar Aure ta gama Tafiya da Duka Tsarinshi na Macen Dayake son Aura.

Sai da suka gama Hotunan kana Diza Ta kalli Mansur Tana Fadin"My Honourable ga Fa Rumana..My Childhood Friend kuma Diyar abokin Daddy Abba da Umma.."Mansur ya saki Mirmishi yana Fadin"Naganta Jinta yafi ganin Hotonta Firstladyta..Ina kallon yanayinta ta Sauyamin kenan ta zama wata so Classic koda yake Likita ce fa da kanta sai mun zo allura Allah ya Sa albarka.."

Yafada Cikin barkwanci Mirmishi kadai Tayi kafin tace"Ameen Nagode.."Kai ya kada yana Fadin"Sunana Mansur Sulaiman Doguwa...Shakikin kani ga Dcp Mastur Habib Doguwa nasan kin Ganeshi shi.."Wani kayattacen Mirmishi ta saki kafin tace"Haba dai kaima ai na ganeka Ko ba kai bane Honourable..?Baki ya Rike yana Dariya yana kallon Diza ita kuma sai ta Dauke kai tana Dariya Mus"ab ya kallah Shi kuma ya Daga hannu yana Fadin"A"a bani na gayamata ba..Ni yau ma nasan da Honourable nake Son abota.."Sai Dariya ta kamasu Dukkansu banda Rumana Data Murmusa Mansur ya kalli Diza yana Fadin"Kalli Rumana..Don Mirmishinta da yanayinta bai miki da Kama dana Yaya Mastur ba..? har ajinsu iri Dayane Basa son mgana da yawan Dariya sai basarwa.."Rumana ta kafeshi da ido Lokaci Daya kamar yadda Diza ta kafeshi da Ido nan da nan Annurin Fuskarta ya Dauke Shi kuwa ko ajikinsa Ya juya yana Gayama Mas"ud yana bashi Labarin yanayin yayan Nashi Rumana kuwa Juyawa kawai tayi tace suzo su Tafi chan wajen iyayan nasu Diza kuma wani Wutan kishi ne ke cin Ranta Don me Mansur zai Hada Abun kaunarta da wata Duk Sai taji Dan Sakin Jiki Datake da Rumana ma ya Dauke,ahaka dai suka karisa wajen su Umma inda suka Saka manyam Dardumai suna Zaune zaune Rumana kuma su Mansur suka Firtotomata da Manyan Ledojin da Kayan Rabonta ke Ciki ta Dauka ta bama wasu Mata Sauran kuma ta tafi Wajen Basma suna Rabaawa itama Yayanta sun zo mata da nata.

Sai La"asar suka bar Cikin makarantan zuwa Gidan Alhaji Yusuf Domin suyi Salloli suci abinci su Huta acikin makaranta sukabar Rumana Zata Tsaya tayi Parking din Duka kayanta Sai gobe Zata Taho da ita zasu Wuce,Haka kuwa akayi Washegari da Safe Tayi bankwana da Jami"ar lagos Basma ma da Safen suka Tafi Mus"ab Abba ya wakilta yaje ya Taho da ita Shi da Mansur Duk da Mus"ab din sai saka baki yake bata bashi wani Fuska ba suna Mota sanda suka Daukota Tafi maida Hankali Wajen Hiran Mansur wanda Haka kurum yake sakata Nishadi ko Domin yana Dan'uwan abun kaunarta ne Bata sani ba Diza kuwa da Mansur yace Tazo suje tace Tana wani abu Alhalin kuwa Tun mganar jiya ce Take jin Haushin kowa Mussmman ma Rumana bata kaunar ganinta.
Chapter 32 · 0% Book details