← Book details Sadaukarwa So Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 94

Sashe 48

Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 8 min read

Rumana bata samu komawa Ciki ba Tunda tana da Hijabinta Ta Fito Tana Fadin"Mansur Ina kwananmu..?Mansur na sosa kai yace"Lafiya lau Anty Rumana..Taimakom ki nake nema Muje ki Dubamin Diza Don Allah.."Rumana tace"Subhanallah..Me ya sameta..? Mansur duk Surutunsa bai iya cewa komai ba kai kawai ya sosa kai yana yar Dariya Sama da kasa Rumana ta kalleshi sai ta Fara Daukan Saunan abunda ya Faru ganinsa da Jallabiya ajuye Daga gani dai baya Cikin Natsuwarsa batayi gaddama ba ta Bisa Tana Fadin"Muje nagani.."
Daga haka suka Rankaya zuwa Shashen na mansur Mastur Dake Ciki Duk yanaji suka Fice Hannu ya sska ya Dafe kansa yana maimaita"Innalillahi wa'inna Illaihirraju"un.."Kawai yake Maimaitawa Acikiin ransa afili kuma ya Furta"Me kenan yake Faruwa dani..? Matar Dan"uwa ne fa..? Yanzu ta fi karfina Tamin Nisa ya kamata na Cireta araina na Daina Tunaninta..Ammh ya zan yi..?na kasa Cireta araina Ballatana na kallo Matar da take Halaliyata,Zufa kawai yake ketomai Lokaci Daya yana jin kansa na saramai bai tsaya ba ya Tura kofar toilet ya shiga Batare Daya cire kayansa ba ya Tsaya kikam ya saki Shower ruwa yana Dukansa Lokaci Daya Tare da Bugun Zuciyarsa.
Sai da ya samu Saukin Jiki Dana Zuciya kana ya Tube kayansa ya Wurga cikin kwandon kayan wankin Daya ke Tara kayansa na Datti in ya Cire yayi wanka kana ya Dauro Towel ya Fito hankalinsa Duk ya tashi bayan ya Sauya Kaya har dakin Rumana ya Leka bata nan hakan ya Tabbatarmai bata dawo ba kenan sai ya fara Tunanin ko Mtsalan ta wuce yadda yake Tunani ne Kamar ya Daga waya ya Kira Mansur haka yake ji ammh yana Kokarin Danne abun acikin Ransa.

Bangaran Rumana kuwa Kafa kafa ta Dinga Bin Mansur Har cikin Bedroom dinsu inda suka iske Diza dungunkune kan gado da blanket Tana kuka Rumana Daga Gefe ta Tsaya Bata karisa ba Mansur ne ya karisa har kan gado ya Dago da Diza yana Fadin"Kinga am sorry tashi..Ga Anty Rumana tazo Dubaki."
Diza Dake kukan abu Biyu na Farko kukan azaban Datasha Hannun Mansur na Biyu kukan Yau wani wanda bata taba Mafarkin zai karbi Budurcinta ba,ya karba Yanzu Shikenan ita da Mastur sai kallo Kallon kenan Kila kuma yazun sun riga sun zama Daya da Rumana itace ke Haukan banzanta in ta Tuna haka sai ta karajin wani Kishi ya Turketa ta Kara jin kuka na Taso mata ammh jin Abunda Mansur yace ne yasa ta Dago Fuskarta Datayi Jage Jage da majina da kuka Tace"Wata Anty Ruman..."Mganarta ne ta makale ne Lokacin Da suka Hada ido da Rumana Dake tsaye Tana kallonsu wani kololon abu Diza Taji Ya Tokare mata Kirji Lalle ba karamin Tozarta Ta mansur yayi ba,ya rasa wacce zai kira mata sai Wacce ta Tsana irin Rumana wacce ta aure mata abun sonta wacce take jin Kishinta Sosai Fiye da kima itace Zai tona mata asiri a wajenta ita da nata ya Faru wa ta kira .? Ko wata gayamawa shine shi zai zo yayi mata Terere haka kurum.

Kada kai kawai Diza Tayi tana wani Cin mgani Saboda karin Haushi sai ga hawaye na Zubo mata Shi kuma Mansur sai ya Rude ya Tarairayota yana Bata baki Rumana na gefe Tana kallon Ikon Allah ita waya bata wannan Damar Mastur ko kyakyawan kallo bai Taba mata ba ballatana Tayi Fatan zai iya karban wani abu Daga wajenta ba.
Ganin Tabaran nasu yayi yawa ne yasa Ta kalli Mansur Tana Fadin"Mansur ko na Jira ku a falo ne..! mansur Dake Lallashin Diza Kamar yayi kuka yace"A"a Anty Rumana taimaka ki Dubamin ita don Allah.."Mirmishi ta saki kafin Tace"Shikenan zan Dubata..Ammh sai ka dan bamu Waje.."Wata uwar Harara Diza ta banka mata ta gefen ido Shi kuwa Mansur da Sauri ya Kwantar da Diza saman Filo ya Sauko Daga kan gadon yana Fadin"Shikenan in kina Bukatar wani abu ina Falo.."Daga haka ya fice bayan ya kalli Diza yana Fadin"Plz My Firstlady ki bari ta Dubamin ke..Tunda aikinta ne.."ko kallonsa Diza Batayi aranta kawai Allah ya isa take yi na Cutar ta da yayi yagama Tona mata asirinta wajen Rumana.

Bayan Fitan mansur Rumana ta Dade Tsaye ta rasa ta ina Zata Fara ganin Dizan ta nuna kamar bata ganeta ba,Ganin Tsayuwa ba nata bane yasa ta karisa gareta Tana Fadin"Sannu Diza..Zaki iya tashi..? Diza da kanta ke gefe Ta muskuta bata ce komai ba Sai Rumana taji ta Raina kanta ammh Bata Dandara ba ta kara Cemata"Sannu..Ki Daure ki Tashi..Muje Tiolet na Hada,miki Ruwa mai Zafi ki Shiga ki gasa Jikin ki.."Sai Lokacin Diza ta waigo da Fuskarta ba Annuri tace cikin Masifa.."Me kike son gani ne.? Tsiraicina ko.? To bani da kaya ajikina Taya zan mike agabanki kina kallona ina Kallon ki.."
Ta karishe Fada ta wani Tsume Fuska Rumana Taja da baya Tana Fadin"Kiyi hakuri ban sani bane.."Daga haka ta isa ga wardrope dinta ta Bude tana Neman mata Zani bata samu ba sai wata Doguwar Riga bata da Nauyi sosai ita ta Dauko mata ta Ijiye mata nan gefen gado Tana Fadin"Gashi ki tashi ki saka..Bari naje na Hada Miki Ruwan Zafin.."Daga haka ta Tura Kofar Tiolet din ta Shiga Diza ta rakata da Harara Lokaci Daya da jan wani Dogon Tsaki Duk Rumana na jinta bata Juyo ba Mirmishi Takaichi kawai tayi ta karisa Cikin Katon Toilet ta Fara Tara ma Diza Ruwan Zafi a babban Jacuzzin dake Bayin Sai da ta Daidaita Ruwan Zafi yadda zai gasa ma Diza jiki kana Ta Fito Tana Gyara Hannun Hijabinta ta iskeDiza Ta Rarrafa ta Mike ta Saka wannan Rigar tana Dafe da Bango Rumana na Fitowa Ta Ganta sai ta bata Hanya Tana Fadin"Kada ki Surka ruwan..Ki gasa Jikin ki ahaka..In son samu ne ki yi Ruwa uku kana kiyi wanka Daga baya.."Tak Diza Bata Ce mata ba ta Wuce ta Shiga Cikin Tiolet Tana jij kamar Bakinciki zai kasheta Lokaci Daya ta Rufo kofar Tiolet din a Fusace Rumana ta Rakata da ido Domin ta Daina mamakin Sauyawar Dizan gareta sai dai Abu Daya yake bata mamaki Kuma takeson Taji Menene yasa Dizan ta Chanza mata..? Shine Abun Tambayan.

Ganin Duk Zanin gadon ya baci Da Jini yasa ta Tattarashi Ta Cireshi Gefe ta Bude Wardrope din Diza ta Dauko wani Sabon Zanin gado Ta Shimfida Mata ta gyara mata gadon Tsaf wanda ya baci kuma ta ijiyeshi nan gefr in Diza ta Fito zata Shiga Tiolet din ta Wanke inda ya baci Duk da bazata iya wankewa Duka ba Fita Falo Tayi ta samu Mansur Zaune ya Zabga Tagumi,Yana ganinta ya mike yana Tambayanta lafiya,Nan Rumana tace yaje ya Siyo ma Diza mganin pain killer ita kuma Zata shiga Kitchen ta sama mata Ruwan Zafi tasha Tea Hanjinta ya warware,Mansur bai Tsaya Gaddama ba ya Zura aguje ya Fita Rumana na mai Dariya sai gashi ya Dawo bai Dauki key din Mota ba da kudi sai da ya koma Cikin Bedroom din ya Dauka Har Lokacin Diza bata Fito ba,Da gudu Sauri Sauri ya Shiga Motarsa ya bata Wuta yayi Hon megadi ya Budemai Kofa ya Fice Mastur na ganin Fitarsa Domin yana Jikin Window yana kallon Shashen nasu Mansur hankalinsa ya kasa kwanciya da Mansur ya Fito da Sauri ya Koma sai da yaji kamar Zuciyarsa Zata Buga sai gashi kuma ya kara Fitowa ya Shiga Mota ya Fita Tuni Mastur yaji kamar kasa bazata iya Daukansa ba komawa yayi ya zauma yana Dafe da kansa.

Ita kuwa Rumana Kitchen ta Shiga ta Dora Ruwan Zafi a gas bayan yayi Zafi ta kashe ta samu wani mug ta Hadama Diza Shayi ta Dauka ta Shigar mata Dashi Ciki ta iske ta Fito Har taSaka wata Doguwar Rigar atamfa Tana Zaune Da ta bata Tea din Bata ki Karba ba Domin Tana Jin yunwa ta karba Rumanan ta Bita da sannu kana ta kwashi Zanin gadon Daya baci ta shiga Dashi Tiolet yayi girma da yawa bazata iya wankewa ba sai kawai ta Dan Taran wajen da Jini ya bata ta wankeshi kana ta Jefashi Cikin Kwandon kayan wanki Tana Cikin Tiolet din taji shigowar Mansur yana Tambayanta Diza na Zaune na shan Tea kala bata ce mai ba sai ga Rumana ta Fito ya Mika mata mganin ta Karba ta gani kafin ta maidamai Tana Fadin"Ka balla Biyu ka bata tasha..Kuma ya kamata Taci wani abinci mai Ruwa Ruwa haka.."Mansur ya karba yana Fadin"Ok..To yanzu ya zamu yi..?kafim ma Rumana Tayi mgana Diza tace"Bana jin cin komai..Anjuma Mommy Zata aiko da Breakafaat zan kirata na gayamata abunda nake so Zata Dafo ta aiko Min dashi..Nagode.."Daga haka ta Mikama Mansur hannu ya Bata mganin Tasha ta kora da Tea Kafin ta mikamai Mug din ta koma ta kwanta Tana Kauda kanta Rumana bata Damu ba Tace"Shikenan..Allah kara sauki.."Mansur yace"Mungode Anty Rumana..Muje na rakaki Gida kada ya Mastur yaga kin Dade.."
Rumana ta wuce Tana Fadin"Ahaba ba komai.."Da Wani Hararan Tara saura kwata Diza ta rakasu Dukkansu suna Fita ta Saki Tsaki Afili Ta Furta"Rubbish..."

Suna zuwa Kofar Apartment dinsu Rumana ta waigo Tana Fadin"Ka koma Mansur..Kaje ka kula da Diza.."Kai ya gyada mata yana Fadin"Ok..anjuma zan Shigo..Mungode.."Bata ce komai ba illah Mirmishi ta Tura Kofa ta Shiga shi kuma ya Juya Abun mamaki Mastur na Zaune afalon yana ganin Shigowarta ya Dago da Idanuwansa da suka Sauya Launi ya kalleta sau Daya ya kauda ita kuma Sai Ta Saci kallonsa kafin ta Dauke Kanta itama Tataka zuwa Dakinta Kamar bazai yi mgana ba sai kuma ya kasa abun nacin Ransa Dakyar taji sanda yace"Ya take..?
Chapter 48 · 0% Book details