Sashe 89
Sadaukarwa So Complete Hausa Novel · about 10 min read
Mastur kuwa da Hanzari ya isa Kofar Shashen nasu ya saka Hannu ya Bude,sai ga Rumana ta Bayyana tana mai mirmishinta mai kayatarwa Cikin Girmamawanta tace"Mrning...! Tafada Lokaci Daya tana Daukan kwandon Ta Nufi cikin Shashen nasu Bayan ya bata Hanya A tsakiyar Falon ta tsaya saman Center Table ta Ijiye Kwandon Tana Fadin"Ina Amarya Diza..? Fatan Tatashi Lafiya..!
Bai bata amsa ba illah karisowa da yayi ta bayanta ya Rumgumota Lokaci Daya yana Sagala kansa ta wuyanta yana Shinshinata kamar wani Mage,Ita kuma Rumana sai ta Sauke ajiyar zuciya kafin ta sami Zarafin mgana tajisa yana Fadin"Uhm..wannan itace irin gaisuwan tawa Ruma..?
Yafada cikin wani sanyin murya Lokaci Daya Yana kai Hannayensa wani waje acikin Jikinta da Sauri ta rike hannunsa tana Dariya Lokaci Daya da kokarin Zillewa Tana Fadin"Kaifa sabon ango ne..Kada Diza ta Fito ta ganmu..bazata ji dadi da..!
Bata gama Rufe baki ba Diza ta Bayyana afalon Cikin Dogon Hijabinta Tana Binsu da wani Kallo acikin idanuwanta na Takaichi da Bakinciki wanda ta kasa Controling kanta da Kishinta.
Rumana ce tayi saurin kwace Jikinta Tana Daidaita kanta Take Fadin"Amaryanmu. kin tashi Lafiya..?
Tafada Tana bayyana Mirmishinta Mastur kuwa yana Gefe goye da Hannayensa Abayansa yana kallon yanayin Diza da yadda Ta hade rai taki sakarma Rumana Fuska sai yaji bai ji Dadin hakan ba Shiyasa ya isa gareta yana Riko hannunta Lokaci Daya yake Fadin"Baki ji bane Rumana na Tambayan ya Amarya ta kwana bane..?
Diza saboda Takaichi Zare Hannunta Tayi Cikin nashi Tana Zama Cikin Daya Daga Cikin kujerun da sukayi ma Falon kwanya Lokaci Daya tana Tattaro Sauran Mirmishin Daya rage akan Labbanta ta ara ta yafa kafin ta Rausaya tana Fadin"Lafiya..!
Daga haka ta Dauke kanta ta kasa Cigaba da mgana saboda tasowar wani Takaici da kishin Rumana Daga kasab Ranta na ganin irin kallon da Mastur ke Bin Rumana da ita kamar zai lasheta.
Rumana Data ga haka sai ta Rausayar da kai itama tana Nuna ma Diza kwandon Abuncin Lokaci Daya Tana Fadin"Daman Breakfast dinku na kawo muku..Ni zan wuce asibiti..!
Dakyar Diza ta iya cewa"Mungode..!
Daga haka ta Dauke kanta Tana kokarin maida kwallar daya kawo mata,Rumana kuwa sai ta Sagala Jakarta Tana kallon Mastur tace"Zan tafi..!
Takowa yayi zuwa gabanta kamar zai rikota sai taga Idanuwan Diza na kansu sai taja Baya Tana Duba agogon Hannunta Lokaci Daya tana Fadin"Na makara fa Ya Mastur.."
Ta karishe Fada Cikin Shagwaba.
Kai ya kada yana Fadin"kun kusa gama wa ko..? Tace"Eh sauran mu wata Daya mu gama Insha Allahu..!
Mastur yace"Allah ya kaimu..Munyi wata mgana da Abba! Da sauri Rumana tace"Allah yasa ba kan mganar komawata Resendency bane yayi maka Domin naga Abba yana Neman yace na Dakata hakanan..!
Bai ce mata komai ba illah cewa da yayi"Koma miye zamu yi mgana in kika Dawo..!
Kai ta Kada kafin ta juya tana yi musu Sallama Diza dai Tana ganin ikon Allah Domin agaban Idonta Mastur ya Fice yayi ma Rumana rakiya bai dawo ba sai da Motarta tabar Haraban Gidan kana ya Dawo bai iske Diza ba taShiga wanka ya Lura da ita da yanayinta Shiyasa shima ya kwabe ya Bita Tiolet din sukayi wankan Tare duk Kamewar Diza Kasawa Tayi Domin Mastur ba irin Mazan da zasu mika ma matansu Hannu suki karba bane Bata da yarda zatayi dole ta Mika kai Bori ya hau shi ya Nadota a Towel zuwa Bedroom dinsu ya kuma Shafamata mai ya Shiryata Tsab Itama ta taikamai ya shafa mai ya maida kayansa na Jiya suka Fito suka karya da kayattacen Abun karin da Rumana ta Shiryamusu Suka Cinyar da juna Cikin soyayyah Kana Mastur yayi amfani da makulin Dake wajensa ya Bude Shashen Rumana ya Dauko kayansa da Zai Bukata kafin ya bar Bangaran Diza.
Wuni sukayi agida Mastur bai fita ko"ina ba wayoyinsa ma kashesu yayi ya Dauki Duka Hankalinsa da Soyayyarsa ya Mikama Diza wacce a wuni Daya Taji kamar tafi kowacce mace sa"ae samun Gwarzon miji irin Mastur Har taji Tana Fatan su Dauwama aahaka su kadai har Abada Kada Rumana ta Dawo gidan Domin in Mastur na Bata Soyayyarsa Dauka take ita kadai ne ta mallakesa Data Tuna da Rumana sai taji Komai ya Fitar mata a ka,
Rumana kuma tana asibiti Umma ta kirata tace sun wuce ita da Anty Hadiza Rumana tayi ta Bata rai kan me Umma Tatafi bata jira sunyi sallama ba Hakanan Umman ta bata Hakuri sai da tatashi da Zata Dawo ta Biya ta Hanwa ta iske Inna Zainaba ma ta koma da Safe Mardiya ta Bita zata kwana Biyu sun samu Break amakarata.
Saboda tabama Diza da Mastur Lokacin nan wajen Hajja tasha Zamanta Illah ta shiga ta gaida Mommy tama jima tana yi mata Nasiha kafin ta Dauko mansur ta Dawo Dashi Gidan Hajja Tunda ya makalemata Tun shigarta Gidan.
Nan takai dare har sai da Ta taya Hajja suka yi tuwon Shinkafa Miyar alaiyahu,Taci ta Koshi Ta Fara Tunanin su Mastur mai zasu ci wata zuciya tace ina Ruwanki..? Sun fiki sanin Cikin su in suka ji yunwa zasu neman ma kansu mafita da wannan Ta kauda Tunaninsu taci ta Koshi bata ma Jira Dawowar Baba Habibu Ta yi Shirin Tafiya saboda bata son Driving din Darw da Zata tafi Mansur karami ya Fara kuka sai ya Bita ita kuma tace Zata tafi dashi ta Biya Mommy ta hada mata kayansa ta saka sa a Mota suka Dawo gida..
Daman ta san Mastur bazai Fita ba Tunda taji Hajja tace bai leko ba tasan ba inda zaahi Tunda shi ba irin Mansur marigayi bane baya yawo Daga gida sai gida.
Basu ji Dawowarta ba suna chan suna Soyewarsu ko yunwa ma basaji Sai zuwa chan da suka ji yunwan suka sha Tea suka Hada da Sauran Dankalin da Rumana ta Soya musu da Safe sai Lokacin Mastur yaji bai kyauta ba ya Kunna wayarsa ya kira Rumana Lokacin Tagama bama Mansur karami abinci tamai wanka ta sakamai kayan Barci suna Shirin Barci Tunda tayi sallar Isha"i Harda Shafa"i da wuturi taji kiran Mastur Duk da Taji ba Dadi Da Sharetan da yayi ammh bata Nuna mai ba,Ta Daga suka gaisa Tace mai ta Dawo gida Tunda Dazu ita da Mansur Karami ya biyota yaji Dadin haka yace zai Shigo tace ya bari sai da safe su zasu zo da haka sukayi sallama da juna.
Awannan Daran ma Kwana Sukayi suna Farantama juna rai Diza taji ta Raina kanta da Saninta Gabadaya saboda Mastur ya Riga ya gama Goge mata Duka Saninta acikin kwana Biyun da sukayi tare Diza ta Tabbatar ma kanta Mastur na sonta ko a washegarin ma Rumana tayi ta Dawainiya dasu ta kawo masu abun karyawa kafin ta Fice zuwa Wajen aiki Tare da Mansur karami Tatafi domin koda Mastur ya nuna ta bar shi Sai yaron yaki yarda sai ta tafi Dashi Diza kuma Daman bai Damu da ita ba Bayan tatashi yau ma din a Hanwa ta wuni tafi son ta basu Lokaci su gama Cin Amarcinsu.
Bayan Mastur ya gama kwana ukunsu na al"ada adakin Diza Rumana tace ta karamai Kwana Hudu yayi ma Diza kwana Bakwai Mastur ya kasa mgana da Karamcin Rumana garesa Duk da yaji Dadi ammh bai nuna mata ba sai ma Rumgumeta da yayi yana Korafin ta yanke mgana batayi Shawara dashi ba ita dai sai ta bashi Hakuri tace tayi Niyyar har ga Allah.....
Koda ya koma Diza sai taji kamar an sakata a aljannah Damar tun Daya Tafi ya barta take kwance Tana kuka Zuciyarta Cike da Tsanar Rumana da Kishinta wanda Daman akwai shi Dalili yasa Komai ya sauya yanzu kuma komai ya sake Bude mata balle yanzu Data Dandanin Zumar Mastur take jin Dama ita kadai ta mallakesa.
Cikin Satin Dayan da Mastur yayi Tare da Diza Rayuwarta ta Sauya ta kara Fari da Kiba ta Cika da Farinciki Shima haka Mastur dim Lalle Diza ce Rayuwarsa ya Tabbata,Domin a satin Daya sukayi tare ya samu Dukkan Farinciki kuma ya Nemi Ciwonsa ya Rasa Batare Dayaje asibiti ba ko ya Nemi mgani ba.
Bayan ya Dawo wajen Rumana da kwana Daya yayi Shirin komawa Bakin aikinsa a kuma Daran ya Daukesu dukkansu zuwa Hanwa Daman mansur karami yana wajen Rumana yaki yarda ya koma wajen Hajja ko Mommy.
Gidan Daddy suka Fara zuwa Allah yasa Daddy yana gida ya Hadasu dukkansu yayi musu Nasiha sosai,mommy ma ta Tofa albarkacin Bakinta,har anan ne Daddy ke Ma Rumana mganar Cigaban karatunta Cikin Ladabi tace"Abba ina so na samu kwarewa kan Abunda ya Shafi yara..Karatun Shekaru Shida ne ammh naji Abba yana mganar na Dakata hakanan Saboda Aurena..!
Daddy yace"Nima yayimin wannan mganar..sai nace ya Tuntubi Mijimki yaji in ya barki sai nayi ma Dr Hambali mgana sai kiyi karatunki anan Abu din..
Rumana ta Dago Tana kallon Mastur wanda ke Latsa wayarsa Mansur karami na kan jikinsa yana ta tsallensa
Daddy ya juya yana Kallonsa yace"Alhaji Muhammed ya kira ka..?
Mastur ya maida wayarsa aljihu yana Fadin"Eh ya kirani munyi mgana Nace mai ni banga Wani Abun Damuwa ba ai abu ne mai kyai bai kamata mu ki bata Dama ba Tunda Tana da Ra"ayin hakan na gayamai in ni yake ji ya Daina ko ba Mijin Rumana nake ba wlh yayanta nake ni mai Biyamata kudin Karatu ne bama anan gida Nageria ba Duk kasar sa Datake so zan bata izinina da Taimako na da aljihuna da yardan Allah naga ta Cika Burinta!.
Ya karishe Fada yana Kallon Rumana Dake kallonsa Cike da wanni Annuri tana aikamai da kalmar Godiya ta ido Shima ya gane ya Shiga make mata kafada yana Girgiza kai alamun bayason irin wannan Godiyar.
Duk Diza na ankare dasu Bakimciki kamar tatashi ta Shakesu haka take ji Daman ga Ranta ya gama baci da Cigaban karatun Rumana haka kurum taji itama Tana Sha"awar ta koma makaranta Bata kaunar Rumana ta Darata a komai
Mastur kuwa Bazai iya Hana Rumana Burinta ba yayi alkawarin Bata Dukkam Farincinki Tunda Tayi sanadiyar samuwae nashi Farinciki itama zai sanyata Farinciki har karshen Rayuwarsa.
Daddy da Mommy kuwa sai sska albarka suke sun Dade agidan kafin su fito su yada Zango Gidan Hajja nam duka Nasihun ne Daga Bangaran Baba Habibu da Hajja da Ayya nan sukayi Dinner sai Mastur ya gayama su Hajja mganar Cigaban karatun Rumana suma sunyi na"am sosai suma sakamata albarka sukeyi Tuni Diza taji itama Tana jin Lokacin Da zata koma makaranta ya kusa
Sai pass 9pm suka koma Gida amota ma sai Hira Rumana suke da Mastur kan tsarin Karatun da Zatayi kan bangaran yara Shi kuma yana bata goyon baya.
Suna isa Gida ko Raka Diza Shashenta bai yi ba nan sukayi Sallama Mansur karami ya makale ma Rumana Dole ta wuce Dashi Shashenta.
Awannam Daran Rumana taga Soyayya da kauna wanda ya kusa Kama na Daran Farkonta ta Zage ta Nuna na Mastur Godiyarta da Goyon bayan Daya bata suka kwana suna Faratama juna rai Tafiyar Safe zai yi shiyasa Bata kwanta ba Bayan sunyi Sallar asuba Ta tashi ta Tayashi Shirya kayansa ta Hada musu abum kari tace ya Kira Diza su karya Tare
Haka kuwa ya Daga waya ya kirata kamar tace bazata zo ba sai dai bata isa tamai gaddama ba,hakanan tazo suka karyawa Tare ita dai Sai Binsu da ido take Ganin yadda suke kafa kafa da Juna Diza Sai taji ta Raina kanta ta Guduri niyar ilimin da Rumana Ta fita ne yasa Mastur ya fi Darajata sosai Shiyasa ta guduri Niyyar in ya Dawo zata mai mganar komawar ta makaranta.
Tare suka rakashi Har wajen Mota Daman tun jiya ya sallami Iyayan naashi sukayi Fatan Dawowa Lafiya da Fatan Nasara.
Duka ya Hada matan nasa ya Rumgume yana Jadadda musu zai yi kewarsu Cikin ransa kuma ya gama Yanke Shawaran in ya sake Dawowa in zai koma sai da Daya Daga Cikinsu bazai yarda yana da mata Har Biyu ba ya zama gauro a parthercourt ba.
Mansur ma ya Rumgumeshi yana Gayamai zai yi kewarsa Shima ya lafe ajikinsa yana gaurancinsa Katin Bakinsa Rumana ya bamawa Tunda itace Babba yace in Wani Bukata ya taso suyi amfani Dashi Ya bar amanan Gidansa da Iyayensa duka Hannun Rumana haka ya Dinga Nanatamata Har taji Jikinta yayi sanyi Tana Tunanin kodai Mutuwa Gogan nasu zai yi..?
Diza Shashenta ta koma Bayan Tafiyarsa Duk yadda Rumana taso su Zauna tare sai tace Zatayi wani abu ne zata Shigo bayan ta gama nan kuwa so take ta kebe Tayi kuka kukan irin girma da mtsayin da Rumana ta samu a wajen Mastur duk da ita yake so sai gaahi Rumana ta samu nasaran Samun Matsayin da ita bata samu ba.
Ta Kara yardan ma kanta Rashin ilimi mai zurfi ne ya jamata ta Dauki Damaran komawa makaranta itama tayi karatun Ta goga Kafada da Rumana.
Bai bata amsa ba illah karisowa da yayi ta bayanta ya Rumgumota Lokaci Daya yana Sagala kansa ta wuyanta yana Shinshinata kamar wani Mage,Ita kuma Rumana sai ta Sauke ajiyar zuciya kafin ta sami Zarafin mgana tajisa yana Fadin"Uhm..wannan itace irin gaisuwan tawa Ruma..?
Yafada cikin wani sanyin murya Lokaci Daya Yana kai Hannayensa wani waje acikin Jikinta da Sauri ta rike hannunsa tana Dariya Lokaci Daya da kokarin Zillewa Tana Fadin"Kaifa sabon ango ne..Kada Diza ta Fito ta ganmu..bazata ji dadi da..!
Bata gama Rufe baki ba Diza ta Bayyana afalon Cikin Dogon Hijabinta Tana Binsu da wani Kallo acikin idanuwanta na Takaichi da Bakinciki wanda ta kasa Controling kanta da Kishinta.
Rumana ce tayi saurin kwace Jikinta Tana Daidaita kanta Take Fadin"Amaryanmu. kin tashi Lafiya..?
Tafada Tana bayyana Mirmishinta Mastur kuwa yana Gefe goye da Hannayensa Abayansa yana kallon yanayin Diza da yadda Ta hade rai taki sakarma Rumana Fuska sai yaji bai ji Dadin hakan ba Shiyasa ya isa gareta yana Riko hannunta Lokaci Daya yake Fadin"Baki ji bane Rumana na Tambayan ya Amarya ta kwana bane..?
Diza saboda Takaichi Zare Hannunta Tayi Cikin nashi Tana Zama Cikin Daya Daga Cikin kujerun da sukayi ma Falon kwanya Lokaci Daya tana Tattaro Sauran Mirmishin Daya rage akan Labbanta ta ara ta yafa kafin ta Rausaya tana Fadin"Lafiya..!
Daga haka ta Dauke kanta ta kasa Cigaba da mgana saboda tasowar wani Takaici da kishin Rumana Daga kasab Ranta na ganin irin kallon da Mastur ke Bin Rumana da ita kamar zai lasheta.
Rumana Data ga haka sai ta Rausayar da kai itama tana Nuna ma Diza kwandon Abuncin Lokaci Daya Tana Fadin"Daman Breakfast dinku na kawo muku..Ni zan wuce asibiti..!
Dakyar Diza ta iya cewa"Mungode..!
Daga haka ta Dauke kanta Tana kokarin maida kwallar daya kawo mata,Rumana kuwa sai ta Sagala Jakarta Tana kallon Mastur tace"Zan tafi..!
Takowa yayi zuwa gabanta kamar zai rikota sai taga Idanuwan Diza na kansu sai taja Baya Tana Duba agogon Hannunta Lokaci Daya tana Fadin"Na makara fa Ya Mastur.."
Ta karishe Fada Cikin Shagwaba.
Kai ya kada yana Fadin"kun kusa gama wa ko..? Tace"Eh sauran mu wata Daya mu gama Insha Allahu..!
Mastur yace"Allah ya kaimu..Munyi wata mgana da Abba! Da sauri Rumana tace"Allah yasa ba kan mganar komawata Resendency bane yayi maka Domin naga Abba yana Neman yace na Dakata hakanan..!
Bai ce mata komai ba illah cewa da yayi"Koma miye zamu yi mgana in kika Dawo..!
Kai ta Kada kafin ta juya tana yi musu Sallama Diza dai Tana ganin ikon Allah Domin agaban Idonta Mastur ya Fice yayi ma Rumana rakiya bai dawo ba sai da Motarta tabar Haraban Gidan kana ya Dawo bai iske Diza ba taShiga wanka ya Lura da ita da yanayinta Shiyasa shima ya kwabe ya Bita Tiolet din sukayi wankan Tare duk Kamewar Diza Kasawa Tayi Domin Mastur ba irin Mazan da zasu mika ma matansu Hannu suki karba bane Bata da yarda zatayi dole ta Mika kai Bori ya hau shi ya Nadota a Towel zuwa Bedroom dinsu ya kuma Shafamata mai ya Shiryata Tsab Itama ta taikamai ya shafa mai ya maida kayansa na Jiya suka Fito suka karya da kayattacen Abun karin da Rumana ta Shiryamusu Suka Cinyar da juna Cikin soyayyah Kana Mastur yayi amfani da makulin Dake wajensa ya Bude Shashen Rumana ya Dauko kayansa da Zai Bukata kafin ya bar Bangaran Diza.
Wuni sukayi agida Mastur bai fita ko"ina ba wayoyinsa ma kashesu yayi ya Dauki Duka Hankalinsa da Soyayyarsa ya Mikama Diza wacce a wuni Daya Taji kamar tafi kowacce mace sa"ae samun Gwarzon miji irin Mastur Har taji Tana Fatan su Dauwama aahaka su kadai har Abada Kada Rumana ta Dawo gidan Domin in Mastur na Bata Soyayyarsa Dauka take ita kadai ne ta mallakesa Data Tuna da Rumana sai taji Komai ya Fitar mata a ka,
Rumana kuma tana asibiti Umma ta kirata tace sun wuce ita da Anty Hadiza Rumana tayi ta Bata rai kan me Umma Tatafi bata jira sunyi sallama ba Hakanan Umman ta bata Hakuri sai da tatashi da Zata Dawo ta Biya ta Hanwa ta iske Inna Zainaba ma ta koma da Safe Mardiya ta Bita zata kwana Biyu sun samu Break amakarata.
Saboda tabama Diza da Mastur Lokacin nan wajen Hajja tasha Zamanta Illah ta shiga ta gaida Mommy tama jima tana yi mata Nasiha kafin ta Dauko mansur ta Dawo Dashi Gidan Hajja Tunda ya makalemata Tun shigarta Gidan.
Nan takai dare har sai da Ta taya Hajja suka yi tuwon Shinkafa Miyar alaiyahu,Taci ta Koshi Ta Fara Tunanin su Mastur mai zasu ci wata zuciya tace ina Ruwanki..? Sun fiki sanin Cikin su in suka ji yunwa zasu neman ma kansu mafita da wannan Ta kauda Tunaninsu taci ta Koshi bata ma Jira Dawowar Baba Habibu Ta yi Shirin Tafiya saboda bata son Driving din Darw da Zata tafi Mansur karami ya Fara kuka sai ya Bita ita kuma tace Zata tafi dashi ta Biya Mommy ta hada mata kayansa ta saka sa a Mota suka Dawo gida..
Daman ta san Mastur bazai Fita ba Tunda taji Hajja tace bai leko ba tasan ba inda zaahi Tunda shi ba irin Mansur marigayi bane baya yawo Daga gida sai gida.
Basu ji Dawowarta ba suna chan suna Soyewarsu ko yunwa ma basaji Sai zuwa chan da suka ji yunwan suka sha Tea suka Hada da Sauran Dankalin da Rumana ta Soya musu da Safe sai Lokacin Mastur yaji bai kyauta ba ya Kunna wayarsa ya kira Rumana Lokacin Tagama bama Mansur karami abinci tamai wanka ta sakamai kayan Barci suna Shirin Barci Tunda tayi sallar Isha"i Harda Shafa"i da wuturi taji kiran Mastur Duk da Taji ba Dadi Da Sharetan da yayi ammh bata Nuna mai ba,Ta Daga suka gaisa Tace mai ta Dawo gida Tunda Dazu ita da Mansur Karami ya biyota yaji Dadin haka yace zai Shigo tace ya bari sai da safe su zasu zo da haka sukayi sallama da juna.
Awannan Daran ma Kwana Sukayi suna Farantama juna rai Diza taji ta Raina kanta da Saninta Gabadaya saboda Mastur ya Riga ya gama Goge mata Duka Saninta acikin kwana Biyun da sukayi tare Diza ta Tabbatar ma kanta Mastur na sonta ko a washegarin ma Rumana tayi ta Dawainiya dasu ta kawo masu abun karyawa kafin ta Fice zuwa Wajen aiki Tare da Mansur karami Tatafi domin koda Mastur ya nuna ta bar shi Sai yaron yaki yarda sai ta tafi Dashi Diza kuma Daman bai Damu da ita ba Bayan tatashi yau ma din a Hanwa ta wuni tafi son ta basu Lokaci su gama Cin Amarcinsu.
Bayan Mastur ya gama kwana ukunsu na al"ada adakin Diza Rumana tace ta karamai Kwana Hudu yayi ma Diza kwana Bakwai Mastur ya kasa mgana da Karamcin Rumana garesa Duk da yaji Dadi ammh bai nuna mata ba sai ma Rumgumeta da yayi yana Korafin ta yanke mgana batayi Shawara dashi ba ita dai sai ta bashi Hakuri tace tayi Niyyar har ga Allah.....
Koda ya koma Diza sai taji kamar an sakata a aljannah Damar tun Daya Tafi ya barta take kwance Tana kuka Zuciyarta Cike da Tsanar Rumana da Kishinta wanda Daman akwai shi Dalili yasa Komai ya sauya yanzu kuma komai ya sake Bude mata balle yanzu Data Dandanin Zumar Mastur take jin Dama ita kadai ta mallakesa.
Cikin Satin Dayan da Mastur yayi Tare da Diza Rayuwarta ta Sauya ta kara Fari da Kiba ta Cika da Farinciki Shima haka Mastur dim Lalle Diza ce Rayuwarsa ya Tabbata,Domin a satin Daya sukayi tare ya samu Dukkan Farinciki kuma ya Nemi Ciwonsa ya Rasa Batare Dayaje asibiti ba ko ya Nemi mgani ba.
Bayan ya Dawo wajen Rumana da kwana Daya yayi Shirin komawa Bakin aikinsa a kuma Daran ya Daukesu dukkansu zuwa Hanwa Daman mansur karami yana wajen Rumana yaki yarda ya koma wajen Hajja ko Mommy.
Gidan Daddy suka Fara zuwa Allah yasa Daddy yana gida ya Hadasu dukkansu yayi musu Nasiha sosai,mommy ma ta Tofa albarkacin Bakinta,har anan ne Daddy ke Ma Rumana mganar Cigaban karatunta Cikin Ladabi tace"Abba ina so na samu kwarewa kan Abunda ya Shafi yara..Karatun Shekaru Shida ne ammh naji Abba yana mganar na Dakata hakanan Saboda Aurena..!
Daddy yace"Nima yayimin wannan mganar..sai nace ya Tuntubi Mijimki yaji in ya barki sai nayi ma Dr Hambali mgana sai kiyi karatunki anan Abu din..
Rumana ta Dago Tana kallon Mastur wanda ke Latsa wayarsa Mansur karami na kan jikinsa yana ta tsallensa
Daddy ya juya yana Kallonsa yace"Alhaji Muhammed ya kira ka..?
Mastur ya maida wayarsa aljihu yana Fadin"Eh ya kirani munyi mgana Nace mai ni banga Wani Abun Damuwa ba ai abu ne mai kyai bai kamata mu ki bata Dama ba Tunda Tana da Ra"ayin hakan na gayamai in ni yake ji ya Daina ko ba Mijin Rumana nake ba wlh yayanta nake ni mai Biyamata kudin Karatu ne bama anan gida Nageria ba Duk kasar sa Datake so zan bata izinina da Taimako na da aljihuna da yardan Allah naga ta Cika Burinta!.
Ya karishe Fada yana Kallon Rumana Dake kallonsa Cike da wanni Annuri tana aikamai da kalmar Godiya ta ido Shima ya gane ya Shiga make mata kafada yana Girgiza kai alamun bayason irin wannan Godiyar.
Duk Diza na ankare dasu Bakimciki kamar tatashi ta Shakesu haka take ji Daman ga Ranta ya gama baci da Cigaban karatun Rumana haka kurum taji itama Tana Sha"awar ta koma makaranta Bata kaunar Rumana ta Darata a komai
Mastur kuwa Bazai iya Hana Rumana Burinta ba yayi alkawarin Bata Dukkam Farincinki Tunda Tayi sanadiyar samuwae nashi Farinciki itama zai sanyata Farinciki har karshen Rayuwarsa.
Daddy da Mommy kuwa sai sska albarka suke sun Dade agidan kafin su fito su yada Zango Gidan Hajja nam duka Nasihun ne Daga Bangaran Baba Habibu da Hajja da Ayya nan sukayi Dinner sai Mastur ya gayama su Hajja mganar Cigaban karatun Rumana suma sunyi na"am sosai suma sakamata albarka sukeyi Tuni Diza taji itama Tana jin Lokacin Da zata koma makaranta ya kusa
Sai pass 9pm suka koma Gida amota ma sai Hira Rumana suke da Mastur kan tsarin Karatun da Zatayi kan bangaran yara Shi kuma yana bata goyon baya.
Suna isa Gida ko Raka Diza Shashenta bai yi ba nan sukayi Sallama Mansur karami ya makale ma Rumana Dole ta wuce Dashi Shashenta.
Awannam Daran Rumana taga Soyayya da kauna wanda ya kusa Kama na Daran Farkonta ta Zage ta Nuna na Mastur Godiyarta da Goyon bayan Daya bata suka kwana suna Faratama juna rai Tafiyar Safe zai yi shiyasa Bata kwanta ba Bayan sunyi Sallar asuba Ta tashi ta Tayashi Shirya kayansa ta Hada musu abum kari tace ya Kira Diza su karya Tare
Haka kuwa ya Daga waya ya kirata kamar tace bazata zo ba sai dai bata isa tamai gaddama ba,hakanan tazo suka karyawa Tare ita dai Sai Binsu da ido take Ganin yadda suke kafa kafa da Juna Diza Sai taji ta Raina kanta ta Guduri niyar ilimin da Rumana Ta fita ne yasa Mastur ya fi Darajata sosai Shiyasa ta guduri Niyyar in ya Dawo zata mai mganar komawar ta makaranta.
Tare suka rakashi Har wajen Mota Daman tun jiya ya sallami Iyayan naashi sukayi Fatan Dawowa Lafiya da Fatan Nasara.
Duka ya Hada matan nasa ya Rumgume yana Jadadda musu zai yi kewarsu Cikin ransa kuma ya gama Yanke Shawaran in ya sake Dawowa in zai koma sai da Daya Daga Cikinsu bazai yarda yana da mata Har Biyu ba ya zama gauro a parthercourt ba.
Mansur ma ya Rumgumeshi yana Gayamai zai yi kewarsa Shima ya lafe ajikinsa yana gaurancinsa Katin Bakinsa Rumana ya bamawa Tunda itace Babba yace in Wani Bukata ya taso suyi amfani Dashi Ya bar amanan Gidansa da Iyayensa duka Hannun Rumana haka ya Dinga Nanatamata Har taji Jikinta yayi sanyi Tana Tunanin kodai Mutuwa Gogan nasu zai yi..?
Diza Shashenta ta koma Bayan Tafiyarsa Duk yadda Rumana taso su Zauna tare sai tace Zatayi wani abu ne zata Shigo bayan ta gama nan kuwa so take ta kebe Tayi kuka kukan irin girma da mtsayin da Rumana ta samu a wajen Mastur duk da ita yake so sai gaahi Rumana ta samu nasaran Samun Matsayin da ita bata samu ba.
Ta Kara yardan ma kanta Rashin ilimi mai zurfi ne ya jamata ta Dauki Damaran komawa makaranta itama tayi karatun Ta goga Kafada da Rumana.